ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Masana Tattalin Arziki Sun Yi Watsi Da Rahoton NBS Kan Tattalin Arziki

by Yusuf Shuaibu
3 weeks ago

Masana tattalin arziki sun yi watsi da rahoton hukumar ƙididdiga ta ƙasa (NBS) na farkon zangon 2026, inda suka tabbatar da cewa tsadar rayuwa a Nijeriya na ƙara ta’azzara.

Idan za a iya tunawa dai, rahoton NBS da aka fitar a ranar Litinin ya nuna cewa tattalin arzikin Nijeriya ya ƙaru da kashi 3.89 cikin ɗari a rubu’in farko na shekara ta 2026 idan aka kwatanta da kashi 3.13 da aka samu a rubu’in farko na bara.

Rahoton ya nuna cewa ɓangaren ayyuka ya bayar da gudummawa mafi girma ga jimillar GDP da kashi 57.73, sannan aikin gona da kashi 23.16 da masana’antu da kashi 19.11.

ADVERTISEMENT

Rahoton NBS ya ƙara nuna cewa GDP ya kai naira tiriliyan 110.79, yayin da GDP na haƙiƙa ya kasance tiriliyan 51.36, inda ɓangaren ba na man fetur ba ke ɗauke da kashi 96.08 kan kashi 3.92 na sashen man fetur.

Rahotannin, kamar sauran bayanan GDP na NBS, sun tayar da martani daga ƴan Nijeriya da masu ruwa da tsaki kan hauhawar tsadar rayuwa a ƙasar.

LABARAI MASU NASABA

An Kashe Mutum 2, Takwas Sun Jikkata Yayin Rikicin A Bauchi

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

An ruwaito cewa tashin farashin makamashi na iskar gas da na girki ke sama da naira 1,500 a kowace kilogram, fetur ya kai naira 1,400 a kowace lita, da dizal kan naira 2,000 a kowace lita sakamakon rikicin gabas ta tsakiya da ya shafe kusan watanni uku.

Da yake magana kan lamarin, tsohon shugaban kuma shugaban cibiyar ‘Chartered Institute of Bankers’ (CIBN), Mazi Okechukwu Unegbu da shugaban ƙungiyar abokan huɗɗar bankun Nijeriya, Dakta Uju Ogunbunka, sun ce GDP ɗin ƙasar bai nuna tasiri ga rayuwar talakawa da ke fama da tsadar rayuwa.

A nasa ɓangaren, Unegbu ya ce duk da ci gaban da aka samu a adadin GDP na ƙasar, rayuwar talakawan Nijeriya ba ta inganta ba.

Unegbu ya ce ci gaban tattalin arziki da aka bayar bai canza zuwa mafi kyawun yanayin rayuwa ga ƴan Nijeriya na yau da kullum ba, yana jaddada cewa hauhawar tsadar rayuwa ya ci gaba da tsananta duk da ingantattun bayanan GDP.

A cewarsa, masana tattalin arziki yanzu suna la’akari da hanyoyi don sake auna GDP don ya dacewa da haƙiƙanin gaskiyar rayuwar ƴan ƙasa ke fuskanta a kan tituna.

Unegbu ya ce ƙaruwar farashin kayayyakin amfani da ayyuka sun ci gaba da ƙaruwa a ƙarƙashin wannan gwamnatin, wanda ke sanya rayuwa ta zama mai wahala ga ƴan Nijeriya.

Kazalika, Ogunbunka ya ce sabon rahoton NBS na GDP ba ya nuna gaskiyar yanayin da ƴan Nijeriya ke fuskanta a rayuwar yau da kullum.

Ya ce cewa duk da batun ci gaban tattalin arziki da aka ruwaito, miliyoyin ƴan Nijeriya har yanzu suna fama da tsadar rayuwa da hauhawar farashin kayayyaki da taɓarɓarewar tattalin arziki.

“Abin takaici, kyawawan ƙididdiga ba su daidaita da gaskiya lamari ba. Rahoton NBS kan ci gaban GDP zuwa kashi 3.89 ya bar fiye da yadda aka zata kan yayin da mutane ke fama da tashin rayuwa,” in ji shi.

Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

MASU ALAKA

An Kashe Mutum 2, Takwas Sun Jikkata Yayin Rikicin A Bauchi
Labarai

An Kashe Mutum 2, Takwas Sun Jikkata Yayin Rikicin A Bauchi

June 24, 2026
Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga
Manyan Labarai

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

June 24, 2026
Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100
Labarai

Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

June 23, 2026
Next Post
Na Cika Kashi 90 Cikin 100 Na Alƙawuran Yaƙin Neman Zaɓe Na – In Ji Gwamnan Kano

Na Cika Kashi 90 Cikin 100 Na Alƙawuran Yaƙin Neman Zaɓe Na – In Ji Gwamnan Kano

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

An Kashe Mutum 2, Takwas Sun Jikkata Yayin Rikicin A Bauchi

An Kashe Mutum 2, Takwas Sun Jikkata Yayin Rikicin A Bauchi

June 24, 2026
Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

June 24, 2026
Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

June 23, 2026
Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

June 23, 2026
Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

June 23, 2026
Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

June 23, 2026
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

’Yansanda Sun Kama Mutane 57 Da Ake Zargi Da Ayyukan Ta’addanci A Adamawa

June 23, 2026
Li Qiang Ya Gana Da Firaministan Kasar Guinea

Li Qiang Ya Gana Da Firaministan Kasar Guinea

June 23, 2026
Maniyyatan Nijeriya

Hajjin 2026: NAHCON Ta Kammala Jigilar Alhazan Nijeriya Daga Saudiyya

June 23, 2026
Kamfanin Sin Ya Kammala Babban Aikin Samar Da Ruwa A Babban Birnin Nijeriya

Kamfanin Sin Ya Kammala Babban Aikin Samar Da Ruwa A Babban Birnin Nijeriya

June 23, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.