ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, July 17, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Matsalar Tsaro: Yadda Tinubu Ya Dauki Matakin Dakile Tasirin Nuhu Ribadu

by Sani Anwar
2 months ago
Tinubu

Nadin Adeyinka Famadewa, Manjo-Janar mai ritaya, a matsayin mai ba da shawara na musamman kan harkokin tsaron cikin gida, ya haifar da cece-kuce kan wani sabon salo na tsarin tsaro na Nijeriya, karkashin Gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu.

Tinubu, wanda a halin yanzu yana wajen kasar, ya sanar da nadin ne ta wata takardar sanarwa a ranar Litinin, mai dauke da sa hannun sakataren gwamnatin tarayya, George Akume, wadda kuma babban sakatare na ofishin kula da ayyuka Ibrahim Kana ya bayar.

A cewar Akume, nadin ya kara jaddada kudirin gwamnatin Tinubu, na karfafa hadin kan tsaro a cikin gida da inganta ayyukan sirri da zurfafa hadin gwiwar hukumomin tsaro, wajen magance matsalolin na tsaro da suka kunno kai a fadin kasar nan.

ADVERTISEMENT

Daily trust ta ruwaito cewa, a ‘yan kwanakin nan, Nijeriya ta fuskanci kalubalen tsaro, inda sojoji da ‘yansanda da sauran jami’an tsaro, suka suka fuskanci babban kalubale daga ‘yan ta’adda tare kuma da kona na’urorin tsaro na zamani.

Yayin da wasu ‘yan Nijeriya ke ganin cewa, matakin da shugaban kasar ya dauka na kan hanya mai kyau, wasu kuma na ganin cewa; nadin na da nasaba da siyasa, kuma zai iya zama wani yunkuri na rage wa mai bai wa shugaban kasa shawara kan harkokin tsaro, Nuhu Ribadu, karfin iko.

LABARAI MASU NASABA

Zaben Fidda Gwani Da Ake Takaddama:APC Ta Dauki Matakan Kauce Wa Shari’o’in Kotu

Sake Daukar Shettima Da Tinubu Ya Yi Zai Kara Karfafa APC A Zaben 2027 –Farfesa Yerima

Manyan Janar guda biyu da suka yi ritaya, sun ba da ra’ayoyi daban-daban kan dalilin da ya sa Shugaba Tinubu ya kirkiro ofishin mai ba da shawara na musamman kan harkokin tsaron cikin gida.

“Bana tunanin zai tsige Ribadu, na yi imani yana kokarin tabbatar da kafa ‘yansandan jiha ne, zai yi amfani da shi (sabon mai ba shi shawara) da Sufeto-Janar na ‘yan sanda (IGP), wajen kafa ‘yansandan,” daya daga cikin Janar din ya shaida wa Daily trust.

Wani Janar ya ce, “Ba zai sallami Ribadu da wuri ba, domin shi ne ke tsara tsare-tsaren hukumar leken asiri ta kasa, shi kuma Janar din zai kula da tsaron cikin gida.

“Duk da haka, idan aka yi la’akari da siyasar kabilanci da ake gani tun lokacin da gwamnati mai ci ta hau mulki, ba zan yi mamaki ba idan Ribadu ya koma gefe, watakila a kan kuri’un Arewa-maso-gabas, yana iya barin sa, duk da haka, kada wani ya gaya min cewa; wannan nadin an yi shi ne bisa cancanta, wace cancanta?”

Wani masani kan harkokin tsaro, wanda ba ya so a bayyana sunansa, ya ce; za a iya samun matsala.

A cewarsa, “Akwai ayyuka masu alaka da juna, babu shakka game da hakan. A Amurka, an raba su gida biyu, NSA mai ba da shawara ne, sannan kuma Sakataren Tsaron Cikin Gida, daidai yake da minista.

“Amma a ce Ribadu da wannan mutumin duk masu ba da shawara ne, hakika wannan wani abu ne daban. Watakila Ribadu ba zai sake jin dadin amincewa da Tinubu ba,” in ji shi. Majiyar ta ce, ra’ayin bai goyi bayan Ribadu ba.

“A haka ne sannu a hankali, Tinubu ya bata wa Wale Edun rai, har sai da ya fita (Edun), na farko, duk wani muhimmin aiki da Edun ya kamata ya yi, an karbe an bai wa wani karamin minista daban ya yi.

Tinubu
Sani Anwar
+ postsBio
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Sake Daukar Shettima Da Tinubu Ya Yi Zai Kara Karfafa APC A Zaben 2027 –Farfesa Yerima
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Shugaban Rundunar Sojojin Nijeriya Ya Nemi Haɗin Kan Fararen Hula
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Ƴan Ƙwadago Sun Buƙaci Naira 300,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    NiMet Ta Gargaɗi Jihohi 27 Kan Barazanar Ambaliyar Ruwa A Farkon Watan Yuli

MASU ALAKA

Zaben Fidda Gwani Da Ake Takaddama:APC Ta Dauki Matakan Kauce Wa Shari’o’in Kotu
Rahotonni

Zaben Fidda Gwani Da Ake Takaddama:APC Ta Dauki Matakan Kauce Wa Shari’o’in Kotu

July 17, 2026
Sake Daukar Shettima Da Tinubu Ya Yi Zai Kara Karfafa APC A Zaben 2027 –Farfesa Yerima
Labarai

Sake Daukar Shettima Da Tinubu Ya Yi Zai Kara Karfafa APC A Zaben 2027 –Farfesa Yerima

July 17, 2026
Gasar Kofin Duniya: Da Ƙarfinmu Muka Kawo Matakin Da Muke Yanzu – Messi
Manyan Labarai

Gasar Kofin Duniya: Da Ƙarfinmu Muka Kawo Matakin Da Muke Yanzu – Messi

July 17, 2026
Next Post
Zan Bai Wa Al’ummar Filato Fifiko – Mai Neman Takarar Gwamna A PDP

Zan Bai Wa Al’ummar Filato Fifiko - Mai Neman Takarar Gwamna A PDP

LABARAI MASU NASABA

Xi Ya Gana Da Babban Sakataren MDD Da Firaministocin Thailand Da CambodiaA

Xi Ya Gana Da Babban Sakataren MDD Da Firaministocin Thailand Da CambodiaA

July 17, 2026
Zaben Fidda Gwani Da Ake Takaddama:APC Ta Dauki Matakan Kauce Wa Shari’o’in Kotu

Zaben Fidda Gwani Da Ake Takaddama:APC Ta Dauki Matakan Kauce Wa Shari’o’in Kotu

July 17, 2026
Sin Ta Mika Sabuwar Manhajar Gargadin Gaggawa Ta MAZU Ga Djibouti

Sin Ta Mika Sabuwar Manhajar Gargadin Gaggawa Ta MAZU Ga Djibouti

July 17, 2026
Sake Daukar Shettima Da Tinubu Ya Yi Zai Kara Karfafa APC A Zaben 2027 –Farfesa Yerima

Sake Daukar Shettima Da Tinubu Ya Yi Zai Kara Karfafa APC A Zaben 2027 –Farfesa Yerima

July 17, 2026
Kwamitin Ba Da Shawara Kan Hadin Gwiwar Kasa Da Kasa Na Dandalin BRI Ya Yi Taronsa Na 2026

Kwamitin Ba Da Shawara Kan Hadin Gwiwar Kasa Da Kasa Na Dandalin BRI Ya Yi Taronsa Na 2026

July 17, 2026
Wang Huning Ya Ziyarci Koriya Ta Arewa

Wang Huning Ya Ziyarci Koriya Ta Arewa

July 17, 2026
Yawan Mu’amalar Kudi Tsakanin Mazauna Sin Da ’Yan Kasashen Waje Ya Hau Wani Sabon Matsayi A Tarihi

Yawan Mu’amalar Kudi Tsakanin Mazauna Sin Da ’Yan Kasashen Waje Ya Hau Wani Sabon Matsayi A Tarihi

July 17, 2026
Gasar Kofin Duniya: Da Ƙarfinmu Muka Kawo Matakin Da Muke Yanzu – Messi

Gasar Kofin Duniya: Da Ƙarfinmu Muka Kawo Matakin Da Muke Yanzu – Messi

July 17, 2026
Matatar Man Dangote Ta Dawo Sayar Da Fetur A Dala

Matatar Man Dangote Ta Dawo Sayar Da Fetur A Dala

July 17, 2026
Xi Jinping Ya Halarci Bikin Bude Babban Taron AI Na Duniya Na 2026 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Xi Jinping Ya Halarci Bikin Bude Babban Taron AI Na Duniya Na 2026 Tare Da Gabatar Da Jawabi

July 17, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.