ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ma’aikatan Wutar Lantarki Sun Yi Barazanar Tafiya Yajin Aiki A Fadin Kasar Nan

by Rabi'u Ali Indabawa and Sulaiman
10 months ago
TCN

Ana iya fuskantar babbar matsala a samar da wutar lantarki a kasa yayin da Kungiyar Kwadago ta Ma’aikatan Wutar Lantarki ta Kasa (NUEE) ta yi barazanar rufe ayyukan samar da wuta a fadin kasa, bayan wani zargin harin da jami’an ‘yansanda masu makamai suka kai wa ma’aikatan Kamfanin Wutar Lantarki na Nijeriya (TCN) a Egbu 132/33kB Transmission Substation da ke Jihar Imo.

Kungiyar ta fada a matsayin martani ga abin da ta kira “shigar da makami cikin tashin hankali”, ta riga ta umurci membobinta da su dakatar da ayyukan samar da wuta a Jihar Imo har sai an ba da sanarwar gaba.

  • Ko Sabon Shugaban PDP Zai Iya Magance Matsalolin Jam’iyyar Kuwa?
  • Gwamnan Kano Ya Ɗauki Malaman Lissafi 400 Aiki

NUEE ta bayyana cewa wannan mataki ya zama dole ne bayan da ma’aikatan da ke aiki aka ce an doke su da makamai, wasu kuma aka sace su ta hannun jami’an ‘yan sanda da ake cewa suna aiki bisa umarnin gwamnatin jihar.

ADVERTISEMENT

Wannan yananyi ya jawo fushi sosai a cikin sashen samar da wuta, inda kungiyar ta yi gargadi cewa za ta dakatar da ayyuka a fadin kasa sai dai idan hukumomi sun dauki mataki nan take don tabbatar da tsaro da kariya ga ma’aikatan wutar lantarki a duk fadin Nijeriya.

An ce ‘yansanda, wadanda ake cewa suna aiki ne a madadin gwamnatin jihar, sun shiga dakunan sarrafa wutar na tashar Egbu 132/33kB Transmission Substation da karfi, inda suka lalata kayan aiki kuma suka hana gudanar da ayyuka.

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

Ana zargin an afka wa ma’aikatan da makami, an doke su, yayin da aka sace wasu zuwa wani wuri da ba a bayyana ba.

A cikin wata sanarwa daga Sakataren Gudanarwa na Kungiyar NUEE, Dominic Igwebike, a daren Asabar, an ce: “NUEE na nuna matukar mamaki da fushi kan irin halin ‘yan ta’adda da rashin kwarewa da jami’an ‘yansanda suka nuna a yayin da suke aiki a madadin gwamnatin Jihar Imo.

“Wadannan jami’an sun kutsa da karfi cikin dakunan sarrafa wuta a Egbu 132/33KB Transmission Substation domin tilasta wa masu aiki su bayar da dakatarwar wuta ta haramtacciya.

“Yayin harin, ana zargin jami’an sun katse wuta da karfi, sun rike dukkan ma’aikatan da ke aiki a matsayin garkuwa, suna tilasta musu bude breakers cikin matsin lamba.

“Bugu da kari, sun yi amfani da tashin hankali kan membobinmu, suna duka, cin zarafi da duk wani ma’aikaci da suka gani. An lalata kayan kansu, ciki har da wayoyi, kwamfutoci, da motoci, haka kuma an lalata na’urorin CCTB.”

“Jami’an ‘yansanda sun aiwatar da wannan mummunan harin bakin ciki da rashin imani ga ma’aikata marasa laifi kuma sun sace su zuwa wani wuri da ba a bayyana ba.

“NUEE na bayyana kiyayya sosai ga wannan abin kunya kuma tana bukatar a sako mambobinmu da aka sace nan da nan. Haka kuma, muna kiran TCN, Ma’aikatar Wutar Lantarki ta Tarayya, da Babban Jami’in ‘Yansanda (IGP) da su bayar da tabbacin kare membobinmu da hana faruwar irin wannan tashin hankali daga ‘yan sanda ta hanyar sanya su a kulawa.

“Bugu da kari, muna bukatar a maye gurbin duk wani kayan ma’aikata da aka lalata ko aka kwace, sannan muna tabbatar da cewa duk ma’aikatan da aka duka su samu cikakken kulawar lafiya.

“Saboda haka, NUEE ta umurci dukkan membobi su nisanci ofis har sai an ba da sanarwa ta gaba, domin ba za mu iya ci gaba da aiki a yanayin tashin hankali, tsangwama, da barazana ga rayuwa ba. Za a iya ci gaba da aiki ne kawai idan an tabbatar da tsaron ma’aikata da kayan aiki gaba daya.

“Idan ba a magance wadannan matsaloli cikin gaggawa ba, kungiyar ba za ta samu wata hanya ba face ta dakatar da ayyukanmu a fadin kasa har sai an tabbatar da isasshen tsaro da kariya a duk wuraren aiki.”

Wutar Lantarki
Rabi'u Ali Indabawa
+ posts Bio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ƙungiya Ta Gudanar Da Zaɓen Sabbin Shugabanninta A Abuja
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Jihar Katsina Da UNICEF Sun Ceto Rayuwar Yara Ta Hanyar Samar Da Abinci Mai Gina Jiki
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Yadda Tinubu Ya Kashe Naira Biliyan 37.64 A Tafiye-tafiye
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ta’addaci: Mutum 14,500 Sun Bace A Arewa Maso Gabas
Wutar Lantarki
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
  • Sulaiman
    Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana
  • Sulaiman
    ‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna
  • Sulaiman
    Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

MASU ALAKA

'Yan Bindiga
Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina
Labarai

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare
Labarai

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Next Post
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

Matsalar Tsaro: Majalisar Wakilai Ta Nemi Tinubu Ya Canza Salon Yaki

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.