Shugaban ƙungiyar manoma ta ƙasa reshen Jihar Taraba AFAN), Mista Saliu Adamu Kumba, ya zayyana manyan dalilan da za su tilasta ɗimbin manoman jihar yin watsi da noma a kakar noma ta 2026.
Ya sanar da cewa, akasarin manoman da ke jihar, ba za su yi noma ba, saboda saukar farashin kayan abinci da kuma tsadar farashin kayan feshi a jihar.
- Manufar Kawar Da Harajin Kwastam Ta Sin Ta Haifar Da Sabbin Damammakin Hadin Gwiwar Noma Tsakanin Sin Da Zimbabwe
- Jakadan Sin a Najeriya Ya Gana Da Shugaban Kwamitin Kula Da Makarantun Noma Da Cibiyoyin Bincike Na Majalisar Dattawa Ta Najeriya
Mitsa Kumba, wanda ya sanar da haka a hirarsa da jaridarmu ta LEADERSHIP a Jalingo, babban birinin jihar.
Sai dai, ya kuma yi kira ga manoman da ke jihar, da kada su sake su yi ƙasa a gwaiwa, a kan yanayin da suka samu kansu, a kakar noma ta bara.
A cewar shugaban ƙungiyar, samun raguwar farashin amfanin gona a jihar, ya zame wa manoman jihar wani babban ƙalubale, musamman duba da irin ɗimbin kuɗaɗen da suka kashe, wajen yin noma a bara, wanda hakan ya jefa su cikin halin ni ‘yasu.
Kazalika, ya buƙaci manoman jihar, da su ci gaba da yin amfani da ƴan kuɗaɗen da suke da su, domin yin noma a kakar ta bana, musamman domin samar da wadataccen abinci a jihar da kuma a ƙasa baki-ɗaya.
Bugu da ƙari, Mista Kumba ya nanata cewa; manoma da dama a jihar a kakar noman bana, ba za su iya sayen takin zamani da taraktocin noma da kuma sauran kayan aikin yin noma ba, musamman saboda tsadar da waɗannan kayan suke da shi.
Ya nanata cewa, manoman jihar na buƙatar matuƙar tallafi da ƙara musu ƙwarin gwiwa, tare da kuma mayar da hankali daga ɓangaren gwamnati, musamman domin daƙile afkuwar yunwa a jihar.
Haka zalika, shugaban ya nuna ɓacin ransa, a kan yadda aka samu gagarumar raguwa a kakar noman rani ta bana, musaman idan aka kwatanta da ƙaruwar da aka samu mai ɗimbin yawa a kakar bara.
Har wa yau, ya sanar da cewa; matuƙar mahukunta a jihar ba su ɗauki matakan da suka dace na lalubo da mafita a kan wannan matsala ta yiwuwar yin watsi da aikin noma a tsakanin manoman jihar ba, akwai matsala.
Da yake yin tsokaci a kan taimaka wa manoman jihar da Gwamnan Jihar na Taraba Agbu Kefas, ya yi a kakar noma ta bara, shugaban ya jinjina masa matuƙa.
Mista Kumba ya kuma sake yin kira ga gwamnan, kan kada ya gajiya wajen ci gaba da taimaka musu, musamman a ɓangaren rage masu farashin kayan aikin noma, domin manoman jihar su ci gaba da samar da wadataccen abinci a jihar.
Kazalika, shugaban ya kuma yi kira ga matakan gwamnati uku na ƙasar nan da sauran ɗaiɗaikun mutane, musamman waɗanda ke jihar, da su taimaka wa manoman jihar kai tsaye, mai makon taimaka wa waɗanda ba manoman na haƙiƙa ba.















Discussion about this post