ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 26, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Manyan Nasarorin Da Dr Matawalle Ya Samar A Sashen Tsaro

by Leadership Hausa
6 months ago

Daga Bashir Aliyu

Tun da aka nada shi a matsayin Karamin Ministan Tsaro a 2023, Dr Bello Matawalle ya sake kawo sabon dabaru ta fannin tsaro, nazari da kuma daukar matakan da suka jibi dasa tubalin ginin sashen tsaro na kasa. A lokacinsa an samu manyan nasarori a bangaren yaki da ta’addanci, zamanantar da rundunar soja, da kuma tabbatar da zaman lafiyar kasa, wadanda ne suka sa ake kallonsa a matsayin daya daga cikin manyan mutunen da suke bayar da muhimmiyar gudummawa wurin yaki da rashin tsaro.

A lokacin jagorancinsa ne Ma’aikatar Tsaro ta samu manya-manyan nasarori domin kawo zaman lafiya a kasa. Wadannan nasarori su ne:

 

ADVERTISEMENT

Nasarori A Kan Ta’addanci Da Satan Mutane

Daya daga cikin manyan nasarorin da Dr Bello Matawalle ya samu shi ne kaimi da aka yi wurin yaki da ta’addanci. Ta hanyar kyautata hadin gwiwa da Sojojin kasa, da Sojojin Sama da sauran hukumomin tsaro, an yi rugu-rugu da matattaran ‘yan ta’adda a Arewa maso Gabas, wanda hakan ya yi sanadiyar raguwar hare-hare. A Arewa Maso Yamma kuwa, gagarumar gudummawa da ma’aikatar tsaro a karkashinsa ta amfani da karfin soja ya yi mummunar illa ga matattarar ‘yan ta’adda wanda hakan ya kyautata fata da al’umma ke da shi cewa an kusan share musu hawaye.

LABARAI MASU NASABA

An Nemi Shugabanni Su Rungumi Tafarkin Adalci A Tsakanin Al’ummunsu

Ƴan Bindiga Sun Tilasta Wa Ƙauyukan Sakkwato Biyan Sabon Haraji

 

Kula Da Walwalar Sojoji Da Karfafa Musu Gwiwa

Ganin cewa karfin Sojan Nijeriya ya dogara ne a rundunarta, Dr Bello Matawalle ya inganta hanyoyin walwalar sojojin ta hanyar biyan su kudin alawus a kan lokaci, kyautata matsuguninsu, da kuma samun ingantaccen kiwon lafiya. Wannan ya kara azama wa sojojin da suke gwabza yaki a fagagen fama.

 

Zamanantar da Dakarun Sojoji

Ganin bukatar gaggawa da ke akwai na zamanan tar da sojojin Nigeriya, Dr Bello Matawalle ya samar da waraka ta hanyar samar da sabbin makamai na zamani, da jirage marasa matuki don tattara bayanai da kuma kayan ayyuka da sojoji ke bukata lokacin yaki.

Wadannan kayayyaki sun inganta dabarun da sojoji ke amfani da su ta hanyar raguwar yawan sojojin da ke rasa rayukansu da kuma karuwar nasarori a duk lokacin da aka fita ba-ta-kashi.

 

Raguwar sace-sacen mai da zagon kasa wa tattalin arziki.

Tattalin arzikin Nijeriya ya jima na fama da yawan watan danyen mai a yankin Niger Delta.

Karkashin jagorancin Matawalle, an samu karuwar aikace-aikacen da suka hada da hadin gwiwar sojojin ruwa wadanda suka hada da lalata cibiyoyin sace danyen mai wanda hakan ya haifar da karuwar danyen mai da ake fitar da kuma karin kudaden shiga ga kasa.

 

Karfafa mu’amala da hadin gwiwa da kaware a yankin Africa da kasa-da-kasa.

Yawancin matsalolin tsaro ya kan wuce iyakar kasa, saboda haka ne Dr Matawalle bai yi kasa a gwiwa ba wurin daukar matakan kulla kawance da makwabtan kasashe irin su Chad, da Niger da Kamaru, da sauran kawayen kasashe irin su Amurka, Birtaniya da Tarayyar Turai wanda ya inganta yanda ake tattara bayanai da kuma musayar bayanan sirri. Hakan ya sa ‘yan ta’adda da masu aikata muggan laifuka ke samun wahalar samun maboya.

 

Karfafa kere-keren kayan yaki a gida

Bisa umurnin da Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya bayar na tunanin dogaro da Kai a fannin tsaro, Dr Bello Matawalle ya yi kokarin agaza wa Hukumar Samar da Kayan Yaki ta Nijeriya (DICON) domin kara samar da makaman yaki a gida Nijeriya. Wannan mataki ya rage dogaro da kasashen waje da kuma karfafa tattalin arzikin tsaron Nijeriya.

Baya ga bangaren yaki, Dr Bello Matawalle yana cigaba da jaddada muhimmancin aiki da al’umma domin dawo da tsaro. Wannan kiranye da yake yi wurin neman tattaunawa, da sasanci da kuma ayyukan ci gaba a yankunan da ake rikici sun taimaka matuka gaya wajen dinke rashin yarda tsakanin jami’an tsaro da kuma fararen hula, wanda hakan zai haifar da zaman lafiya mai dorewa.

Jagorancin Dr Bello Matawalle ya nuna aiki ba kama kafar yaro, sabbin dabaru, da kuma kishin kasa. Nasarorinsa ya nuna irin fahimtarsa a matsalolin tsaron Nijeriya da kuma irin niyyar da gwamnati ke da shi wurin magance su.

 

Bashir Aliyu dan jarida ne mai nazarin al’amuran da suka shafi siyasa da tsaro.

Leadership Hausa
Website |  + postsBio
  • Leadership Hausa
    Batun Dakile Shan Taba Sigari A Tsakanin Yara A Nijeriya
  • Leadership Hausa
    Har Yanzu Akwai Sauran Rina A Kaba Game Da Makomar Yara A Nijeriya
  • Leadership Hausa
    Yadda Arsenal Ta Lashe Gasar Firimiya Bayan Shekara 22
  • Leadership Hausa
    Bukatar Kawo Karshen Akidar Kyamar Baki A Kasar Afirka Ta Kudu

MASU ALAKA

Nijeriya
Rahotonni

An Nemi Shugabanni Su Rungumi Tafarkin Adalci A Tsakanin Al’ummunsu

June 20, 2026
Ambaliyar Ruwa Ta Lalata Gidaje 14,940 A Sokoto
Rahotonni

Ƴan Bindiga Sun Tilasta Wa Ƙauyukan Sakkwato Biyan Sabon Haraji

June 20, 2026
IMF
Rahotonni

Tattalin Arziƙin Ƙasa: Masana Sun Buƙaci Tinubu Ya Yi Hattara Da Shawarar IMF

June 20, 2026
Next Post
APC Na Dab Da Mallakar Jihohi Sama Da 30

APC Na Dab Da Mallakar Jihohi Sama Da 30

LABARAI MASU NASABA

Sin Da Amurka Sun Amince Da Kafa Majalisar Kasuwanci

Sin Da Amurka Sun Amince Da Kafa Majalisar Kasuwanci

June 25, 2026
Mukaddashiyar Shugaban Venezuela Ta Yi Godiya Da Aniyar Sin Ta Ba Su Agaji

Mukaddashiyar Shugaban Venezuela Ta Yi Godiya Da Aniyar Sin Ta Ba Su Agaji

June 25, 2026
Shugabar Namibia Ta Kaddamar Da Dakin Baje Kolin Kimiyya Da Sinawa Suka Gina

Shugabar Namibia Ta Kaddamar Da Dakin Baje Kolin Kimiyya Da Sinawa Suka Gina

June 25, 2026
Gwamna Lawal Ya Yi Alƙawarin Bayar Da Ƙarin Tallafi Ga Jami’an Tsaro A Zamfara

Gwamna Lawal Ya Yi Alƙawarin Bayar Da Ƙarin Tallafi Ga Jami’an Tsaro A Zamfara

June 25, 2026
Salon Jagorancin Kasar Sin Na Ingiza Samar Da Ci Gaba Mai Nagarta

Salon Jagorancin Kasar Sin Na Ingiza Samar Da Ci Gaba Mai Nagarta

June 25, 2026
NNPCL Ya Rage Farashin Man Fetur Zuwa ₦860 Kan Kowacce Lita – IPMAN

Dangote Ya Rage Farashin Fetur Zuwa N1,125 Kan Kowace Lita

June 25, 2026
Adadin Injunan Samar Da Wutar Lantarki Da Sin Ya Wuce Kilowatts Awa Biliyan 4, Wato Ya Kai Ga Matsayi Na Farko A Duniya

Adadin Injunan Samar Da Wutar Lantarki Da Sin Ya Wuce Kilowatts Awa Biliyan 4, Wato Ya Kai Ga Matsayi Na Farko A Duniya

June 25, 2026
Gwamna Yusuf Ya Naɗa Muhuyi A Matsayin Shugaban Kwamitin Yaƙi Da Miyagun Ƙwayoyi A Kano

Gwamna Yusuf Ya Naɗa Muhuyi A Matsayin Shugaban Kwamitin Yaƙi Da Miyagun Ƙwayoyi A Kano

June 25, 2026
Wani Gidan Adana Kayan Tarihi Na Sin Ya Fitar Da Rahoton Yadda Dakarun Japan Suka Rika Zubawa Mutane Jinin Dabbobi Yayin Yakin Duniya Na Biyu

Wani Gidan Adana Kayan Tarihi Na Sin Ya Fitar Da Rahoton Yadda Dakarun Japan Suka Rika Zubawa Mutane Jinin Dabbobi Yayin Yakin Duniya Na Biyu

June 25, 2026
Wang Yi Ya Yi Kira Da A Gaggauta Bude Mashigin Hormuz

Wang Yi Ya Yi Kira Da A Gaggauta Bude Mashigin Hormuz

June 25, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.