Malaman makarantun firamare da sakandare na Hukumar Babban Birnin Tarayya (FCT) sun sanar da shiga yajin aiki daga ranar Litinin, 20 ga Afrilu, 2026, matakin da zai haddasa rufe dukkan makarantun gwamnati a yankin.
Kungiyar Malaman Nijeriya (NUT), reshen FCT, ta yanke wannan shawara ne a wani taron gaggawa da ta gudanar a ranar Juma’a a Gwagwalada.
A cikin wata sanarwa da shugabannin ƙungiyar suka fitar, sun bayyana cewa matakin ya biyo bayan gazawar gwamnati wajen magance matsalolin da suka shafi walwalar malamai da kuma aiwatar da rahoton kwamitin da aka kafa tun fiye da watanni tara da suka gabata.
Sun ce an bai wa hukumomin FCT wa’adin farko na kwanaki bakwai a watan Maris, sannan aka ƙara wa’adin wata 28, amma duk da haka ba a samu wani sakamako mai ma’ana ba.
Ƙungiyar ta kuma nuna damuwa kan jinkirin fitar da rahoton kwamitin da aka kafa a watan Yuli 2025, wanda aka dorawa alhakin daidaita dukkan haƙƙoƙin da ke kan malamai da kuma kawo mafita mai ɗorewa a bangaren matsalolin aiki.
Haka kuma, malamai sun nemi a soke sharadin “vacancies” da ake amfani da shi wajen dakile ci gaban malamai, tare da sake duba tsarin karin girma na shekarar 2024.
Duk da cewa sun yaba da wasu matakan da Ministan FCT ya ɗauka a baya, ciki har da biyan sabon mafi ƙarancin albashi da kuma wasu bashin watanni tara, sun ce har yanzu akwai manyan matsaloli da ba a warware ba.
A ƙarshe, ƙungiyar ta umarci dukkan malamai da su bi wannan umarni, tare da shawartar iyaye da su killace ‘ya’yansu a gida har sai an samu sabon bayani.















Discussion about this post