ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Manyan Ƙalubale 5 Da Janar Christopher Musa Zai Fuskanta Domin Yin Nasara

by Abubakar Sulaiman
7 months ago

A matsayinsa na ministan tsaron Nijeriya Janar Christopher Musa mai ritaya yana riƙe da muƙami mai matuƙar nauyi a tsarin tsaron ƙasa. Yayin da matsalar rashin tsaro ke ci gaba da addabar sassa daban-daban na Nijeriya, nasararsa za ta ta’allaka ne kan yadda zai tunkari manyan ƙalubale masu zurfi da suka daɗe suna damun rundunonin tsaro.

Ɗaya daga cikin manyan ƙalubalen shi ne yaƙi da matsalolin tsaro masu yawa a lokaci guda. A Arewa maso Gabas akwai Boko Haram da ISWAP, a Arewa maso Yamma ana fama da ƴan bindiga da satar mutane, a Arewa ta tsakiya rikicin manoma da makiyaya na ƙara ta’azzara, yayin da a Kudu maso Gabas da Kudu maso Kudu ake fama da tashe-tashen hankula na ƴan aware da kuma fasa bututun mai. Wannan yanayi na sa Sojoji su bazu a fannoni da dama, lamarin da ke buƙatar tsari, da daidaito da dabaru na musamman domin kada a rasa nasarorin da aka samu a wasu yankuna.

  • ’Yan Majalisa Sun Roƙi Tinubu Ya Sake Duba Lamarin Janye Musu ’Yansanda
  • Shugaba Xi Ya Saurari Rahoton Aiki Daga Kantoman Yankin Musamman Na Macao

Wani babban ƙalubale shi ne dawo da amincewar jama’a ga rundunonin soji. A tsawon shekaru, zarge-zargen tauye haƙƙin ɗan Adam da asarar rayukan fararen hula sun raunana dangantaka tsakanin Sojoji da al’umma musamman bayan ƙarin kuskure kai harin ta sama. Samun sahihin bayanan sirri daga jama’a na da muhimmanci wajen yaƙi da ta’addanci, amma hakan ba zai yiwu ba idan babu amincewa. Don haka, Janar Musa na da alhaƙin ƙarfafa ladabi, da bin doka, da hulɗa mai kyau tsakanin rundunar Sojojin ƙasar da al’umma.

ADVERTISEMENT

Yawaitar makamai ba bisa ƙa’ida ba da raunin tsaron iyakoki ma na daga cikin manyan barazana. Iyakokin Nijeriya masu faɗi da rikice-rikice a yankin Sahel sun sa makamai na shiga hannun ƴan ta’adda da masu laifi cikin sauƙi. Janar Musa dole ne ya ƙarfafa haɗin gwuiwa tsakanin hukumomin tsaro, da leƙen asiri, da ƙasashe makwabta domin toshe hanyoyin shigo da makamai da kuma inganta sa ido a kan iyakoki. Shi da kansa ya taɓa cewa; yin katanga a iyakar hanya ce babba wajen tabbatar da tsaro.

A ƙarshe, tabbatar da walwala da jin daɗin dakarun soji, da haɗin gwuiwar hukumomin tsaro, da cikakken goyon bayan siyasa su ma manyan ƙalubale ne. Gajiya da rashin isassun kayan aiki, da jinkirin alawus na iya raunana ƙwarin gwuiwar sojoji. Haka kuma, rashin daidaito tsakanin sojoji, da ƴansanda da sauran hukumomi kan rage tasirin yaƙin tabbatar da tsaro.

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan

Lalata Da Ƙaramar Yarinya: Kotu Ta Yanke Wa Tsoho Mai Shekara 75 Hukuncin Ɗaurin Shekara 10 A Ribas

Nasarar Janar Christopher Musa za ta dogara ne kan yadda zai gyara waɗannan matsaloli, ya ƙarfafa rundunoni sama da na ƙasa tare da tabbatar da cewa matakan tsaro sun yi daidai da manufofin zaman lafiya da ci gaban ƙasa baki ɗaya.

Abubakar Sulaiman
Website |  + postsBio
  • Abubakar Sulaiman
    Gwamnatin Tarayya Za Ta Ƙaddamar Da Tsarin Daƙile Rugujewar Gine-Gine
  • Abubakar Sulaiman
    Kotu Ta Hana INEC Amincewa Da Tarukan ADC Ƙarƙashin Jagorancin David Mark
  • Abubakar Sulaiman
    Mahara Sun Kashe Mutane 9 Ƴan Gida Ɗaya, Har Da Jariri Ɗan Wata 2 A Filato
  • Abubakar Sulaiman
    FIFA Na Nazarin Faɗaɗa Gasar Kofin Duniya Zuwa Ƙasashe 64

MASU ALAKA

‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan
Manyan Labarai

‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan

July 15, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga
Manyan Labarai

Lalata Da Ƙaramar Yarinya: Kotu Ta Yanke Wa Tsoho Mai Shekara 75 Hukuncin Ɗaurin Shekara 10 A Ribas

July 15, 2026
‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi
Manyan Labarai

‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi

July 15, 2026
Next Post
Sin Ta Yi Martani Kan Shirin TikTok Na Kafa Kamfanin Hadin Gwiwa Tare Da Masu Zuba Jari Na Amurka

Sin Ta Yi Martani Kan Shirin TikTok Na Kafa Kamfanin Hadin Gwiwa Tare Da Masu Zuba Jari Na Amurka

LABARAI MASU NASABA

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026
Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

July 15, 2026
‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan

‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan

July 15, 2026
Majalisa Ta Ba da Tallafin ₦50m Ga Iyalan Malamai Da Jami’an Tsaro Da Aka Kashe A Aikin Ceto A Oyo

Majalisa Ta Ba da Tallafin ₦50m Ga Iyalan Malamai Da Jami’an Tsaro Da Aka Kashe A Aikin Ceto A Oyo

July 15, 2026
Xi Ya Bukaci A Mayar Da Hankali Kan Bukatun Jama’a Yayin Rangadin Da Ya Yi A Shanghai

Xi Ya Bukaci A Mayar Da Hankali Kan Bukatun Jama’a Yayin Rangadin Da Ya Yi A Shanghai

July 15, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Lalata Da Ƙaramar Yarinya: Kotu Ta Yanke Wa Tsoho Mai Shekara 75 Hukuncin Ɗaurin Shekara 10 A Ribas

July 15, 2026
Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.