Masana tattalin arziki sun yi watsi da rahoton hukumar ƙididdiga ta ƙasa (NBS) na farkon zangon 2026, inda suka tabbatar da cewa tsadar rayuwa a Nijeriya na ƙara ta’azzara.
Idan za a iya tunawa dai, rahoton NBS da aka fitar a ranar Litinin ya nuna cewa tattalin arzikin Nijeriya ya ƙaru da kashi 3.89 cikin ɗari a rubu’in farko na shekara ta 2026 idan aka kwatanta da kashi 3.13 da aka samu a rubu’in farko na bara.
Rahoton ya nuna cewa ɓangaren ayyuka ya bayar da gudummawa mafi girma ga jimillar GDP da kashi 57.73, sannan aikin gona da kashi 23.16 da masana’antu da kashi 19.11.
Rahoton NBS ya ƙara nuna cewa GDP ya kai naira tiriliyan 110.79, yayin da GDP na haƙiƙa ya kasance tiriliyan 51.36, inda ɓangaren ba na man fetur ba ke ɗauke da kashi 96.08 kan kashi 3.92 na sashen man fetur.
Rahotannin, kamar sauran bayanan GDP na NBS, sun tayar da martani daga ƴan Nijeriya da masu ruwa da tsaki kan hauhawar tsadar rayuwa a ƙasar.
An ruwaito cewa tashin farashin makamashi na iskar gas da na girki ke sama da naira 1,500 a kowace kilogram, fetur ya kai naira 1,400 a kowace lita, da dizal kan naira 2,000 a kowace lita sakamakon rikicin gabas ta tsakiya da ya shafe kusan watanni uku.
Da yake magana kan lamarin, tsohon shugaban kuma shugaban cibiyar ‘Chartered Institute of Bankers’ (CIBN), Mazi Okechukwu Unegbu da shugaban ƙungiyar abokan huɗɗar bankun Nijeriya, Dakta Uju Ogunbunka, sun ce GDP ɗin ƙasar bai nuna tasiri ga rayuwar talakawa da ke fama da tsadar rayuwa.
A nasa ɓangaren, Unegbu ya ce duk da ci gaban da aka samu a adadin GDP na ƙasar, rayuwar talakawan Nijeriya ba ta inganta ba.
Unegbu ya ce ci gaban tattalin arziki da aka bayar bai canza zuwa mafi kyawun yanayin rayuwa ga ƴan Nijeriya na yau da kullum ba, yana jaddada cewa hauhawar tsadar rayuwa ya ci gaba da tsananta duk da ingantattun bayanan GDP.
A cewarsa, masana tattalin arziki yanzu suna la’akari da hanyoyi don sake auna GDP don ya dacewa da haƙiƙanin gaskiyar rayuwar ƴan ƙasa ke fuskanta a kan tituna.
Unegbu ya ce ƙaruwar farashin kayayyakin amfani da ayyuka sun ci gaba da ƙaruwa a ƙarƙashin wannan gwamnatin, wanda ke sanya rayuwa ta zama mai wahala ga ƴan Nijeriya.
Kazalika, Ogunbunka ya ce sabon rahoton NBS na GDP ba ya nuna gaskiyar yanayin da ƴan Nijeriya ke fuskanta a rayuwar yau da kullum.
Ya ce cewa duk da batun ci gaban tattalin arziki da aka ruwaito, miliyoyin ƴan Nijeriya har yanzu suna fama da tsadar rayuwa da hauhawar farashin kayayyaki da taɓarɓarewar tattalin arziki.
“Abin takaici, kyawawan ƙididdiga ba su daidaita da gaskiya lamari ba. Rahoton NBS kan ci gaban GDP zuwa kashi 3.89 ya bar fiye da yadda aka zata kan yayin da mutane ke fama da tashin rayuwa,” in ji shi.















Discussion about this post