Gwamnan Jihar Oyo, Seyi Makinde, ya gargadi sarakunan gargajiya da ke jihar da su nisanci siyasa gabanin babban zaben 2027, yana mai cewa duk wani basarake da ya shiga harkokin siyasa zai fuskanci suka da kalaman siyasa daga ’yan siyasa.
Makinde ya yi wannan gargadin ne a ranar Asabar a garin Eruwa, lokacin da Eleruwa na Eruwa, Oba Samuel Adegbola, ya nada shi sarautar gargajiya ta Aare Asoludero na Ibarapaland. Gwamnan ya ce sarakuna ya kamata su kasance iyaye ga dukkan ’yan siyasa ba tare da nuna bangaranci ba.
Ya ce idan basarake ya yanke shawarar shiga siyasa, to bai kamata ya yi tsammanin za a ci gaba da kallonsa a matsayin wanda ba ya cikin siyasa ba. Makinde ya bayyana cewa a lokacin yakin neman zabe, ’yan siyasa kan rika sukar juna, don haka sarakuna su kare mutuncin kujerunsu ta hanyar kasancewa a tsakiya.
Makinde, wanda ke shirin neman shugabancin Nijeriya a 2027 a karkashin jam’iyyar Allied Peoples Movement (APM), ya kuma ce burinsa bai takaita ga wani yanki na kasar ba. Ya bayyana cewa zai zagaya sassan Nijeriya domin gabatar wa al’umma da manufofinsa na shugabanci da ci gaba.
A yayin taron, Eleruwa ya yabawa Makinde tare da mika bukatun ci gaban Ibarapaland, ciki har da gyaran hanyoyi da wasu muhimman ayyukan more rayuwa. An gudanar da bikin ne tare da kaddamar da sabuwar fadar Eleruwa, wanda ya samu halartar sarakunan gargajiya, da ’yan siyasa da jami’an gwamnati.














