ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mata Ne Ke Rike Da Kaso 40 Na Matsakaitan Sana’oi —Hannatu Musawa

by Abubakar Abba and Sulaiman
5 months ago
Musawa

Masu ruwa da tsaki, a fannin hada-hadar kudi a kasar nan, sun yi kira ga gwamnatin tarayya da ta gaggauta samar da tsari, domin a dakile shingen da ke hana matan kasar shiga a dama da su, a fannin tattalin arzikin kasar nan.

Sun yi gargadi da cewa, duk da cewa, matan kasar ne ke da kaso 40 a cikin dari na matsakaita da kananan sana’oin amma har yanzu, suna ci gaba da fuskantar gibi ne samun rancen kudaden da za su ci gaba da bunkasa kasuwancin su.

  • INEC Ta Gyara Jadawalin Zaben 2027 Tare Da Tsawaita Wa’adin Mika Rajistar Jam’iyyun Siyasa
  • NPA Ta Kaddamar Da Tsarin Kara Bunkasa Fitar Da Kayan Da Basu Da Nasaba Da Fannin Mai

Ministar al’adu da kirkirar tattalin arziki Hannatu Musawa da kuma tsohuwar ministar ilimi Oby Ezekwesili, suka bayyana wannan damuwar a jawabinssu da ban da ban a taron ranar mata ta duniya na bana, na wannan shekarar da aka gudanar a kwananbaya a jihar Legas.

ADVERTISEMENT

Sun zayyano kalubalen da mata masu gudanar da kanana da matsakaitan sana’oin ke ci gaba da fuskanta wajen samun rancen kudaden daga bankuna da cibiyoyin hada-hadar kudade, na kasar nan wanda hakan ke janyo masu na shiga a dama da su, a fagen kara ciyar da tattalin arzikin kasar gaba..

Musawa ta yi nuni da cewa, har yanzu matan kasar nan, su ne a kan gaba a,fannin bunkasa tattalin arzikin kasar nan, amma abin takaici, suna ci gaba da fuskantar kalubale na samun kudaden da za su ci gaba da gudanar da kasuwancin su.

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

Ta kara da cewa, hakan na kuma dakile su, daga samun damar kara fadada kasuwanin su,inda ta yi nuni da cewa, hakan,babbar koma baya ne, ga kasuwanin su.

Sai dai, a bangaren gwamatin tarayya, ministar ta bayyana cewa, domin a magance wannan matsalar na ci gaba da samar da shirye-shiye, bisa nufin samar wa da mata’yan kasuwa kudaden da za su ci gaba da bunkasa kasuwancin su, musamman ta hanyar ma’aikatar da take shugabanta.

Ta jaddada cewa ,akwai bukatar a sanya mata a kasar a cikin batun gudanar da tsare-tsare da kuma daukar matakan bayar da shawara, musamman duba da fahimtar al’amuran yau da kullum da su ke da shi, a bangaren gudanar da shugabanci da kuma shuganci, a bangaren tafiyar da tattalin arzikin kasar.

Ita kuwa a na ta jawabin tsohuwar ministar ta ilimi ta bayyana cewa, shigen da ke dakile matan’yan kasuwa na kasar nan na haifar da gagarumin cikas wajen bayar da gudunmawar su, a fagen kara bunkasa fannonin tattalin arzikin kasar

Ta buga misali kan hujjar yadda a kasashen duniya, ake samarwa da mata ‘yan kasuwa, kudaden da suke ci gaba da habaka sana’oin su,wanda hakan, ke kara habaka fannin tattalin arzikin kasashen.

A cewar tsohuwar ministan magance wannan matsalar, ba wai kawai ta tallawa sana’oin su aka yi ba, har da kuma kara karfafa fannin tattalin arzikin kasar da kuma bayar da damar, gudanar da yin gasa, a fannin kasuwanin kasar.

“Akwai bukatar a kawar da wannan shingen da janyo mata ‘ yan kasuwa na kasar samun kudaden da za su bunkasa kasuwancin su, inda hakan zai ba su damar kara fadada kasuwancin su.

Ta buga misali da fannin aikin noma wanda ta bayyana cewa, muna gsni kaso 30 a cikin dari matan da suka rungumi fannin na bayar da gagarumar gudunmawa,” .Inji tsohuwar ministan.

Ta alakanta wannan matsalar ta gibin na ssmun kudaden ga matan’yan kasuwa, a matsayin babban abin da ke taka masu birki a fagen kasuwancin su.

Ta yi gargadi da cewa, ci gaba da barin wannan gibin, za a ci gaba da dakile matan ‘yan kasuwa na kasar daga bayar da ta su gudunmawar wajen ciyar da tattalin arzikin kasar gaba.

Ta kuma bayar da shawarar da a yi hadaka a tsakanin masana’antu masu zaman kansu da kuma masu kirkiro da dokoki a kasar domin a janyo matan kasar ‘yan kasuwa domin a rinka tattaunawa da su a fannin tattalin arzikin kasar.

Musawa
Abubakar Abba
+ posts Bio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Tun Ina Karama Marigayi Tumbuleke Ke Sa Ni Dariya —Hannatu Musawa
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    NPA Ta Bayyana Cewa Kirkiro Da Sabuwar Hukumar NPERA Ba Zai Zame Mata Tarnaki Ba
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Yadda Bikin Girke-girke Ya Karfafa Alaka Tsakanin Musulmai Da Kiristoci A Kaduna
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Nazari Kan Wasu Dalilan Da Ke Haddasa Sabanin Abotakar Jarumi Ko Jaruma A Kannywood
Musawa
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
  • Sulaiman
    Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana
  • Sulaiman
    ‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna
  • Sulaiman
    Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

MASU ALAKA

'Yan Bindiga
Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina
Labarai

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare
Labarai

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Next Post
Rikicin ADC: Lauya Ya Caccaki Kotun Ɗaukaka Ƙara

Rikicin ADC: Lauya Ya Caccaki Kotun Ɗaukaka Ƙara

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.