ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kykkyawar Fata Ga Ziyarar Da Ministan Harkokin Wajen Sin Ya Kai A Afirka

by CGTN Hausa and Sulaiman
5 months ago
Sin

Ranar Litinin 12 ga wannan wata na Janairu ne ministan kula da harkokin wajen kasar Sin, Mr. Wang Yi ya kammala ziyararsa zuwa nahiyar Afrika, inda ya ziyarci hedkwatar kungiyar tarayyar Afirka ta AU, da kasashen Habasha, da Tanzania, da Lesotho. Wannan ziyarar diplomasiyya ta kasance ziyara ta farko a hukumance da Sin ta fara kaiwa a wannan sabuwar shekara ta 2026, kuma a nahiyar Afirka. Afirka dai na ci gaba da kasancewa nahiya ta farko da kasar Sin take fara kai ziyara a kowace sabuwar shekara a cikin shekaru 36 ke nan a jere. Shin ko mene ne sirrin na fara bude ziyararta da kasashen Afirka?

Ziyarar ta kwanaki biyar, wadda ministan harkokin wajen na Sin ya fara daga ranar Laraba 7 ga wannan wata na Janairu ya kammalata ne ranar Litinin 12 ga watan Janairu. Ya kuwa fara aiwatar da wannan ziyara a kasar Ethiopia, wato Habasha, hedikwatar kungiyar tarayyar Afirka (AU), inda daga nan kuma ya zarce zuwa kasashen Tanzania da Lesotho. Wannan ziyara ta zuwa yankin gabashi da kudancin nahiyar Afirka yana da matukar mahimmaci, musamman ta fuskar bunkasa cinikayya tsakanin Sin da wadannan kasashe. Kazalika ziyarar ta kara zurfafa aminci tsakanin bangarorin biyu ta fuskar siyasa da zamantakewa.

Akwai nasarori da dama da wannan ziyarar Mr. Wang ta samu, musamman idan aka yi la’akari da cewa ziyarar ta zo daidai lokacin da ake bukatar hakan. Saboda baya ga kasancewar cika shekaru 70 da kulla dangantakar diplomasiyya tsakanin Sin da kasashen Afirka, wannan ziyara ta zo daidai da lokacin da wasu kasashen Afirka suka shiga cikin halin ni ’ya su ta fuskar tattalin arziki, sakamakon manufofin nan na rashin imani da Amerika ta bullo da su, kama daga batun tsauwala harajin cinikayya, tsananta matakan samar da visa da batun tursasawa wasu kasashen Afirka karbar bakin hauren da Amerika take son raba su da kasar.

ADVERTISEMENT

Sabo da haka wannan ziyara ta samu nasarar kwantar da hankalin kasashen da suka fada cikin mawuyacin hali na tattalin arziki da rikicin siyasa sakamakon munanan manufofin Amerika da kasashen Turai kan kasashen Afirka. Abin da ya kara baiwa wadannan kasashe kwarin gwiwar cewa, kasar Sin tana tare da su ko wuya ko dadi, kuma a ko wane lokaci.

Alfanun hadin gwiwa tsakanin Sin da Afirka a bayyane yake, musamman idan aka yi la’akari da irin dubban kilomita na layin dogo da titunan mota da kamfunnan Sin suka shimfida a kasashe daban daban na Afirka, abin sai san barka. Baya ga wannan kuma ga gadoji da tashoshin jiragen ruwa da filayen saukar jiragen sama masu dimbin yawa da kasar ta Sin ta samar a kasashen na Afirka.

LABARAI MASU NASABA

Abokin Jibi Shi Ne Aboki

Rayukan Mutanen Kenya Na Da Muhimmanci Daidai Da Na ‘Yan Amurka

Nasara a bangaren cinikayya kuwa, Sin ta kasance babbar kawar cinikayya da kasahen Afirka sama da shekaru 16. A bara, darajar cinikayya tsakanin bangarorin biyu ta zarce dala biliyan 300. Sabo da yayin da Amerika take ta tsauwala harajin cinikayya kan kasashen Afirka, ita kuwa kasar ta Sin janye harajin cinikayyar ta yi kwata kwata ga kasashen Afirka dake da dangantakar diplomasiyya.

A dunkule, nasarorin da wannan ziyara da minstan harkokin wajen na Sin ya kai a Afirka sun hada da zurfafa dangantakar tattalin arziki, bunkasa harkokin cinikayya tsakanin Sin da Afirka da kuma inganta hadin gwiwa ta fannin kiwon lafiya, tsaro da kuma samar da ababen more rayuwa.

 

Sin
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos
Sin
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing
  • Sulaiman
    2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed
  • Sulaiman
    Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada
  • Sulaiman
    Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

MASU ALAKA

Abokin Jibi Shi Ne Aboki
Ra'ayi Riga

Abokin Jibi Shi Ne Aboki

June 3, 2026
Rayukan Mutanen Kenya Na Da Muhimmanci Daidai Da Na ‘Yan Amurka
Ra'ayi Riga

Rayukan Mutanen Kenya Na Da Muhimmanci Daidai Da Na ‘Yan Amurka

June 1, 2026
Nagartattun Manufofin Sin Suna Janyo Hankalin Kasashen Duniya
Ra'ayi Riga

Nagartattun Manufofin Sin Suna Janyo Hankalin Kasashen Duniya

May 29, 2026
Next Post
Sin

Hasashe Game Da Siyasar Nijeriya A 2027

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.