ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Majalisar Dokoki Ta Amince Da Dokar Kayyade Tsadar Aure A Sakkwato

by Sharfaddeen Sidi Umar, Sokoto
3 years ago
Aure

Majalisar Dokokin Jihar Sakkwato ta aminta da kudurin dokar kayyade tsada da almubazzaranci a bukukuwan aure, zanen suna, kaciya da makamantan su a Jihar.

Honarabul Faruku Mustapha Balle (PDP- Gudu) da gudunmuwar Abubakar Shehu Shamaki (APC- Yabo) ne suka gabatar da dokar waddd Majalisar ta aminta da ita a matsayin doka a zaman ta na wannan makon.

  • Kotu Ta Tura Shugaban Asibiti Kurkuku Kan Zargin Yi Wa Majinyaciya Fyade
  • ‘Yansanda Sun Kama Kauraye 72 Da Ake Zargi Da Kwacen Wayar Salula A Katsina

Tun da farko, bayan tsallake karatu na biyu, Majalisar ta gabatar da kudurin dokar a gaban kwamitin ta na sha’anin Addini wanda ya gabatar da rahotonsa a ranar Talata tare da samun amincewar manbobin majalisar da kudurin a matsayin doka.

ADVERTISEMENT

Da yake gabatar da rahoton, shugaban kwamitin, Abubakar Shamak ya bayyana cewar sun tattauna da masu ruwa da tsaki a Sakkwato wadanda suka bayar da gudunmuwar da aka yi amfani da ita a cikin dokar wadda za ta amfani al’umma.

Bayan muhawara, kudurin ya samu amincewar zama doka a zaman majalisar da Mataimakin Shugaban Majalisar, Honarabul Abubakar Magaji ya jagoran ta.

LABARAI MASU NASABA

Ko Yakin Iran Zai Kawo Karshen Kawancen Amurka Da Kasashen Larabawa?

Yadda Sauya Shekar ‘Yan Siyasa Ta Sauya Fasalin Majalisar Dokokin Kasa

Honarabul Shamaki ya bayyana cewar dokar na da manufar kayyade da takaitawa daidai gwargwado kan tsada da sharholiya da ake yi a bukukuwan aure, zanen suna da kaciya a Sakkwato.

Ya ce ko shakka babu dabi’ar almubazzaranci da ake yi da sunan bukukuwa ba karamar illa ba ce wadda ke haifar da tabarbarewar tattalin arziki a cikin al’umma.

“Wannan bakar dabi’ar idan aka ci-gaba a haka ba tare da daukar mataki da kayyadewa ba, za ta sa aure ya yi wa jama’a matukar wahala wanda hakan zai iya haifar da zina, madugo, luwadi da sauran ayyukan assha.

Dan Majalisar ya kara da cewar a yanzu haka kasawar ango ga yin hidimar da aka bukata ta sharholiya a yayin aure na haifar da watsewar auren bakidaya.

“Matsalar ta haifar da yawaitar mace- macen aure a cikin al’umma. Don haka wannan dokar za ta taimaka kwarai wajen rage tsadar aure da sharholiyar da ake yi da takaita yawan zawarawa.” Ya bayyana.

Aure
Sharfaddeen Sidi Umar, Sokoto
+ postsBio
  • Sharfaddeen Sidi Umar, Sokoto
    https://hausa.leadership.ng/author/sharfaddeen-sidi-umar-sokoto/
    A Yayin Da Babban Bankin Ƙasa (CBN) Ke Yaƙi Da Laifukan Intanet
  • Sharfaddeen Sidi Umar, Sokoto
    https://hausa.leadership.ng/author/sharfaddeen-sidi-umar-sokoto/
    Halin Da Matsalar Tsaro Ta Jefa ‘Yan Gudun Hijira A Arerwacin Nijeriya
  • Sharfaddeen Sidi Umar, Sokoto
    https://hausa.leadership.ng/author/sharfaddeen-sidi-umar-sokoto/
    Sanata Tambuwal Ya Sadaukar Da Takararsa Ga Faruku Yabo
  • Sharfaddeen Sidi Umar, Sokoto
    https://hausa.leadership.ng/author/sharfaddeen-sidi-umar-sokoto/
    Dan-Iya Ya Zama Ɗan Takarar Gwamnan ADC A Sakkwato

MASU ALAKA

Aure
Rahotonni

Ko Yakin Iran Zai Kawo Karshen Kawancen Amurka Da Kasashen Larabawa?

May 17, 2026
Aure
Rahotonni

Yadda Sauya Shekar ‘Yan Siyasa Ta Sauya Fasalin Majalisar Dokokin Kasa

May 16, 2026
Abincin Da Ya Kamata Ku Ci Lokacin Al’ada
Rahotonni

Almajiranci:Matsala Ko Maslaha

May 10, 2026
Next Post
Wakilin Kasar Sin Zai Kai Ziyara Turai Dangane Da Samar Da Mafita Ga Rikicin Ukraine

Wakilin Kasar Sin Zai Kai Ziyara Turai Dangane Da Samar Da Mafita Ga Rikicin Ukraine

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.