ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Masana Tattalin Arziki Sun Yi Watsi Da Rahoton NBS Kan Tattalin Arziki

by Yusuf Shuaibu
4 days ago

Masana tattalin arziki sun yi watsi da rahoton hukumar ƙididdiga ta ƙasa (NBS) na farkon zangon 2026, inda suka tabbatar da cewa tsadar rayuwa a Nijeriya na ƙara ta’azzara.

Idan za a iya tunawa dai, rahoton NBS da aka fitar a ranar Litinin ya nuna cewa tattalin arzikin Nijeriya ya ƙaru da kashi 3.89 cikin ɗari a rubu’in farko na shekara ta 2026 idan aka kwatanta da kashi 3.13 da aka samu a rubu’in farko na bara.

Rahoton ya nuna cewa ɓangaren ayyuka ya bayar da gudummawa mafi girma ga jimillar GDP da kashi 57.73, sannan aikin gona da kashi 23.16 da masana’antu da kashi 19.11.

ADVERTISEMENT

Rahoton NBS ya ƙara nuna cewa GDP ya kai naira tiriliyan 110.79, yayin da GDP na haƙiƙa ya kasance tiriliyan 51.36, inda ɓangaren ba na man fetur ba ke ɗauke da kashi 96.08 kan kashi 3.92 na sashen man fetur.

Rahotannin, kamar sauran bayanan GDP na NBS, sun tayar da martani daga ƴan Nijeriya da masu ruwa da tsaki kan hauhawar tsadar rayuwa a ƙasar.

LABARAI MASU NASABA

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

An ruwaito cewa tashin farashin makamashi na iskar gas da na girki ke sama da naira 1,500 a kowace kilogram, fetur ya kai naira 1,400 a kowace lita, da dizal kan naira 2,000 a kowace lita sakamakon rikicin gabas ta tsakiya da ya shafe kusan watanni uku.

Da yake magana kan lamarin, tsohon shugaban kuma shugaban cibiyar ‘Chartered Institute of Bankers’ (CIBN), Mazi Okechukwu Unegbu da shugaban ƙungiyar abokan huɗɗar bankun Nijeriya, Dakta Uju Ogunbunka, sun ce GDP ɗin ƙasar bai nuna tasiri ga rayuwar talakawa da ke fama da tsadar rayuwa.

A nasa ɓangaren, Unegbu ya ce duk da ci gaban da aka samu a adadin GDP na ƙasar, rayuwar talakawan Nijeriya ba ta inganta ba.

Unegbu ya ce ci gaban tattalin arziki da aka bayar bai canza zuwa mafi kyawun yanayin rayuwa ga ƴan Nijeriya na yau da kullum ba, yana jaddada cewa hauhawar tsadar rayuwa ya ci gaba da tsananta duk da ingantattun bayanan GDP.

A cewarsa, masana tattalin arziki yanzu suna la’akari da hanyoyi don sake auna GDP don ya dacewa da haƙiƙanin gaskiyar rayuwar ƴan ƙasa ke fuskanta a kan tituna.

Unegbu ya ce ƙaruwar farashin kayayyakin amfani da ayyuka sun ci gaba da ƙaruwa a ƙarƙashin wannan gwamnatin, wanda ke sanya rayuwa ta zama mai wahala ga ƴan Nijeriya.

Kazalika, Ogunbunka ya ce sabon rahoton NBS na GDP ba ya nuna gaskiyar yanayin da ƴan Nijeriya ke fuskanta a rayuwar yau da kullum.

Ya ce cewa duk da batun ci gaban tattalin arziki da aka ruwaito, miliyoyin ƴan Nijeriya har yanzu suna fama da tsadar rayuwa da hauhawar farashin kayayyaki da taɓarɓarewar tattalin arziki.

“Abin takaici, kyawawan ƙididdiga ba su daidaita da gaskiya lamari ba. Rahoton NBS kan ci gaban GDP zuwa kashi 3.89 ya bar fiye da yadda aka zata kan yayin da mutane ke fama da tashin rayuwa,” in ji shi.

Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Alƙawarin Wa’adi Ɗaya Na Peter Obi Ya Raba Kawunan Ƴan Arewa
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    ‘Yan Majalisar Wakilai 50 Da Suka Rasa Tikitin Takara A Zaɓen Fid Da Gwani Na APC
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Zaɓen Fitar Da Gwani: APC Na Fuskantar Barazanar Tawaye
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027: Rashin Hadin Kan Atiku Da Obi Da Kwankwaso Na Iya Taimaka Wa Tazarcen Tinubu

MASU ALAKA

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli
Labarai

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro
Manyan Labarai

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Zamfara Ta Shirya Tallafa Wa Mata Da Masu Ƙaramin Ƙarfi Fiye Da Miliyan Ɗaya
Manyan Labarai

Gwamnatin Zamfara Ta Shirya Tallafa Wa Mata Da Masu Ƙaramin Ƙarfi Fiye Da Miliyan Ɗaya

June 3, 2026
Next Post
Na Cika Kashi 90 Cikin 100 Na Alƙawuran Yaƙin Neman Zaɓe Na – In Ji Gwamnan Kano

Na Cika Kashi 90 Cikin 100 Na Alƙawuran Yaƙin Neman Zaɓe Na – In Ji Gwamnan Kano

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026
Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

June 3, 2026
An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Magadan Gari Na 2026 A Beijing

An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Magadan Gari Na 2026 A Beijing

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.