Hukumar Shirya Jarabawar Shiga Jami’a ta Ƙasa (JAMB) ta ƙara wa’adin sayar da fom ɗin Direct Entry (DE) zuwa ranar 8 ga watan Mayu, 2026, daga tsohon wa’adin da aka sa a baya.
A cikin sanarwar da kakakin hukumar, Dakta Fabian Benjamin, ya fitar, JAMB ta ce an ɗauki wannan mataki ne domin tabbatar da cewa babu ɗan maso cikewar da zai rasa damar shiga manyan makarantu a ƙasar.
Hukumar ta kuma amince da ƙarin cibiyoyin rajista guda biyar domin rage cunkoso a wuraren yin rajista. Cibiyoyin sun haɗa da Jami’ar Ilorin, da Bells University of Technology da ke Ota, da Jami’ar Olabisi Onabanjo da ke Ago-Iwoye, da kuma Federal College of Education (Special) da ke Oyo.
Sauran sun haɗa da Human Development Initiatives (Grace House) da ke Lagos, wacce za ta fara aiki daga ranar 30 ga Afrilu, 2026. JAMB ta ce dukkan cibiyoyin PRCs da PTCs a faɗin ƙasar na ci gaba da gudanar da rajistar.
A ƙarshe, hukumar ta shawarci ɗalibai masu niyyar shiga da su gaggauta kammala rajistarsu kafin sabuwar ranar rufewa domin gujewa matsala.















Discussion about this post