ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kykkyawar Fata Ga Ziyarar Da Ministan Harkokin Wajen Sin Ya Kai A Afirka

by CGTN Hausa and Sulaiman
8 months ago
Sin

Ranar Litinin 12 ga wannan wata na Janairu ne ministan kula da harkokin wajen kasar Sin, Mr. Wang Yi ya kammala ziyararsa zuwa nahiyar Afrika, inda ya ziyarci hedkwatar kungiyar tarayyar Afirka ta AU, da kasashen Habasha, da Tanzania, da Lesotho. Wannan ziyarar diplomasiyya ta kasance ziyara ta farko a hukumance da Sin ta fara kaiwa a wannan sabuwar shekara ta 2026, kuma a nahiyar Afirka. Afirka dai na ci gaba da kasancewa nahiya ta farko da kasar Sin take fara kai ziyara a kowace sabuwar shekara a cikin shekaru 36 ke nan a jere. Shin ko mene ne sirrin na fara bude ziyararta da kasashen Afirka?

Ziyarar ta kwanaki biyar, wadda ministan harkokin wajen na Sin ya fara daga ranar Laraba 7 ga wannan wata na Janairu ya kammalata ne ranar Litinin 12 ga watan Janairu. Ya kuwa fara aiwatar da wannan ziyara a kasar Ethiopia, wato Habasha, hedikwatar kungiyar tarayyar Afirka (AU), inda daga nan kuma ya zarce zuwa kasashen Tanzania da Lesotho. Wannan ziyara ta zuwa yankin gabashi da kudancin nahiyar Afirka yana da matukar mahimmaci, musamman ta fuskar bunkasa cinikayya tsakanin Sin da wadannan kasashe. Kazalika ziyarar ta kara zurfafa aminci tsakanin bangarorin biyu ta fuskar siyasa da zamantakewa.

Akwai nasarori da dama da wannan ziyarar Mr. Wang ta samu, musamman idan aka yi la’akari da cewa ziyarar ta zo daidai lokacin da ake bukatar hakan. Saboda baya ga kasancewar cika shekaru 70 da kulla dangantakar diplomasiyya tsakanin Sin da kasashen Afirka, wannan ziyara ta zo daidai da lokacin da wasu kasashen Afirka suka shiga cikin halin ni ’ya su ta fuskar tattalin arziki, sakamakon manufofin nan na rashin imani da Amerika ta bullo da su, kama daga batun tsauwala harajin cinikayya, tsananta matakan samar da visa da batun tursasawa wasu kasashen Afirka karbar bakin hauren da Amerika take son raba su da kasar.

ADVERTISEMENT

Sabo da haka wannan ziyara ta samu nasarar kwantar da hankalin kasashen da suka fada cikin mawuyacin hali na tattalin arziki da rikicin siyasa sakamakon munanan manufofin Amerika da kasashen Turai kan kasashen Afirka. Abin da ya kara baiwa wadannan kasashe kwarin gwiwar cewa, kasar Sin tana tare da su ko wuya ko dadi, kuma a ko wane lokaci.

Alfanun hadin gwiwa tsakanin Sin da Afirka a bayyane yake, musamman idan aka yi la’akari da irin dubban kilomita na layin dogo da titunan mota da kamfunnan Sin suka shimfida a kasashe daban daban na Afirka, abin sai san barka. Baya ga wannan kuma ga gadoji da tashoshin jiragen ruwa da filayen saukar jiragen sama masu dimbin yawa da kasar ta Sin ta samar a kasashen na Afirka.

LABARAI MASU NASABA

Taswirar Duniya Mai Adalci: Afirka Ta Ki A Sake “Rage” Girmanta

Duk Runtsi, Akwai Mai Ba Da Kulawa Ta Musamman A Kasar Sin

Nasara a bangaren cinikayya kuwa, Sin ta kasance babbar kawar cinikayya da kasahen Afirka sama da shekaru 16. A bara, darajar cinikayya tsakanin bangarorin biyu ta zarce dala biliyan 300. Sabo da yayin da Amerika take ta tsauwala harajin cinikayya kan kasashen Afirka, ita kuwa kasar ta Sin janye harajin cinikayyar ta yi kwata kwata ga kasashen Afirka dake da dangantakar diplomasiyya.

A dunkule, nasarorin da wannan ziyara da minstan harkokin wajen na Sin ya kai a Afirka sun hada da zurfafa dangantakar tattalin arziki, bunkasa harkokin cinikayya tsakanin Sin da Afirka da kuma inganta hadin gwiwa ta fannin kiwon lafiya, tsaro da kuma samar da ababen more rayuwa.

 

Sin
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa
Sin
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi
  • Sulaiman
    Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara
  • Sulaiman
    Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
  • Sulaiman
    Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

MASU ALAKA

Taswirar Duniya Mai Adalci: Afirka Ta Ki A Sake “Rage” Girmanta
Ra'ayi Riga

Taswirar Duniya Mai Adalci: Afirka Ta Ki A Sake “Rage” Girmanta

September 8, 2026
Duk Runtsi, Akwai Mai Ba Da Kulawa Ta Musamman A Kasar Sin
Ra'ayi Riga

Duk Runtsi, Akwai Mai Ba Da Kulawa Ta Musamman A Kasar Sin

September 4, 2026
Samun Rarar Kudin Ciniki Ba “Laifi” Ba Ne, Hadin Gwiwa Da Cin Moriya Tare Ita Ce Mafita Ga Kowa
Ra'ayi Riga

Samun Rarar Kudin Ciniki Ba “Laifi” Ba Ne, Hadin Gwiwa Da Cin Moriya Tare Ita Ce Mafita Ga Kowa

September 2, 2026
Next Post
Sin

Hasashe Game Da Siyasar Nijeriya A 2027

LABARAI MASU NASABA

Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.