ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mata Ne Ke Rike Da Kaso 40 Na Matsakaitan Sana’oi —Hannatu Musawa

by Abubakar Abba and Sulaiman
3 months ago
Musawa

Masu ruwa da tsaki, a fannin hada-hadar kudi a kasar nan, sun yi kira ga gwamnatin tarayya da ta gaggauta samar da tsari, domin a dakile shingen da ke hana matan kasar shiga a dama da su, a fannin tattalin arzikin kasar nan.

Sun yi gargadi da cewa, duk da cewa, matan kasar ne ke da kaso 40 a cikin dari na matsakaita da kananan sana’oin amma har yanzu, suna ci gaba da fuskantar gibi ne samun rancen kudaden da za su ci gaba da bunkasa kasuwancin su.

  • INEC Ta Gyara Jadawalin Zaben 2027 Tare Da Tsawaita Wa’adin Mika Rajistar Jam’iyyun Siyasa
  • NPA Ta Kaddamar Da Tsarin Kara Bunkasa Fitar Da Kayan Da Basu Da Nasaba Da Fannin Mai

Ministar al’adu da kirkirar tattalin arziki Hannatu Musawa da kuma tsohuwar ministar ilimi Oby Ezekwesili, suka bayyana wannan damuwar a jawabinssu da ban da ban a taron ranar mata ta duniya na bana, na wannan shekarar da aka gudanar a kwananbaya a jihar Legas.

ADVERTISEMENT

Sun zayyano kalubalen da mata masu gudanar da kanana da matsakaitan sana’oin ke ci gaba da fuskanta wajen samun rancen kudaden daga bankuna da cibiyoyin hada-hadar kudade, na kasar nan wanda hakan ke janyo masu na shiga a dama da su, a fagen kara ciyar da tattalin arzikin kasar gaba..

Musawa ta yi nuni da cewa, har yanzu matan kasar nan, su ne a kan gaba a,fannin bunkasa tattalin arzikin kasar nan, amma abin takaici, suna ci gaba da fuskantar kalubale na samun kudaden da za su ci gaba da gudanar da kasuwancin su.

LABARAI MASU NASABA

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

Ta kara da cewa, hakan na kuma dakile su, daga samun damar kara fadada kasuwanin su,inda ta yi nuni da cewa, hakan,babbar koma baya ne, ga kasuwanin su.

Sai dai, a bangaren gwamatin tarayya, ministar ta bayyana cewa, domin a magance wannan matsalar na ci gaba da samar da shirye-shiye, bisa nufin samar wa da mata’yan kasuwa kudaden da za su ci gaba da bunkasa kasuwancin su, musamman ta hanyar ma’aikatar da take shugabanta.

Ta jaddada cewa ,akwai bukatar a sanya mata a kasar a cikin batun gudanar da tsare-tsare da kuma daukar matakan bayar da shawara, musamman duba da fahimtar al’amuran yau da kullum da su ke da shi, a bangaren gudanar da shugabanci da kuma shuganci, a bangaren tafiyar da tattalin arzikin kasar.

Ita kuwa a na ta jawabin tsohuwar ministar ta ilimi ta bayyana cewa, shigen da ke dakile matan’yan kasuwa na kasar nan na haifar da gagarumin cikas wajen bayar da gudunmawar su, a fagen kara bunkasa fannonin tattalin arzikin kasar

Ta buga misali kan hujjar yadda a kasashen duniya, ake samarwa da mata ‘yan kasuwa, kudaden da suke ci gaba da habaka sana’oin su,wanda hakan, ke kara habaka fannin tattalin arzikin kasashen.

A cewar tsohuwar ministan magance wannan matsalar, ba wai kawai ta tallawa sana’oin su aka yi ba, har da kuma kara karfafa fannin tattalin arzikin kasar da kuma bayar da damar, gudanar da yin gasa, a fannin kasuwanin kasar.

“Akwai bukatar a kawar da wannan shingen da janyo mata ‘ yan kasuwa na kasar samun kudaden da za su bunkasa kasuwancin su, inda hakan zai ba su damar kara fadada kasuwancin su.

Ta buga misali da fannin aikin noma wanda ta bayyana cewa, muna gsni kaso 30 a cikin dari matan da suka rungumi fannin na bayar da gagarumar gudunmawa,” .Inji tsohuwar ministan.

Ta alakanta wannan matsalar ta gibin na ssmun kudaden ga matan’yan kasuwa, a matsayin babban abin da ke taka masu birki a fagen kasuwancin su.

Ta yi gargadi da cewa, ci gaba da barin wannan gibin, za a ci gaba da dakile matan ‘yan kasuwa na kasar daga bayar da ta su gudunmawar wajen ciyar da tattalin arzikin kasar gaba.

Ta kuma bayar da shawarar da a yi hadaka a tsakanin masana’antu masu zaman kansu da kuma masu kirkiro da dokoki a kasar domin a janyo matan kasar ‘yan kasuwa domin a rinka tattaunawa da su a fannin tattalin arzikin kasar.

Musawa
Abubakar Abba
+ posts Bio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Nazari A Kan Wasu Cututtuka Da Ke Shafar Dabbobi Lokacin Damina
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Ɗantsoho Ya Jinjina Wa Hukumar FCC Kan Sabbin Sauye-Sauyen Da Ta Samar
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    “Mutunta Ƴancin Addinai Ita Ce Hanyar Wanzar Da Zaman Lafiya A Kaduna”
Musawa
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya
  • Sulaiman
    Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026
  • Sulaiman
    An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”
  • Sulaiman
    Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

MASU ALAKA

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu
Labarai

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga
Manyan Labarai

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi
Labarai

Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

July 14, 2026
Next Post
Rikicin ADC: Lauya Ya Caccaki Kotun Ɗaukaka Ƙara

Rikicin ADC: Lauya Ya Caccaki Kotun Ɗaukaka Ƙara

LABARAI MASU NASABA

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

July 14, 2026
Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

July 14, 2026
Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

July 14, 2026
CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.