ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kykkyawar Fata Ga Ziyarar Da Ministan Harkokin Wajen Sin Ya Kai A Afirka

by CGTN Hausa and Sulaiman
5 months ago
Sin

Ranar Litinin 12 ga wannan wata na Janairu ne ministan kula da harkokin wajen kasar Sin, Mr. Wang Yi ya kammala ziyararsa zuwa nahiyar Afrika, inda ya ziyarci hedkwatar kungiyar tarayyar Afirka ta AU, da kasashen Habasha, da Tanzania, da Lesotho. Wannan ziyarar diplomasiyya ta kasance ziyara ta farko a hukumance da Sin ta fara kaiwa a wannan sabuwar shekara ta 2026, kuma a nahiyar Afirka. Afirka dai na ci gaba da kasancewa nahiya ta farko da kasar Sin take fara kai ziyara a kowace sabuwar shekara a cikin shekaru 36 ke nan a jere. Shin ko mene ne sirrin na fara bude ziyararta da kasashen Afirka?

Ziyarar ta kwanaki biyar, wadda ministan harkokin wajen na Sin ya fara daga ranar Laraba 7 ga wannan wata na Janairu ya kammalata ne ranar Litinin 12 ga watan Janairu. Ya kuwa fara aiwatar da wannan ziyara a kasar Ethiopia, wato Habasha, hedikwatar kungiyar tarayyar Afirka (AU), inda daga nan kuma ya zarce zuwa kasashen Tanzania da Lesotho. Wannan ziyara ta zuwa yankin gabashi da kudancin nahiyar Afirka yana da matukar mahimmaci, musamman ta fuskar bunkasa cinikayya tsakanin Sin da wadannan kasashe. Kazalika ziyarar ta kara zurfafa aminci tsakanin bangarorin biyu ta fuskar siyasa da zamantakewa.

Akwai nasarori da dama da wannan ziyarar Mr. Wang ta samu, musamman idan aka yi la’akari da cewa ziyarar ta zo daidai lokacin da ake bukatar hakan. Saboda baya ga kasancewar cika shekaru 70 da kulla dangantakar diplomasiyya tsakanin Sin da kasashen Afirka, wannan ziyara ta zo daidai da lokacin da wasu kasashen Afirka suka shiga cikin halin ni ’ya su ta fuskar tattalin arziki, sakamakon manufofin nan na rashin imani da Amerika ta bullo da su, kama daga batun tsauwala harajin cinikayya, tsananta matakan samar da visa da batun tursasawa wasu kasashen Afirka karbar bakin hauren da Amerika take son raba su da kasar.

ADVERTISEMENT

Sabo da haka wannan ziyara ta samu nasarar kwantar da hankalin kasashen da suka fada cikin mawuyacin hali na tattalin arziki da rikicin siyasa sakamakon munanan manufofin Amerika da kasashen Turai kan kasashen Afirka. Abin da ya kara baiwa wadannan kasashe kwarin gwiwar cewa, kasar Sin tana tare da su ko wuya ko dadi, kuma a ko wane lokaci.

Alfanun hadin gwiwa tsakanin Sin da Afirka a bayyane yake, musamman idan aka yi la’akari da irin dubban kilomita na layin dogo da titunan mota da kamfunnan Sin suka shimfida a kasashe daban daban na Afirka, abin sai san barka. Baya ga wannan kuma ga gadoji da tashoshin jiragen ruwa da filayen saukar jiragen sama masu dimbin yawa da kasar ta Sin ta samar a kasashen na Afirka.

LABARAI MASU NASABA

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Sin Na Daukar hakikanan Matakan Gina Kyakkaywar Makomar Al’ummun Sin Da Afirka Ta Bai Daya

Nasara a bangaren cinikayya kuwa, Sin ta kasance babbar kawar cinikayya da kasahen Afirka sama da shekaru 16. A bara, darajar cinikayya tsakanin bangarorin biyu ta zarce dala biliyan 300. Sabo da yayin da Amerika take ta tsauwala harajin cinikayya kan kasashen Afirka, ita kuwa kasar ta Sin janye harajin cinikayyar ta yi kwata kwata ga kasashen Afirka dake da dangantakar diplomasiyya.

A dunkule, nasarorin da wannan ziyara da minstan harkokin wajen na Sin ya kai a Afirka sun hada da zurfafa dangantakar tattalin arziki, bunkasa harkokin cinikayya tsakanin Sin da Afirka da kuma inganta hadin gwiwa ta fannin kiwon lafiya, tsaro da kuma samar da ababen more rayuwa.

 

Sin
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    ’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi
Sin
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace
  • Sulaiman
    ’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin
  • Sulaiman
    Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
  • Sulaiman
    Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

MASU ALAKA

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
Ra'ayi Riga

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Sin Na Daukar hakikanan Matakan Gina Kyakkaywar Makomar Al’ummun Sin Da Afirka Ta Bai Daya
Ra'ayi Riga

Sin Na Daukar hakikanan Matakan Gina Kyakkaywar Makomar Al’ummun Sin Da Afirka Ta Bai Daya

June 19, 2026
A Yi Watsi Da Wannan “Mummunan Teburi”
Ra'ayi Riga

A Yi Watsi Da Wannan “Mummunan Teburi”

June 18, 2026
Next Post
Sin

Hasashe Game Da Siyasar Nijeriya A 2027

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.