ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, September 10, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Manyan Ƙalubale 5 Da Janar Christopher Musa Zai Fuskanta Domin Yin Nasara

by Abubakar Sulaiman
9 months ago

A matsayinsa na ministan tsaron Nijeriya Janar Christopher Musa mai ritaya yana riƙe da muƙami mai matuƙar nauyi a tsarin tsaron ƙasa. Yayin da matsalar rashin tsaro ke ci gaba da addabar sassa daban-daban na Nijeriya, nasararsa za ta ta’allaka ne kan yadda zai tunkari manyan ƙalubale masu zurfi da suka daɗe suna damun rundunonin tsaro.

Ɗaya daga cikin manyan ƙalubalen shi ne yaƙi da matsalolin tsaro masu yawa a lokaci guda. A Arewa maso Gabas akwai Boko Haram da ISWAP, a Arewa maso Yamma ana fama da ƴan bindiga da satar mutane, a Arewa ta tsakiya rikicin manoma da makiyaya na ƙara ta’azzara, yayin da a Kudu maso Gabas da Kudu maso Kudu ake fama da tashe-tashen hankula na ƴan aware da kuma fasa bututun mai. Wannan yanayi na sa Sojoji su bazu a fannoni da dama, lamarin da ke buƙatar tsari, da daidaito da dabaru na musamman domin kada a rasa nasarorin da aka samu a wasu yankuna.

  • ’Yan Majalisa Sun Roƙi Tinubu Ya Sake Duba Lamarin Janye Musu ’Yansanda
  • Shugaba Xi Ya Saurari Rahoton Aiki Daga Kantoman Yankin Musamman Na Macao

Wani babban ƙalubale shi ne dawo da amincewar jama’a ga rundunonin soji. A tsawon shekaru, zarge-zargen tauye haƙƙin ɗan Adam da asarar rayukan fararen hula sun raunana dangantaka tsakanin Sojoji da al’umma musamman bayan ƙarin kuskure kai harin ta sama. Samun sahihin bayanan sirri daga jama’a na da muhimmanci wajen yaƙi da ta’addanci, amma hakan ba zai yiwu ba idan babu amincewa. Don haka, Janar Musa na da alhaƙin ƙarfafa ladabi, da bin doka, da hulɗa mai kyau tsakanin rundunar Sojojin ƙasar da al’umma.

ADVERTISEMENT

Yawaitar makamai ba bisa ƙa’ida ba da raunin tsaron iyakoki ma na daga cikin manyan barazana. Iyakokin Nijeriya masu faɗi da rikice-rikice a yankin Sahel sun sa makamai na shiga hannun ƴan ta’adda da masu laifi cikin sauƙi. Janar Musa dole ne ya ƙarfafa haɗin gwuiwa tsakanin hukumomin tsaro, da leƙen asiri, da ƙasashe makwabta domin toshe hanyoyin shigo da makamai da kuma inganta sa ido a kan iyakoki. Shi da kansa ya taɓa cewa; yin katanga a iyakar hanya ce babba wajen tabbatar da tsaro.

A ƙarshe, tabbatar da walwala da jin daɗin dakarun soji, da haɗin gwuiwar hukumomin tsaro, da cikakken goyon bayan siyasa su ma manyan ƙalubale ne. Gajiya da rashin isassun kayan aiki, da jinkirin alawus na iya raunana ƙwarin gwuiwar sojoji. Haka kuma, rashin daidaito tsakanin sojoji, da ƴansanda da sauran hukumomi kan rage tasirin yaƙin tabbatar da tsaro.

LABARAI MASU NASABA

Ambaliyar Ruwa Ta Tafi Da Ɗalibai 2 A Abuja Da Abia

2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato

Nasarar Janar Christopher Musa za ta dogara ne kan yadda zai gyara waɗannan matsaloli, ya ƙarfafa rundunoni sama da na ƙasa tare da tabbatar da cewa matakan tsaro sun yi daidai da manufofin zaman lafiya da ci gaban ƙasa baki ɗaya.

Abubakar Sulaiman
Website |  + postsBio
  • Abubakar Sulaiman
    Iyalin El-Rufai Sun Bai Ministan Tsaro Wa’adin Kwana 7 Kan Zargin Rikicin Kudancin Kaduna
  • Abubakar Sulaiman
    Atiku Ya Zargi Gwamnatin Tarayya Da Cin Bashi Kamar Mashayin Da Kuɗi Ya Ƙarewa
  • Abubakar Sulaiman
    Boko Haram Ta Kai Hari Adamawa, Ana Fargabar Mutuwar Mutane 11
  • Abubakar Sulaiman
    Ƴan Bindiga Sun Kai Hari Sokoto, Sun Kashe Mutane 7, Sun Yi Garkuwa Da 12

MASU ALAKA

Ambaliyar Ruwa Ta Tafi Da Ɗalibai 2 A Abuja Da Abia
Manyan Labarai

Ambaliyar Ruwa Ta Tafi Da Ɗalibai 2 A Abuja Da Abia

September 10, 2026
2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato
Manyan Labarai

2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato

September 10, 2026
Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu
Manyan Labarai

Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu

September 9, 2026
Next Post
Sin Ta Yi Martani Kan Shirin TikTok Na Kafa Kamfanin Hadin Gwiwa Tare Da Masu Zuba Jari Na Amurka

Sin Ta Yi Martani Kan Shirin TikTok Na Kafa Kamfanin Hadin Gwiwa Tare Da Masu Zuba Jari Na Amurka

LABARAI MASU NASABA

Al’umma Sun Yaba Wa Sojoji Kan Yaƙar ’Yan Bindiga A Zamfara

Al’umma Sun Yaba Wa Sojoji Kan Yaƙar ’Yan Bindiga A Zamfara

September 10, 2026
Ambaliyar Ruwa Ta Tafi Da Ɗalibai 2 A Abuja Da Abia

Ambaliyar Ruwa Ta Tafi Da Ɗalibai 2 A Abuja Da Abia

September 10, 2026
’Yansanda Sun Kama Wadda Ta Yaɗa Labarin OPay Zai Daina Aiki A Nijeriya

’Yansanda Sun Kama Wadda Ta Yaɗa Labarin OPay Zai Daina Aiki A Nijeriya

September 10, 2026
2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato

2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato

September 10, 2026
Zabe: Gwamnatin Kano Ta Taƙaita Zirga-zirgar Mutane Da Ababen Hawa

Gwamna Yusuf Ya Umarci Jami’an Tsaro Su Gano Waɗanda Suka Kashe Danshagamu

September 10, 2026
Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

September 9, 2026
An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

September 9, 2026
Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba

Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba

September 9, 2026
Xi Ya Aike Da Gaisuwa Albarkacin Ranar Malamai Yana Mai Kira Da A Samar Da Matasa Masu Hazaka Domin Kara Farfado Da Kasa

Xi Ya Aike Da Gaisuwa Albarkacin Ranar Malamai Yana Mai Kira Da A Samar Da Matasa Masu Hazaka Domin Kara Farfado Da Kasa

September 9, 2026
Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu

Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu

September 9, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.