ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ma’aikatan Wutar Lantarki Sun Yi Barazanar Tafiya Yajin Aiki A Fadin Kasar Nan

by Rabi'u Ali Indabawa and Sulaiman
8 months ago
TCN

Ana iya fuskantar babbar matsala a samar da wutar lantarki a kasa yayin da Kungiyar Kwadago ta Ma’aikatan Wutar Lantarki ta Kasa (NUEE) ta yi barazanar rufe ayyukan samar da wuta a fadin kasa, bayan wani zargin harin da jami’an ‘yansanda masu makamai suka kai wa ma’aikatan Kamfanin Wutar Lantarki na Nijeriya (TCN) a Egbu 132/33kB Transmission Substation da ke Jihar Imo.

Kungiyar ta fada a matsayin martani ga abin da ta kira “shigar da makami cikin tashin hankali”, ta riga ta umurci membobinta da su dakatar da ayyukan samar da wuta a Jihar Imo har sai an ba da sanarwar gaba.

  • Ko Sabon Shugaban PDP Zai Iya Magance Matsalolin Jam’iyyar Kuwa?
  • Gwamnan Kano Ya Ɗauki Malaman Lissafi 400 Aiki

NUEE ta bayyana cewa wannan mataki ya zama dole ne bayan da ma’aikatan da ke aiki aka ce an doke su da makamai, wasu kuma aka sace su ta hannun jami’an ‘yan sanda da ake cewa suna aiki bisa umarnin gwamnatin jihar.

ADVERTISEMENT

Wannan yananyi ya jawo fushi sosai a cikin sashen samar da wuta, inda kungiyar ta yi gargadi cewa za ta dakatar da ayyuka a fadin kasa sai dai idan hukumomi sun dauki mataki nan take don tabbatar da tsaro da kariya ga ma’aikatan wutar lantarki a duk fadin Nijeriya.

An ce ‘yansanda, wadanda ake cewa suna aiki ne a madadin gwamnatin jihar, sun shiga dakunan sarrafa wutar na tashar Egbu 132/33kB Transmission Substation da karfi, inda suka lalata kayan aiki kuma suka hana gudanar da ayyuka.

LABARAI MASU NASABA

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

Ana zargin an afka wa ma’aikatan da makami, an doke su, yayin da aka sace wasu zuwa wani wuri da ba a bayyana ba.

A cikin wata sanarwa daga Sakataren Gudanarwa na Kungiyar NUEE, Dominic Igwebike, a daren Asabar, an ce: “NUEE na nuna matukar mamaki da fushi kan irin halin ‘yan ta’adda da rashin kwarewa da jami’an ‘yansanda suka nuna a yayin da suke aiki a madadin gwamnatin Jihar Imo.

“Wadannan jami’an sun kutsa da karfi cikin dakunan sarrafa wuta a Egbu 132/33KB Transmission Substation domin tilasta wa masu aiki su bayar da dakatarwar wuta ta haramtacciya.

“Yayin harin, ana zargin jami’an sun katse wuta da karfi, sun rike dukkan ma’aikatan da ke aiki a matsayin garkuwa, suna tilasta musu bude breakers cikin matsin lamba.

“Bugu da kari, sun yi amfani da tashin hankali kan membobinmu, suna duka, cin zarafi da duk wani ma’aikaci da suka gani. An lalata kayan kansu, ciki har da wayoyi, kwamfutoci, da motoci, haka kuma an lalata na’urorin CCTB.”

“Jami’an ‘yansanda sun aiwatar da wannan mummunan harin bakin ciki da rashin imani ga ma’aikata marasa laifi kuma sun sace su zuwa wani wuri da ba a bayyana ba.

“NUEE na bayyana kiyayya sosai ga wannan abin kunya kuma tana bukatar a sako mambobinmu da aka sace nan da nan. Haka kuma, muna kiran TCN, Ma’aikatar Wutar Lantarki ta Tarayya, da Babban Jami’in ‘Yansanda (IGP) da su bayar da tabbacin kare membobinmu da hana faruwar irin wannan tashin hankali daga ‘yan sanda ta hanyar sanya su a kulawa.

“Bugu da kari, muna bukatar a maye gurbin duk wani kayan ma’aikata da aka lalata ko aka kwace, sannan muna tabbatar da cewa duk ma’aikatan da aka duka su samu cikakken kulawar lafiya.

“Saboda haka, NUEE ta umurci dukkan membobi su nisanci ofis har sai an ba da sanarwa ta gaba, domin ba za mu iya ci gaba da aiki a yanayin tashin hankali, tsangwama, da barazana ga rayuwa ba. Za a iya ci gaba da aiki ne kawai idan an tabbatar da tsaron ma’aikata da kayan aiki gaba daya.

“Idan ba a magance wadannan matsaloli cikin gaggawa ba, kungiyar ba za ta samu wata hanya ba face ta dakatar da ayyukanmu a fadin kasa har sai an tabbatar da isasshen tsaro da kariya a duk wuraren aiki.”

Wutar Lantarki
Rabi'u Ali Indabawa
+ posts Bio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Wasu Fusatattun Mutane Sun Lakaɗa Wa Mutum Biyu Duka Har Lahira A Kaduna
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Mun Ɗauki Nauyin Karatun Masu Digiri Ta Hanyar Sayar Da Ƙosai Da Ƙuli-ƙuli —Wasu Ƴan Kasuwa
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Adadin Mutanen Da Tsananin Zafi Ya Kashe A Turai Ya Haura Dubu 1,300 —WHO
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Pakistan Ta Kashe Mutum 36 A Hare-haren Da Ta Kai Kan Iyakarta Da Afghanistan
Wutar Lantarki
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya
  • Sulaiman
    Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026
  • Sulaiman
    An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”
  • Sulaiman
    Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

MASU ALAKA

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu
Labarai

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga
Manyan Labarai

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi
Labarai

Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

July 14, 2026
Next Post
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

Matsalar Tsaro: Majalisar Wakilai Ta Nemi Tinubu Ya Canza Salon Yaki

LABARAI MASU NASABA

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

July 14, 2026
Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

July 14, 2026
Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

July 14, 2026
CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.