ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 27, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Matsalar Tsaro: Yadda Tinubu Ya Dauki Matakin Dakile Tasirin Nuhu Ribadu

by Sani Anwar
1 month ago
Tinubu

Nadin Adeyinka Famadewa, Manjo-Janar mai ritaya, a matsayin mai ba da shawara na musamman kan harkokin tsaron cikin gida, ya haifar da cece-kuce kan wani sabon salo na tsarin tsaro na Nijeriya, karkashin Gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu.

Tinubu, wanda a halin yanzu yana wajen kasar, ya sanar da nadin ne ta wata takardar sanarwa a ranar Litinin, mai dauke da sa hannun sakataren gwamnatin tarayya, George Akume, wadda kuma babban sakatare na ofishin kula da ayyuka Ibrahim Kana ya bayar.

A cewar Akume, nadin ya kara jaddada kudirin gwamnatin Tinubu, na karfafa hadin kan tsaro a cikin gida da inganta ayyukan sirri da zurfafa hadin gwiwar hukumomin tsaro, wajen magance matsalolin na tsaro da suka kunno kai a fadin kasar nan.

ADVERTISEMENT

Daily trust ta ruwaito cewa, a ‘yan kwanakin nan, Nijeriya ta fuskanci kalubalen tsaro, inda sojoji da ‘yansanda da sauran jami’an tsaro, suka suka fuskanci babban kalubale daga ‘yan ta’adda tare kuma da kona na’urorin tsaro na zamani.

Yayin da wasu ‘yan Nijeriya ke ganin cewa, matakin da shugaban kasar ya dauka na kan hanya mai kyau, wasu kuma na ganin cewa; nadin na da nasaba da siyasa, kuma zai iya zama wani yunkuri na rage wa mai bai wa shugaban kasa shawara kan harkokin tsaro, Nuhu Ribadu, karfin iko.

LABARAI MASU NASABA

ADC Ta Yi Allah-Wadai Da Soke Rajistar NDC, Ta Yi Gargaɗi Kan Barazanar Dimokuraɗiyya

TCN Ta Sanar Da Ɗaukewar Wutar Lantarki A Kano Da Wasu Jihohi Huɗu

Manyan Janar guda biyu da suka yi ritaya, sun ba da ra’ayoyi daban-daban kan dalilin da ya sa Shugaba Tinubu ya kirkiro ofishin mai ba da shawara na musamman kan harkokin tsaron cikin gida.

“Bana tunanin zai tsige Ribadu, na yi imani yana kokarin tabbatar da kafa ‘yansandan jiha ne, zai yi amfani da shi (sabon mai ba shi shawara) da Sufeto-Janar na ‘yan sanda (IGP), wajen kafa ‘yansandan,” daya daga cikin Janar din ya shaida wa Daily trust.

Wani Janar ya ce, “Ba zai sallami Ribadu da wuri ba, domin shi ne ke tsara tsare-tsaren hukumar leken asiri ta kasa, shi kuma Janar din zai kula da tsaron cikin gida.

“Duk da haka, idan aka yi la’akari da siyasar kabilanci da ake gani tun lokacin da gwamnati mai ci ta hau mulki, ba zan yi mamaki ba idan Ribadu ya koma gefe, watakila a kan kuri’un Arewa-maso-gabas, yana iya barin sa, duk da haka, kada wani ya gaya min cewa; wannan nadin an yi shi ne bisa cancanta, wace cancanta?”

Wani masani kan harkokin tsaro, wanda ba ya so a bayyana sunansa, ya ce; za a iya samun matsala.

A cewarsa, “Akwai ayyuka masu alaka da juna, babu shakka game da hakan. A Amurka, an raba su gida biyu, NSA mai ba da shawara ne, sannan kuma Sakataren Tsaron Cikin Gida, daidai yake da minista.

“Amma a ce Ribadu da wannan mutumin duk masu ba da shawara ne, hakika wannan wani abu ne daban. Watakila Ribadu ba zai sake jin dadin amincewa da Tinubu ba,” in ji shi. Majiyar ta ce, ra’ayin bai goyi bayan Ribadu ba.

“A haka ne sannu a hankali, Tinubu ya bata wa Wale Edun rai, har sai da ya fita (Edun), na farko, duk wani muhimmin aiki da Edun ya kamata ya yi, an karbe an bai wa wani karamin minista daban ya yi.

Tinubu
Sani Anwar
+ postsBio
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Tattalin Arziƙin Ƙasa: Masana Sun Buƙaci Tinubu Ya Yi Hattara Da Shawarar IMF
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (2)
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (1)
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

MASU ALAKA

ADC Ta Yi Allah-Wadai Da Soke Rajistar NDC, Ta Yi Gargaɗi Kan Barazanar Dimokuraɗiyya
Labarai

ADC Ta Yi Allah-Wadai Da Soke Rajistar NDC, Ta Yi Gargaɗi Kan Barazanar Dimokuraɗiyya

June 27, 2026
TCN Ta Sanar Da Ɗaukewar Wutar Lantarki A Kano Da Wasu Jihohi Huɗu
Manyan Labarai

TCN Ta Sanar Da Ɗaukewar Wutar Lantarki A Kano Da Wasu Jihohi Huɗu

June 27, 2026
Magoya Bayan Pantami Sun Zargi Ana Musgunawa Gombawa Motors A Gombe
Labarai

Magoya Bayan Pantami Sun Zargi Ana Musgunawa Gombawa Motors A Gombe

June 27, 2026
Next Post
Zan Bai Wa Al’ummar Filato Fifiko – Mai Neman Takarar Gwamna A PDP

Zan Bai Wa Al’ummar Filato Fifiko - Mai Neman Takarar Gwamna A PDP

LABARAI MASU NASABA

Zaben 2027: Jam’iyyun Siyasa Sun Bayyana Shirinsu Yayin Da INEC Ta Fitar Da Jawalin Zabe

2027: Jam’iyyun Siyasa Sun Yi Maraba Da Hukuncin Kotu Kan Dakatar Da Jadawalin INEC

June 27, 2026
ADC Ta Yi Allah-Wadai Da Soke Rajistar NDC, Ta Yi Gargaɗi Kan Barazanar Dimokuraɗiyya

ADC Ta Yi Allah-Wadai Da Soke Rajistar NDC, Ta Yi Gargaɗi Kan Barazanar Dimokuraɗiyya

June 27, 2026
TCN Ta Sanar Da Ɗaukewar Wutar Lantarki A Kano Da Wasu Jihohi Huɗu

TCN Ta Sanar Da Ɗaukewar Wutar Lantarki A Kano Da Wasu Jihohi Huɗu

June 27, 2026
Magoya Bayan Pantami Sun Zargi Ana Musgunawa Gombawa Motors A Gombe

Magoya Bayan Pantami Sun Zargi Ana Musgunawa Gombawa Motors A Gombe

June 27, 2026
Babu Wani Saɓani Tsakanin Osimhen Da Lookman – Ndidi

Babu Wani Saɓani Tsakanin Osimhen Da Lookman – Ndidi

June 27, 2026
Gasar Kofin Duniya: Senegal Ta Kai Zagaye Na 32 Bayan Lallasa Iraki Da Ci 5-0

Gasar Kofin Duniya: Senegal Ta Kai Zagaye Na 32 Bayan Lallasa Iraki Da Ci 5-0

June 27, 2026
Tinubu Ya Sanya Hannu Kan Sabuwar Dokar Shaidar Ɗan Ƙasa, Duba Abin Da Ta Ƙunsa

Tinubu Ya Sanya Hannu Kan Sabuwar Dokar Shaidar Ɗan Ƙasa, Duba Abin Da Ta Ƙunsa

June 27, 2026
Tinubu

Nasiha Ga Uwargida Kan Zafin Kishi (1)

June 27, 2026
Yadda Jami’an ‘Yansanda Suka Yi Garkuwa Da Wani Mazaunin Abuja, Sun Kwashe Fiye Da Naira Miliyan 20 A Asusunsa

An Kama Uwa Da Abokiyar Burminta Kan Kisan Jariri A Jihar Yobe

June 27, 2026
Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

Gwamnatin Tarayya Ta Raba Wa Manoma 2,930 Buhun Taki 11,720 A Abuja

June 27, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.