ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Majalisar Dattawa Ta Gayyaci Tsohon Shugaban NNPC Kan Ɓatan Naira Tiriliyan 210

by Sadiq
4 months ago
Majalisar

Kwamitin Asusun Jama’a na Majalisar Dattawa, ya gayyaci tsohon Shugaban Kamfanin Man Fetur na Nijeriya (NNPCL), Mele Kyari, domin ya yi bayani kan zargin ɓatan naira tiriliyan 210 da bai yi cikakken bayani a kansu ba tsakanin shekarar 2017 zuwa 2023.

Haka kuma an gayyaci tsohon Babban Jami’in Kuɗi na kamfanin, Umar Ajia Isa, da tsohon Babban Manajan National Petroleum Investment Management Services (NAPIMS), Bala Wunti.

  • Yadda Manyan Taruka Biyu Na Sin Ke Zamowa Madubin Turbar Ci Gaban Kasar
  • ISWAP Sun Hallaka Sojoji 14 A Borno

Shugaban kwamitin, Aliyu Wadada, ya ce sun yanke wannan hukunci ne bayan duba rahotannin binciken kuɗi na kamfanin.

ADVERTISEMENT

Ya kuma yi gargaɗin cewa za su iya bayar da sammacin kame idan waɗanda aka gayyata suka kasa halarta a lokacin da aka buƙace su.

A cewarsa, rahotannin binciken sun nuna cewa akwai naira tiriliyan 103 da naira tiriliyan 107 da ba a yi cikakken bayani a kansu ba, wanda jimillarsu ta kai naira tiriliyan 210.

LABARAI MASU NASABA

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

Ya ce NNPCL ta bayyana cewa tiriliyan 103 kuɗin da abokan hulɗar kamfanin a harkar haɗin gwiwar mai suka kashe ne tsakanin 2017 da 2023, amma kwamitin ya ce wannan bayani bai gamsar da shi ba.

Haka kuma kamfanin ya rubuta naira tiriliyan 107 a matsayin kuɗaɗen tallafin mai da sauran basussuka a cikin rahoton kuɗinsa na shekarar 2023.

Kwamitin ya kuma yi tambaya kan naira biliyan biyar da aka ce an kashe wajen sauya sunan kamfanin daga Nigerian National Petroleum Corporation (NNPC) zuwa NNPCL.

Hakazalika, an umarci ofishin babban mai bincike da ta gudanar da cikakken binciken kuɗi kan asusun kamfanin a wannan lokaci.

Kwamitin ya ce wannan mataki na daga cikin ƙoƙarin gwamnatin Bola Ahmed Tinubu na tabbatar da gaskiya da riƙon amana wajen tafiyar da kuɗaɗen gwamnati.

MASU ALAKA

Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso
Manyan Labarai

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku
Manyan Labarai

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Next Post
Xi Jinping Ya Halarci Taron Tattaunawa Da Wakilan Jama’a Na Jiangsu Mahalartar Zaman NPC

Xi Jinping Ya Halarci Taron Tattaunawa Da Wakilan Jama’a Na Jiangsu Mahalartar Zaman NPC

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.