ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Manoma Da Makiyaya 200 Sun Amfana Daga Shirin SPAR Na Noma A Katsina

by Abubakar Sulaiman
2 months ago
Manoma

Aƙalla manoma da masu kiwon dabbobi 200 ne suka amfana da shirin Sustainable Peace and Resilience (SPAR) a jihar Katsina, wani tsari da aka ƙaddamar domin inganta zaman lafiya da ƙarfafa hanyoyin samun abin dogaro ta hanyar noma mai dacewa da sauyin yanayi.

Manajan aikin na Women Environmental Programme, Damaris Uja, ta bayyana hakan yayin taron rufe aikin da bitar darussa, inda ta yi bayani kan tasirin shirin a al’ummomin da suka ci gajiyarsa.

Ta ce shirin, wanda Foreign, Commonwealth and Development Office ke tallafawa tare da haɗin gwuiwar ActionAid da Tetra Tech, an ƙirƙire shi ne domin magance tushen rikice-rikicen manoma da makiyaya tare da inganta juriya ta tattalin arziki.

ADVERTISEMENT

A cewarta, an zaɓi masu cin gajiyar kai tsaye 200 daga jihohin Katsina da Binuwe, inda kowace jiha ta bayar da manoma 50 da makiyaya 50, yayin da wasu da dama suka amfana a daga gefe.

Shirin ya haɗa da horo kan kiwon dabbobi mai ɗorewa da noma mai jure sauyin yanayi, tare da samar da ƙaramar Ruga da aquaponics domin ƙara hanyoyin samun kuɗi da inganta wadatar abinci.

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

Haka kuma, an jaddada muhimmancin haɗa mata da masu nakasa cikin shirin, yayin da aka gudanar da wayar da kai da ziyarce-ziyarcen shawarwari ga gwamnati da sarakunan gargajiya domin tabbatar da dorewar shirin.

A nasa ɓangaren, jagoran shirin SPRING, Ukona Ukiwo, ya bayyana cewa haɗa batun sauyin yanayi da rikicin manoma da makiyaya yana da muhimmanci, yana mai cewa shirin ya taimaka wajen ƙarfafa hanyoyin warware rikici da gina juriya a tsakanin al’umma.

Ya ƙara da cewa tun fara shirin a 2024, an yi aiki da hukumomi da al’umma domin ƙarfafa tsarin gargaɗi da matakan magance rikice-rikice, tare da tallafa wa manufofi da dokoki da ke inganta sarrafa albarkatu da zaman lafiya.

Manoma
Abubakar Sulaiman
Website |  + postsBio
  • Abubakar Sulaiman
    Jam’iyyar APC Ta Tafka Asarar Mabiya A Gombe, Sun Bi Pantami PDP
  • Abubakar Sulaiman
    Gwamnatin Tarayya Ta Gargaɗi Masu Ɓoye Gas Ɗin Girki
  • Abubakar Sulaiman
    Kotu Ta Bayar Da Umarnin Tsare Sowore A Gidan Yarin Kuje
  • Abubakar Sulaiman
    Yanzu-Yanzu: An Kashe Manoma 18 Da Raunata Wasu A Wani Sabon Hari A Filato

MASU ALAKA

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba
Labarai

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

June 24, 2026
An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi
Labarai

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

June 24, 2026
Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga
Manyan Labarai

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

June 24, 2026
Next Post
JAMB Ta Ƙara Wa’adin Sayar Da Fom Ɗin Shiga Jami’a Kai Tsaye Zuwa 8 Ga Watan Mayu

JAMB Ta Ƙara Wa’adin Sayar Da Fom Ɗin Shiga Jami'a Kai Tsaye Zuwa 8 Ga Watan Mayu

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

June 24, 2026
An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

June 24, 2026
Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

June 24, 2026
Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

June 23, 2026
Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

June 23, 2026
Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

June 23, 2026
Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

June 23, 2026
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

’Yansanda Sun Kama Mutane 57 Da Ake Zargi Da Ayyukan Ta’addanci A Adamawa

June 23, 2026
Li Qiang Ya Gana Da Firaministan Kasar Guinea

Li Qiang Ya Gana Da Firaministan Kasar Guinea

June 23, 2026
Maniyyatan Nijeriya

Hajjin 2026: NAHCON Ta Kammala Jigilar Alhazan Nijeriya Daga Saudiyya

June 23, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.