ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, June 14, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Manyan Ƙalubale 5 Da Janar Christopher Musa Zai Fuskanta Domin Yin Nasara

by Abubakar Sulaiman
6 months ago

A matsayinsa na ministan tsaron Nijeriya Janar Christopher Musa mai ritaya yana riƙe da muƙami mai matuƙar nauyi a tsarin tsaron ƙasa. Yayin da matsalar rashin tsaro ke ci gaba da addabar sassa daban-daban na Nijeriya, nasararsa za ta ta’allaka ne kan yadda zai tunkari manyan ƙalubale masu zurfi da suka daɗe suna damun rundunonin tsaro.

Ɗaya daga cikin manyan ƙalubalen shi ne yaƙi da matsalolin tsaro masu yawa a lokaci guda. A Arewa maso Gabas akwai Boko Haram da ISWAP, a Arewa maso Yamma ana fama da ƴan bindiga da satar mutane, a Arewa ta tsakiya rikicin manoma da makiyaya na ƙara ta’azzara, yayin da a Kudu maso Gabas da Kudu maso Kudu ake fama da tashe-tashen hankula na ƴan aware da kuma fasa bututun mai. Wannan yanayi na sa Sojoji su bazu a fannoni da dama, lamarin da ke buƙatar tsari, da daidaito da dabaru na musamman domin kada a rasa nasarorin da aka samu a wasu yankuna.

  • ’Yan Majalisa Sun Roƙi Tinubu Ya Sake Duba Lamarin Janye Musu ’Yansanda
  • Shugaba Xi Ya Saurari Rahoton Aiki Daga Kantoman Yankin Musamman Na Macao

Wani babban ƙalubale shi ne dawo da amincewar jama’a ga rundunonin soji. A tsawon shekaru, zarge-zargen tauye haƙƙin ɗan Adam da asarar rayukan fararen hula sun raunana dangantaka tsakanin Sojoji da al’umma musamman bayan ƙarin kuskure kai harin ta sama. Samun sahihin bayanan sirri daga jama’a na da muhimmanci wajen yaƙi da ta’addanci, amma hakan ba zai yiwu ba idan babu amincewa. Don haka, Janar Musa na da alhaƙin ƙarfafa ladabi, da bin doka, da hulɗa mai kyau tsakanin rundunar Sojojin ƙasar da al’umma.

ADVERTISEMENT

Yawaitar makamai ba bisa ƙa’ida ba da raunin tsaron iyakoki ma na daga cikin manyan barazana. Iyakokin Nijeriya masu faɗi da rikice-rikice a yankin Sahel sun sa makamai na shiga hannun ƴan ta’adda da masu laifi cikin sauƙi. Janar Musa dole ne ya ƙarfafa haɗin gwuiwa tsakanin hukumomin tsaro, da leƙen asiri, da ƙasashe makwabta domin toshe hanyoyin shigo da makamai da kuma inganta sa ido a kan iyakoki. Shi da kansa ya taɓa cewa; yin katanga a iyakar hanya ce babba wajen tabbatar da tsaro.

A ƙarshe, tabbatar da walwala da jin daɗin dakarun soji, da haɗin gwuiwar hukumomin tsaro, da cikakken goyon bayan siyasa su ma manyan ƙalubale ne. Gajiya da rashin isassun kayan aiki, da jinkirin alawus na iya raunana ƙwarin gwuiwar sojoji. Haka kuma, rashin daidaito tsakanin sojoji, da ƴansanda da sauran hukumomi kan rage tasirin yaƙin tabbatar da tsaro.

LABARAI MASU NASABA

Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle

Nasarar Janar Christopher Musa za ta dogara ne kan yadda zai gyara waɗannan matsaloli, ya ƙarfafa rundunoni sama da na ƙasa tare da tabbatar da cewa matakan tsaro sun yi daidai da manufofin zaman lafiya da ci gaban ƙasa baki ɗaya.

Abubakar Sulaiman
Website |  + postsBio
  • Abubakar Sulaiman
    Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle
  • Abubakar Sulaiman
    Tsohon Kakakin Ma’aikatar Tsaro Rabe Abubakar Ya Rasu A Hannun ‘Ƴan Bindiga
  • Abubakar Sulaiman
    Yadda Matata Ta Daina Girki, Ta Ke Lakaɗamin Duka — Miji Ya Koka
  • Abubakar Sulaiman
    Zan Saki Nnamdi Kanu Idan Na Zama Shugaban Ƙasa – Peter Obi

MASU ALAKA

Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar
Manyan Labarai

Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

June 13, 2026
Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle
Manyan Labarai

Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle

June 13, 2026
Tsohon Kakakin Ma’aikatar Tsaro Rabe Abubakar Ya Rasu A Hannun ‘Ƴan Bindiga
Manyan Labarai

Tsohon Kakakin Ma’aikatar Tsaro Rabe Abubakar Ya Rasu A Hannun ‘Ƴan Bindiga

June 13, 2026
Next Post
Sin Ta Yi Martani Kan Shirin TikTok Na Kafa Kamfanin Hadin Gwiwa Tare Da Masu Zuba Jari Na Amurka

Sin Ta Yi Martani Kan Shirin TikTok Na Kafa Kamfanin Hadin Gwiwa Tare Da Masu Zuba Jari Na Amurka

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (1)

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (1)

June 13, 2026
Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

June 13, 2026
Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

June 13, 2026
Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

June 13, 2026

Sake Jan Damarar Soja Da Japan Ke Yi Karin Alama Ce Mai Hadari

June 13, 2026
NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

June 13, 2026
Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

June 13, 2026
Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

June 13, 2026
Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

June 13, 2026
Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

June 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.