ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Laifukan Intanet: Kotun Abuja Ta Karɓi Rahoton DSS, Ta Ba Da Belin Wani Ɗan Gwagwarmaya

by Rabi'u Ali Indabawa
1 month ago

Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja ta bai wa ɗan gwagwarmaya kuma mai sharhi a kafofin sada zumunta, Justice Chidiebere, wanda aka fi sani da Justice Crack, beli kan zargin aikata laifukan intanet.

Mai shari’a Joyce Abdulmalik ta bayar da belin ne kan kuɗi Naira miliyan 5 tare da mutum ɗaya da zai tsaya masa da makamancin wannan adadi.

Kotun ta ce wanda zai tsaya masa dole ne ya kasance yana zaune a yankin da kotun ke da iko a kai tsawon aƙalla shekaru huɗu tare da tabbataccen adireshi, sannan ya gabatar da shaidar zama kamar yarjejeniyar haya ko takardar mallakar gida ga ma’ajiyar kotu.

ADVERTISEMENT

Mai shari’ar ta kuma bayyana cewa wanda zai tsaya masa dole ne ya kasance ma’aikacin gwamnatin tarayya mai mataki na 15 ko sama da haka, tare da shaidar albashin aƙalla watanni uku, wasiƙar tabbatarwa daga shugaban sashensa da kuma shaidar fansho.

Wani shaida ya bayyana wa kotu cewa wanda ake tuhuma ya bayar da bayaninsa da kansa a gaban lauyoyinsa.

LABARAI MASU NASABA

Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026

Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

A cewarsa, wasu sojoji ne suka aika wa wanda ake tuhuma hotuna, sannan ya yi bidiyo daga hotunan tare da wallafa su a kafofin sada zumunta ba tare da tabbatar da sahihancinsu daga hukumomin soja ba.

Ya kuma shaida wa kotu cewa masu bincike sun cire bayanai daga wayar wanda ake tuhuma, ciki har da bidiyoyin da ake zargin ya wallafa a intanet, tattaunawarsa da wasu sojoji, saƙonnin da ya yi da wanda ya kira “uban gidansa” kan zanga-zanga, da kuma bayanai daga shafukansa na sada zumunta.

Shaidar ya ƙara da cewa an fitar da takardar tabbatar da bin ƙa’ida kuma wani babban jami’i ya sanya wa hannu bayan kammala binciken fasaha.

A yayin zaman kotun, lauyan kariya, Sam Amadi, ya sanar da kotun cewa ba a ba su rahoton binciken da sauran takardun da masu gabatar da ƙara ke son gabatarwa ba.

Sai dai masu gabatar da ƙarar sun bayyana hakan a matsayin kuskure tare da bayar da haƙuri a gaban kotu.

Daga nan ne Mai shari’a Abdulmalik ta amince da rahoton binciken DSS a matsayin hujja ta Eɗhibit A.

Masu gabatar da ƙarar sun kuma gabatar da wayar iPhone da ake zargin an ƙwato daga hannun wanda ake tuhuma, da flash driɓe da aka ce na ɗauke da bidiyoyin da aka wallafa a kafofin sada zumunta, tattaunawar da aka cire daga wayar, da kuma takardar tabbatar da bin ƙa’ida.

Lauyoyin kariya sun ƙi amincewa da karɓar flash driɓe ɗin a matsayin hujja, suna masu cewa ba a bayyana abin da ke cikinsa ba kuma ba a kunna shi a gaban kotu ba.

An ɗage sauraron ƙarar zuwa ranar 25 ga Mayu domin ci gaba da shari’ar, yayin da har yanzu ba a sallami shaidar farko ta masu gabatar da ƙara ba.

Jaridar PUNCH Metro ta rawaito cewa sauraron neman belin ya tsaya a ranar 14 ga Mayu bayan saɓani ya ɓarke tsakanin lauyoyin wanda ake tuhuma kan wanda zai jagoranci tawagar kariya.

Saɓanin ya janyo janye wata tsohuwar buƙatar beli da aka gabatar a madadin ɗan gwagwarmayar, lamarin da ya tilasta wa kotun ɗage shari’ar zuwa ranar Litinin domin sauraron sabuwar buƙatar beli.

Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Nijar Ta Rattaba Hannu A Kan Dokar Haramta Auren Jinsi
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Za Mu Iya Sayar Da Manmu Ba Tare Da Wata Matsala Ba -Iran
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Dattawan Arewa Sun Buƙaci Tinubu Ya Ayyana Dokar Ta-baci Kan Tabarbarewar Tsaro
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Nijeriya Ta Karbi Ƴan Nijeriya 268 Da Suka Tsero Daga Afirka Ta Kudu

MASU ALAKA

Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026
Manyan Labarai

Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026

June 25, 2026
Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi
Manyan Labarai

Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

June 25, 2026
EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53
Manyan Labarai

EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

June 25, 2026
Next Post
Laifukan Intanet: Kotun Abuja Ta Karɓi Rahoton DSS, Ta Ba Da Belin Wani Ɗan Gwagwarmaya

Ya Kamata Mawaƙa Su Guji Munafunci Da Hassada Su Rungumi Juna —Fati UK

LABARAI MASU NASABA

Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026

Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026

June 25, 2026
An Fara Gasar Tseren Dawakai Ta ‘Renewed Hope’ da Sabon Salo A Kano

An Fara Gasar Tseren Dawakai Ta ‘Renewed Hope’ da Sabon Salo A Kano

June 25, 2026
APC Ta Dage Yakin Zaben Shugaban Kasarta A Kano

An Dakatar Da Shugaban APC Na Kebbi Da Kwamishina Kan Zaɓen Cike Gurbin Zuru

June 25, 2026
Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

June 25, 2026
EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

June 25, 2026
Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

June 25, 2026
Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa — Atiku

June 25, 2026
Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.