ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, September 10, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Majalisar Dattawa Ta Gayyaci Tsohon Shugaban NNPC Kan Ɓatan Naira Tiriliyan 210

by Sadiq
6 months ago
Majalisar

Kwamitin Asusun Jama’a na Majalisar Dattawa, ya gayyaci tsohon Shugaban Kamfanin Man Fetur na Nijeriya (NNPCL), Mele Kyari, domin ya yi bayani kan zargin ɓatan naira tiriliyan 210 da bai yi cikakken bayani a kansu ba tsakanin shekarar 2017 zuwa 2023.

Haka kuma an gayyaci tsohon Babban Jami’in Kuɗi na kamfanin, Umar Ajia Isa, da tsohon Babban Manajan National Petroleum Investment Management Services (NAPIMS), Bala Wunti.

  • Yadda Manyan Taruka Biyu Na Sin Ke Zamowa Madubin Turbar Ci Gaban Kasar
  • ISWAP Sun Hallaka Sojoji 14 A Borno

Shugaban kwamitin, Aliyu Wadada, ya ce sun yanke wannan hukunci ne bayan duba rahotannin binciken kuɗi na kamfanin.

ADVERTISEMENT

Ya kuma yi gargaɗin cewa za su iya bayar da sammacin kame idan waɗanda aka gayyata suka kasa halarta a lokacin da aka buƙace su.

A cewarsa, rahotannin binciken sun nuna cewa akwai naira tiriliyan 103 da naira tiriliyan 107 da ba a yi cikakken bayani a kansu ba, wanda jimillarsu ta kai naira tiriliyan 210.

LABARAI MASU NASABA

Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu

’Yansanda Sun Cafke Matar Da Ta Kwara Wa Maƙociyarta Tafasasshen Ruwan Zafi A Abuja

Ya ce NNPCL ta bayyana cewa tiriliyan 103 kuɗin da abokan hulɗar kamfanin a harkar haɗin gwiwar mai suka kashe ne tsakanin 2017 da 2023, amma kwamitin ya ce wannan bayani bai gamsar da shi ba.

Haka kuma kamfanin ya rubuta naira tiriliyan 107 a matsayin kuɗaɗen tallafin mai da sauran basussuka a cikin rahoton kuɗinsa na shekarar 2023.

Kwamitin ya kuma yi tambaya kan naira biliyan biyar da aka ce an kashe wajen sauya sunan kamfanin daga Nigerian National Petroleum Corporation (NNPC) zuwa NNPCL.

Hakazalika, an umarci ofishin babban mai bincike da ta gudanar da cikakken binciken kuɗi kan asusun kamfanin a wannan lokaci.

Kwamitin ya ce wannan mataki na daga cikin ƙoƙarin gwamnatin Bola Ahmed Tinubu na tabbatar da gaskiya da riƙon amana wajen tafiyar da kuɗaɗen gwamnati.

MASU ALAKA

Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu
Manyan Labarai

Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu

September 9, 2026
’Yansanda Sun Cafke Matar Da Ta Kwara Wa Maƙociyarta Tafasasshen Ruwan Zafi A Abuja
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Cafke Matar Da Ta Kwara Wa Maƙociyarta Tafasasshen Ruwan Zafi A Abuja

September 9, 2026
’Yan Takarar ADC A Arewa Maso Yamma Sun Yi Alƙawarin Biyan N110,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi
Manyan Labarai

’Yan Takarar ADC A Arewa Maso Yamma Sun Yi Alƙawarin Biyan N110,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi

September 9, 2026
Next Post
Xi Jinping Ya Halarci Taron Tattaunawa Da Wakilan Jama’a Na Jiangsu Mahalartar Zaman NPC

Xi Jinping Ya Halarci Taron Tattaunawa Da Wakilan Jama’a Na Jiangsu Mahalartar Zaman NPC

LABARAI MASU NASABA

Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

September 9, 2026
An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

September 9, 2026
Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba

Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba

September 9, 2026
Xi Ya Aike Da Gaisuwa Albarkacin Ranar Malamai Yana Mai Kira Da A Samar Da Matasa Masu Hazaka Domin Kara Farfado Da Kasa

Xi Ya Aike Da Gaisuwa Albarkacin Ranar Malamai Yana Mai Kira Da A Samar Da Matasa Masu Hazaka Domin Kara Farfado Da Kasa

September 9, 2026
Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu

Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu

September 9, 2026
Renon Matasa A Kan Kyakkyawar Turba Ginshiki Ne Na Gina KasaBy

Renon Matasa A Kan Kyakkyawar Turba Ginshiki Ne Na Gina KasaBy

September 9, 2026
Bikin CIFTIS Zai Ingiza Bude Kofa A Kasar Sin

Bikin CIFTIS Zai Ingiza Bude Kofa A Kasar Sin

September 9, 2026
“Ajin Tashar Sararin Samaniya Na Hong Kong Da Macau” Ya Kara Wa Matasa Sha’awar Kimiyya Da Karfafa Kishin Kasa

“Ajin Tashar Sararin Samaniya Na Hong Kong Da Macau” Ya Kara Wa Matasa Sha’awar Kimiyya Da Karfafa Kishin Kasa

September 9, 2026
’Yansanda Sun Cafke Matar Da Ta Kwara Wa Maƙociyarta Tafasasshen Ruwan Zafi A Abuja

’Yansanda Sun Cafke Matar Da Ta Kwara Wa Maƙociyarta Tafasasshen Ruwan Zafi A Abuja

September 9, 2026
Taron Kolin Urumqi Ya Mayar Da Hankali Kan Kwarewar Shugabanci A Xinjiang Da Muhimmancinta Ga Duniya

Taron Kolin Urumqi Ya Mayar Da Hankali Kan Kwarewar Shugabanci A Xinjiang Da Muhimmancinta Ga Duniya

September 9, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.