Gandun dazukan ƙasar nan, na buƙatar a samar masu da ɗaukin gaggawa, na kula da su, yadda ya kamata
Misali, gidauniyar da ke kula da gandun daji ta ƙasa, wato NCF ta yi gargaɗin cewa, Nijeriya ta yi asarar aƙalla kaso 90 na gangun dazukan da ke a ƙasar, a cikin ƙarni uku kacal, da suka wuce
Wannan asarar, ta sanya an rasa ƙasa da kaso 10 na faɗin ƙasar da ake da shi, a gandun dazukan ƙasar.
Kazalika, wannan adadin, ya nuna yadda ake ci gaba da samun, ƙaruwar sare Bishiyoyin, da ke a cikin dazukan ƙasar, wanda ya haura, na adadin duniya.
- Wata Ƙungiya Ta Mara Wa Ganduje Baya Don Zama Daraktan Kamfen Ɗin Tinubu A 2027
- Gwamnan Sakkwato Ya Nada Manyann Mukaman Gwamnati A Jihar
A ɓangare ɗaya, batun ƙalubalen rashin tsaro, hauwan farashin kaya da rashin nuna damuwa, daga gun masu riƙe da madafun iko na siyasa a ƙasar, na ci gaba da zama barazana, ga gandun dazukan ƙasar.
Ana ci gaba da samun ƙaruwar sare Bishiyoyi, a dazukan, ta haramtacciyar hanya, saboda buƙatar da ake da ita, ta Gawayi da kuma Katakon, da ake fasaƙwarinsa, zuwa kasuwannin duniya.
Bugu da ƙari, biyo bayan ci gaba da samun yawan alumma a ƙasar, hakan ya sanya, ana ci gaba da buƙatar Itacen yin girki da kuma sauran buƙatar da ake da ita, ta Itacen.
Bisa wasu alƙaluma da ƙungiyar ƙasa da ƙasa da ke sanya ido kan gandun daji wato Global Forest Watch, ta sanar da cewa, a tsakain 2001 zuwa 2024, Nijeriya ta yi asarar hecktar da ta kai miliyan 1.4, tare da kuma wasu hekta aƙalla dubu 250, 000 da suka ɓace, a 2024.
Hakazalika, hukumar ta NCF, ta ƙiyasta cewa, a duk shekara, Nijeriya na yin asarar hekta 400,000 da ke a cikin gandun dazukan ƙasar.
Wannan matsalar na ƙara janyo sare Bishiyoyi, da ke gandun dazukan ƙasar, musamman a yankin Sahele, na Arewaci ƙasar da kuma ci gaba da samun aukuwar ambaliyar ruwan sama a kudancin Sahel.
Kazalika, matsalar na kuma janyo zaizayar ƙasa da samun raguwar ruwa, musamman a Kainji da Shiroro, inda hakan ke haiyar da ambaliyar ruwan da ke kwararowa, zuwa cikin birane.
Misali, a johohin da ke a cikin Sahel, kamar irinsu, Borno, Yobe, Jigawa, Bauchi da Katsina, matsalar sare Bishiyoyi, na shafar ƙasar noma da ƙara aukuwar ambaliyar ruwa tare da kuma ƙara haddasa, talauci, ga mazauna karkara.
Akasarin alumomin da ke a Arewa da wanda suke a yankin Tsakiyar Nijeriya, wato Middle Belt, sun jima, suna dogaro da albarkatun da suke samu, daga cikin gandun zazukan ƙasar, inda suke samun saiwoyin Itace, da suke sarrafa sum zuwa magunguna da yin farauta da sauransu.
Sai dai, ɓacewar waɗannan kadarorin, na ci gaba da tarwatsa iyalansu da kuma gaba da aukuwar rikice-rikice.
Misali, matsalar rikice-rikice, a tsakanin Fulani makiyaya da manoma, tuni, ta ƙara ta’azzara, ƙalubalen rashin tsaro, wanda hakan ya haifar da ɓacewar Burtali, da dabbobin Fulanin ke yin kiwo a kansu.
Wannan, na ƙara haifar da matsalar yin balagoron mazuna karkara, zuwa cikin birane, tare da kuma haifar da rashin aikin yi. Inda hakan kuma ke sanya, ƴan ta’adda, yin hayar matasa, domin gudanar da ayyukan ta’adanci
Waɗannan matsalolin, sun nuna a zahiri, na rashin iya gudanar da shugabanci, a tsakanin ƴan siyasa, masu riƙe da madafun iko.
Kundin tsarin mulkin ƙasar na 1999 da aka sabunta, ya ɗorawa gwamnonin jihohin ƙasar, nauyin kare rayuka da dukiyoyin ƴan ƙasar
Duk da tsare-tsaren ƙasa da aka samar domin kare gandun dazukan ƙasar, amma abin takaici, tun daga matakin jihohi har zuwa na tarayya, babu wani ƙoƙari da suka yi, na bayar da kariyar.
Ƙwararu a fannin kare muhalli a ƙasar, na ci gaba da bayar da shawarar ɗaukar matakan da suka kamata, domin a bai wa gandun dazukan ƙasar, kariyar da ta kamata.
Kazalika, akwai kuma buƙatar tun a matakin jiha, da na tarayya, a tabbatar da sun ɗauki matakin gaggauawa, musaman domin a magance, sare Bishiyoyin da ke a cikin gandun dazaukan ƙasar.
Ya kuma zama wajbi, a yi koyi da irin salon yin gangami na ƙasar Ethiopia, na kare gandun dazuka tare da kuma bai wa alumomin ragamar ci gaba da bai wa gandun dazukan kulawar da ta kamata.
Kazalika, akwai buƙatar a samar da Jirage, marsa matuƙa, da za su rinƙa bayar da tsaro, a gandun dazukan ƙasar da kuma tura dakarun kula da gandun dazukan ƙasar, musamman domin yaƙar, masu sarar Bishiyoyi, ta haramtacciyar hanya.
Bugu da ƙari, ya kamata a tanadi hunkunci mai tsauri, kamar dai yanke hukuncin zama gidan yari, ga masu sarar Bishishiyin da ke a gandun dazukan ƙasar ƙasar.
Ya waja, a samar da wani tsari, na yin amfani da makamashi, wanda hakan zai daƙile yawan sarar Bishiyoyin domin samar da Gwayin yin girki.
Matuƙar gandun dazukan ƙasar nan suna ɓace ɓata, Nijeriya za ta yi asarar ba wai ruwa ba kawai, har da ma, gaza samar da wadataccen abinci, inda kuma kwararowar mazauna karkara da aukuwar rikice-rikice za su ƙara ƙaruwa, a ƙasar.















Discussion about this post