An gudanar da wani muhimmin taro na masu ruwa da tsaki a fannin baƙunci da yawon buɗe ido na ƙasa, ƙarƙashin jagorancin hukumar bunƙasa harkokin yawon buɗe ido (NTDA), na tsawon kwanaki biyu a Babban Birnin Tarayya, Abuja.
Taron ya samu halartar manyan baƙi da dama, ciki har da ministar ma’aikatar al’adu da yawon buɗe ido, Hannatu Musa Musawa, tare da kwamishinoni da daraktoci da sauran masu ruwa da tsaki a fannin.
- EFCC Ta Ɗauki Matakin Ƙwace Wasu Gidajen Abubakar Malami A Abuja
- Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja
An gabatar da maƙaloli masu muhimmanci a taron, daga ciki akwai,“Ƙarfafa gudanar da harkar yawon buɗe ido: Rawar da dokoki ke takawa wajen ingantawa da kawo ci gaba mai ɗorewa a fannin yawon buɗe ido ƙarƙashin dokar NTDA ta shekarar 2022″, wanda Mista Ebele Sally Achike, Esƙ ya gabatar.
Zalika, akwai muƙala mai taken, “Daidaita ƙa’idoji a fannin baƙunci: Kafa ƙa’idoji na bai ɗaya don tabbatar da inganci”, wanda shugaban kamfanin Global Consultant, Dakta Tony Luka Elumelu ya gabatar.
Haka kuma, taron ya samu halartar Gwamnan Jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, wanda kwamishinar al’adu da yawon buɗe ido, Hajiya Aisha Lawan Saji Rano ta wakilta tare da daraktocinta.
Mai girma Kwamishinar ta yaba wa gwamnan bisa ƙoƙarin da yake yi na bai wa ma’aikatar damar bunƙasa harkokin yawon buɗe ido a jihar da ma ƙasa baki ɗaya.
Ta miƙa godiyarta ga Ministar ma’aikatar al’adu da yawon buɗe ido, Hannatu Musa Musawa, bisa goyon baya da ƙarfafa giwa wajen haɓaka harkokin yawon buɗe ido a Jihar Kano dama Nijeriya baki ɗaya. Kamar yadda jami’in hulɗa da jama’a na ma’aikatar al’adu da yawon buɗe ido na Jihar Kano, Auwal Umar Dahir ya bayyana wa Jaridar Leadership Hausa.















Discussion about this post