ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Manoma Da Dama Za Su Yi Watsi Da Fannin Noma A Taraba A 2026 -AFAN

by Abubakar Abba
2 months ago
Manoma

Shugaban ƙungiyar manoma ta ƙasa reshen Jihar Taraba AFAN), Mista Saliu Adamu Kumba, ya zayyana manyan dalilan da za su tilasta ɗimbin manoman jihar yin watsi da noma a kakar noma ta 2026.

Ya sanar da cewa, akasarin manoman da ke jihar, ba za su yi noma ba, saboda saukar farashin kayan abinci da kuma tsadar farashin kayan feshi a jihar.

  • Manufar Kawar Da Harajin Kwastam Ta Sin Ta Haifar Da Sabbin Damammakin Hadin Gwiwar Noma Tsakanin Sin Da Zimbabwe
  • Jakadan Sin a Najeriya Ya Gana Da Shugaban Kwamitin Kula Da Makarantun Noma Da Cibiyoyin Bincike Na Majalisar Dattawa Ta Najeriya

Mitsa Kumba, wanda ya sanar da haka a hirarsa da jaridarmu ta LEADERSHIP a Jalingo, babban birinin jihar.

ADVERTISEMENT

Sai dai, ya kuma yi kira ga manoman da ke jihar, da kada su sake su yi ƙasa a gwaiwa, a kan yanayin da suka samu kansu, a kakar noma ta bara.

A cewar shugaban ƙungiyar, samun raguwar farashin amfanin gona a jihar, ya zame wa manoman jihar wani babban ƙalubale, musamman duba da irin ɗimbin kuɗaɗen da suka kashe, wajen yin noma a bara, wanda hakan ya jefa su cikin halin ni ‘yasu.

LABARAI MASU NASABA

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Kazalika, ya buƙaci manoman jihar, da su ci gaba da yin amfani da ƴan kuɗaɗen da suke da su, domin yin noma a kakar ta bana, musamman domin samar da wadataccen abinci a jihar da kuma a ƙasa baki-ɗaya.

Bugu da ƙari, Mista Kumba ya nanata cewa; manoma da dama a jihar a kakar noman bana, ba za su iya sayen takin zamani da taraktocin noma da kuma sauran kayan aikin yin noma ba, musamman saboda tsadar da waɗannan kayan suke da shi.

Ya nanata cewa, manoman jihar na buƙatar matuƙar tallafi da ƙara musu ƙwarin gwiwa, tare da kuma mayar da hankali daga ɓangaren gwamnati, musamman domin daƙile afkuwar yunwa a jihar.

Haka zalika, shugaban ya nuna ɓacin ransa, a kan yadda aka samu gagarumar raguwa a kakar noman rani ta bana, musaman idan aka kwatanta da ƙaruwar da aka samu mai ɗimbin yawa a kakar bara.

Har wa yau, ya sanar da cewa; matuƙar mahukunta a jihar ba su ɗauki matakan da suka dace na lalubo da mafita a kan wannan matsala ta yiwuwar yin watsi da aikin noma a tsakanin manoman jihar ba, akwai matsala.

Da yake yin tsokaci a kan taimaka wa manoman jihar da Gwamnan Jihar na Taraba Agbu Kefas, ya yi a kakar noma ta bara, shugaban ya jinjina masa matuƙa.

Mista Kumba ya kuma sake yin kira ga gwamnan, kan kada ya gajiya wajen ci gaba da taimaka musu, musamman a ɓangaren rage masu farashin kayan aikin noma, domin manoman jihar su ci gaba da samar da wadataccen abinci a jihar.

Kazalika, shugaban ya kuma yi kira ga matakan gwamnati uku na ƙasar nan da sauran ɗaiɗaikun mutane, musamman waɗanda ke jihar, da su taimaka wa manoman jihar kai tsaye, mai makon taimaka wa waɗanda ba manoman na haƙiƙa ba.

Manoma
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Abin Da Ya Sa Gwamnatin Taraba Ta Sayo Sabbin Kayan Noma Na Zamani
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Kamfanin Simintin Ɗangote Ya Ƙaddamar Da Shirye-shiryen Tallafa Wa Mazauna Jihar Biniwe
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Dalilin Gwamnatin Kwara Na Zuba Dala Biliyan 70 A Fannin Kiwon Dabbobi
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Cibiyar IAR Ta Gudanar Da Ayyukan Bincike 140 Kan Sabbin Amfanin Gona 

MASU ALAKA

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli
Labarai

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro
Manyan Labarai

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Next Post
Kofin Duniya

Ko Ka San Manyan Ƴanwasa Da Ƙasashen Da Ba Za Su Je Gasar Cin Kofin Duniya Ba?

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026
Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.