ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 13, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Manoma Da Dama Za Su Yi Watsi Da Fannin Noma A Taraba A 2026 -AFAN

by Abubakar Abba
2 months ago
Manoma

Shugaban ƙungiyar manoma ta ƙasa reshen Jihar Taraba AFAN), Mista Saliu Adamu Kumba, ya zayyana manyan dalilan da za su tilasta ɗimbin manoman jihar yin watsi da noma a kakar noma ta 2026.

Ya sanar da cewa, akasarin manoman da ke jihar, ba za su yi noma ba, saboda saukar farashin kayan abinci da kuma tsadar farashin kayan feshi a jihar.

  • Manufar Kawar Da Harajin Kwastam Ta Sin Ta Haifar Da Sabbin Damammakin Hadin Gwiwar Noma Tsakanin Sin Da Zimbabwe
  • Jakadan Sin a Najeriya Ya Gana Da Shugaban Kwamitin Kula Da Makarantun Noma Da Cibiyoyin Bincike Na Majalisar Dattawa Ta Najeriya

Mitsa Kumba, wanda ya sanar da haka a hirarsa da jaridarmu ta LEADERSHIP a Jalingo, babban birinin jihar.

ADVERTISEMENT

Sai dai, ya kuma yi kira ga manoman da ke jihar, da kada su sake su yi ƙasa a gwaiwa, a kan yanayin da suka samu kansu, a kakar noma ta bara.

A cewar shugaban ƙungiyar, samun raguwar farashin amfanin gona a jihar, ya zame wa manoman jihar wani babban ƙalubale, musamman duba da irin ɗimbin kuɗaɗen da suka kashe, wajen yin noma a bara, wanda hakan ya jefa su cikin halin ni ‘yasu.

LABARAI MASU NASABA

Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci

An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya

Kazalika, ya buƙaci manoman jihar, da su ci gaba da yin amfani da ƴan kuɗaɗen da suke da su, domin yin noma a kakar ta bana, musamman domin samar da wadataccen abinci a jihar da kuma a ƙasa baki-ɗaya.

Bugu da ƙari, Mista Kumba ya nanata cewa; manoma da dama a jihar a kakar noman bana, ba za su iya sayen takin zamani da taraktocin noma da kuma sauran kayan aikin yin noma ba, musamman saboda tsadar da waɗannan kayan suke da shi.

Ya nanata cewa, manoman jihar na buƙatar matuƙar tallafi da ƙara musu ƙwarin gwiwa, tare da kuma mayar da hankali daga ɓangaren gwamnati, musamman domin daƙile afkuwar yunwa a jihar.

Haka zalika, shugaban ya nuna ɓacin ransa, a kan yadda aka samu gagarumar raguwa a kakar noman rani ta bana, musaman idan aka kwatanta da ƙaruwar da aka samu mai ɗimbin yawa a kakar bara.

Har wa yau, ya sanar da cewa; matuƙar mahukunta a jihar ba su ɗauki matakan da suka dace na lalubo da mafita a kan wannan matsala ta yiwuwar yin watsi da aikin noma a tsakanin manoman jihar ba, akwai matsala.

Da yake yin tsokaci a kan taimaka wa manoman jihar da Gwamnan Jihar na Taraba Agbu Kefas, ya yi a kakar noma ta bara, shugaban ya jinjina masa matuƙa.

Mista Kumba ya kuma sake yin kira ga gwamnan, kan kada ya gajiya wajen ci gaba da taimaka musu, musamman a ɓangaren rage masu farashin kayan aikin noma, domin manoman jihar su ci gaba da samar da wadataccen abinci a jihar.

Kazalika, shugaban ya kuma yi kira ga matakan gwamnati uku na ƙasar nan da sauran ɗaiɗaikun mutane, musamman waɗanda ke jihar, da su taimaka wa manoman jihar kai tsaye, mai makon taimaka wa waɗanda ba manoman na haƙiƙa ba.

Manoma
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Hukumar FAO Ta Samar Da Shirin Kiwon Tarwada A Jihar Gombe
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Dalilin Da Ya Sa Matatar Dangote Ta Kara Habaka Tura Man Fetur
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Manoma 67 Suka Amfana Da Horon Cibiyar  NIHORT
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Dalilan Da Suka Sa Fannin Kiwo Ke Fuskantar Kalubale A Nijeriya —Gwamnatin Tarayya

MASU ALAKA

Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci
Ra'ayi Riga

Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci

June 13, 2026
An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya
Kotu Da Ɗansanda

An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya

June 13, 2026
Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle
Manyan Labarai

Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle

June 13, 2026
Next Post
Kofin Duniya

Ko Ka San Manyan Ƴanwasa Da Ƙasashen Da Ba Za Su Je Gasar Cin Kofin Duniya Ba?

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci

Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci

June 13, 2026
An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya

An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya

June 13, 2026
Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle

Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle

June 13, 2026
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

’Yansanda Sun Cafke Mutun Biyu Da Ake Zargi Da Fashi Da Makami A Adamawa

June 13, 2026
Kamfanin Simintin Dangote Ya Kaddamar Da Tsarin Fasahar Zamani (AI) Domin Inganta Tsaro Da Harkar Sufuri

Kamfanin Simintin Dangote Ya Kaddamar Da Tsarin Fasahar Zamani (AI) Domin Inganta Tsaro Da Harkar Sufuri

June 13, 2026
Tsohon Kakakin Ma’aikatar Tsaro Rabe Abubakar Ya Rasu A Hannun ‘Ƴan Bindiga

Tsohon Kakakin Ma’aikatar Tsaro Rabe Abubakar Ya Rasu A Hannun ‘Ƴan Bindiga

June 13, 2026
Yadda Matata Ta Daina Girki, Ta Ke Lakaɗamin Duka — Miji Ya Koka

Yadda Matata Ta Daina Girki, Ta Ke Lakaɗamin Duka — Miji Ya Koka

June 13, 2026
Ranar Dimokuraɗiyya: Gwamna Uba Sani Ya ‘Yanta Fursunoni 97

Ranar Dimokuraɗiyya: Gwamna Uba Sani Ya ‘Yanta Fursunoni 97

June 13, 2026
Bukatar Rike Sirri A Tsakanin Ma’aurata

Bukatar Rike Sirri A Tsakanin Ma’aurata

June 13, 2026
Hukumar FAO Ta Samar Da Shirin Kiwon Tarwada A Jihar Gombe

Hukumar FAO Ta Samar Da Shirin Kiwon Tarwada A Jihar Gombe

June 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.