ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Matakan Dakile Annobar Ambaliyar Ruwa (Ra’ayinmu)

by Sulaiman
4 years ago
Ambaliyar ruwa

Nijeriya, kamar dai sauran wasu kasashen Afrika dama duniya gaba daya na fuskantar barnar da matsananciyar ambaliyar ruwa da ta haifar ta asarar rayuka da dimbin dukiyar miliyoyin Nairori.

Abubuwan da suka hada da ruwa kamar da bakin kwarya da matsalolin da suka shafi dumamar yanayi wanda gwamnati ta kasa daukar matakin da ya kamata don dakilewa ya sanya duk kokarin da ake yi na shawo kan ambaliyar ya ci tura.

  • Wike Ya Amince Da Kashe Biliyan 1 Don Taimakon Wadanda Ambaliyar Ruwa Ta Shafa

A kan haka a duk shekara barnar da ambaliyar ke haifarwa yake kara munana. Abin takaicin kuma a nan shi ne yadda gwamnati bata mayar da hankali ga matakan dakile yawaitar ambaliyar da irin barnar da take haifarwa ba a duk shekara. Ya zuwa watan Satumba ambaliyar ta yi sanadiyyar asarar rayuka da dukiyoyin al’umma da amna duk kuwa da gargadin da aka yi aukuwar lamarin.

ADVERTISEMENT

A ranar 19 ga watan Satumba, Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa (NEMA) ta yi gargadin yiyuwar ambaliya daga Tafkin Kogin Neja da Benuwa zuwa wasu jihohi 14 a fadin tarayyar Nijeriya.

Hukumar NEMA ta bayar da gargadin ne tare da hadin gwiwar Hukumar Hasashen Yanayi ta Kasa inda ta bayyana yiyuwar gaggarumin ambaliyar ruwa a jihohin Adamawa, Taraba, Benuwai, Neja, Nasarawa, Kebbi, Kogi, Neja, Delta, Edo, Delta, Anambra, Cross Riber, Ribers da kuma Jihar Bayelsa.

LABARAI MASU NASABA

Karuwar Farin Jinin Gwamna Umaru Bago A Siyasar Jihar Neja

Kyakkyawan Tsarin Laken Asiri Zai Dakile Shirin Magudin Zabe A Nijeriya —Mohammed

A taron da ya yi da manema labarai, Shugababn Hukumar NEMA, Mustapha Habib Ahmed, ya bukaci gwamnatin wadannan jihohin su gaggauta tayar da al’ummar da ke a yankuna da suka fi fuskantar hatsari ambaliyar zuwa yankunan da bashi da matsala don kaucewa asarar rayuka da dukiya.

Ya bayar da bayanin irin tsananin da lamarin za iya yi, yana mai cewa, masu kula da babban dam din nan na kasar Kamaru mai suna Lagdo dam sun fara sake ruwa tun daga ranar 14 ga watan Satumba 2022.
“Muna sane da an fara sake ruwa daga wannan Dam zuwa yankuna Nijeriya ta kogin Benuwai wanda hakan zai kai ga samuwar ambaliyar ruwa a garuruwa da dama tare da haifar da barna mai yawa.

“Wannan ruwa da aka sako zai kara ta’azzara matsalar da ake fusksanta a wasu Dam-dama na Nijeriya kamar na Kainji, Jebba da Shiroro wadanda suma ana sa ran za su yi ambaliya, kamar dai yadda hukumar kula da yanayi ta yi hasashe.”
Ganin muhimmanci da girman matsalar da ake fuskanta sai ya yi kira ga dukkan masu ruwa da tsaki su gaggauta daukar matakin da ya kamata na kawar da al’ummar yankunan da ambaliyar zai fii shafa da gaggawa.

Ba wai ba a taba ganin irin wannan lamarin ba ne amma dai ba a taba ganin irin yadda lamarin ya gawurta ba kamar a wannan lokacin. Bayani ya nuna cewa, mutum 805 suka mutu a sassan Nijeriya a shekarar 2017 da 2022, kamar yadda bayanai daga hukumar Bayar da Agajinn Gaggawa ya nuna da kuma kafar Floodlist kafar da ke bayar da bayanai na labaran da suka shafi ambaliyar ruwa a sassan duniya.

Zuwa yanzu ambaliyar ta tarwatsa mazauna 1,290,455 kamar yadda bayanai ya nuna, hukumar NEMA ta kuma sanar da cewa, mutum 372 ne suka mutu sakamakon ambaliyar a shekarar 2022, yayin ambaliyar ta shafi mutum fiye da 508,000 yayin da mutum 277 suka ji munanan raunuka a cikin wata 8 da suka wuce.

Tabbas wannan na kara nuna irin girmar mastalar da ake fuskanta ne, ya bayyana lamarin inda yake cewa, duniya na fuskantar babbar matsala, matsala daga abubuwan da suka shafi dumamar yanayi. Watakila in har abubuwan da suka faru a cikin watannin uku basu isa su gamsar da mutum akan irin matsalar da duniya ke ciki ba to lallai babu wani abin da ya isa ya gamsar da shi game al’amarin dumamar yanayi.

Tun daga ambaliyar da ta taso daga kasar Pakistan da ambaliyar nan mai tayar da hankali ta ‘Ian’ data ratsa Florida zuwa Carolina ta Yamma a kasar Amurka a bayyana yake cewa lallai abubuwa ba kamar yadda suke ba ne a da a halin yanzu.

Lamarin bai bar yankin Turai ba suma sun dandana barnar ambaliyar tun daga Landan har zuwa Spaniya duk sun fuskanci barnar ambaliyar a cikin wannan shekara haka ma a yankin nahiyar Asia inda kasar Chana ta fusknaci matsananciyar yanayi irn wanda basu taba fuskanta ba a a tsawon shekaru masu yawa.

A tsawon shekaru, hujjoji na cutar da muhalli sun bayyana a Ni.

Ambaliyar ruwa
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Na Sayar Da ’Ya’yana, Na Sace Wasu 19 – Wata Da Ake Zargi Da Safarar Yara
  • Sulaiman
    Hormuz: Iran Ta Kai Muggan Hare-hare Kan Sansanin Amurka A Jordan
  • Sulaiman
    ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto
  • Sulaiman
    PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

MASU ALAKA

Gwamnatin Neja Ta Bayar Da Umarnin Kawo Karshen Matsalar Tsaro
Rahotonni

Karuwar Farin Jinin Gwamna Umaru Bago A Siyasar Jihar Neja

September 5, 2026
Kyakkyawan Tsarin Laken Asiri Zai Dakile Shirin Magudin Zabe A Nijeriya —Mohammed
Rahotonni

Kyakkyawan Tsarin Laken Asiri Zai Dakile Shirin Magudin Zabe A Nijeriya —Mohammed

September 5, 2026
Jihar Katsina Da UNICEF Sun Ceto Rayuwar Yara Ta Hanyar Samar Da Abinci Mai Gina Jiki
Rahotonni

Jihar Katsina Da UNICEF Sun Ceto Rayuwar Yara Ta Hanyar Samar Da Abinci Mai Gina Jiki

September 5, 2026
Next Post
Zagayen Maulidin Annabi (SAW) Ya Gudana Cikin Armashi A Bauchi

Zagayen Maulidin Annabi (SAW) Ya Gudana Cikin Armashi A Bauchi

LABARAI MASU NASABA

Yadda Jami’an ‘Yansanda Suka Yi Garkuwa Da Wani Mazaunin Abuja, Sun Kwashe Fiye Da Naira Miliyan 20 A Asusunsa

Na Sayar Da ’Ya’yana, Na Sace Wasu 19 – Wata Da Ake Zargi Da Safarar Yara

September 9, 2026
Iran Ta Musanta Ikirarin Trump Tare Da Zafafa Hare-hare Kan Isra’ila

Hormuz: Iran Ta Kai Muggan Hare-hare Kan Sansanin Amurka A Jordan

September 9, 2026
ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

September 9, 2026
Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.