ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, June 7, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Matsalar Tsaro: Yadda Tinubu Ya Dauki Matakin Dakile Tasirin Nuhu Ribadu

by Sani Anwar
3 weeks ago
Tinubu

Nadin Adeyinka Famadewa, Manjo-Janar mai ritaya, a matsayin mai ba da shawara na musamman kan harkokin tsaron cikin gida, ya haifar da cece-kuce kan wani sabon salo na tsarin tsaro na Nijeriya, karkashin Gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu.

Tinubu, wanda a halin yanzu yana wajen kasar, ya sanar da nadin ne ta wata takardar sanarwa a ranar Litinin, mai dauke da sa hannun sakataren gwamnatin tarayya, George Akume, wadda kuma babban sakatare na ofishin kula da ayyuka Ibrahim Kana ya bayar.

A cewar Akume, nadin ya kara jaddada kudirin gwamnatin Tinubu, na karfafa hadin kan tsaro a cikin gida da inganta ayyukan sirri da zurfafa hadin gwiwar hukumomin tsaro, wajen magance matsalolin na tsaro da suka kunno kai a fadin kasar nan.

ADVERTISEMENT

Daily trust ta ruwaito cewa, a ‘yan kwanakin nan, Nijeriya ta fuskanci kalubalen tsaro, inda sojoji da ‘yansanda da sauran jami’an tsaro, suka suka fuskanci babban kalubale daga ‘yan ta’adda tare kuma da kona na’urorin tsaro na zamani.

Yayin da wasu ‘yan Nijeriya ke ganin cewa, matakin da shugaban kasar ya dauka na kan hanya mai kyau, wasu kuma na ganin cewa; nadin na da nasaba da siyasa, kuma zai iya zama wani yunkuri na rage wa mai bai wa shugaban kasa shawara kan harkokin tsaro, Nuhu Ribadu, karfin iko.

LABARAI MASU NASABA

Matsalar Tsaro Da Tsadar Kayan Noma Na Barazana Ga Samar Da Abinci A Daminar Bana

Ban Sha Wata Wahala Ba A Gwagwarmayar Shiga Harkar Fim —Hadiza

Manyan Janar guda biyu da suka yi ritaya, sun ba da ra’ayoyi daban-daban kan dalilin da ya sa Shugaba Tinubu ya kirkiro ofishin mai ba da shawara na musamman kan harkokin tsaron cikin gida.

“Bana tunanin zai tsige Ribadu, na yi imani yana kokarin tabbatar da kafa ‘yansandan jiha ne, zai yi amfani da shi (sabon mai ba shi shawara) da Sufeto-Janar na ‘yan sanda (IGP), wajen kafa ‘yansandan,” daya daga cikin Janar din ya shaida wa Daily trust.

Wani Janar ya ce, “Ba zai sallami Ribadu da wuri ba, domin shi ne ke tsara tsare-tsaren hukumar leken asiri ta kasa, shi kuma Janar din zai kula da tsaron cikin gida.

“Duk da haka, idan aka yi la’akari da siyasar kabilanci da ake gani tun lokacin da gwamnati mai ci ta hau mulki, ba zan yi mamaki ba idan Ribadu ya koma gefe, watakila a kan kuri’un Arewa-maso-gabas, yana iya barin sa, duk da haka, kada wani ya gaya min cewa; wannan nadin an yi shi ne bisa cancanta, wace cancanta?”

Wani masani kan harkokin tsaro, wanda ba ya so a bayyana sunansa, ya ce; za a iya samun matsala.

A cewarsa, “Akwai ayyuka masu alaka da juna, babu shakka game da hakan. A Amurka, an raba su gida biyu, NSA mai ba da shawara ne, sannan kuma Sakataren Tsaron Cikin Gida, daidai yake da minista.

“Amma a ce Ribadu da wannan mutumin duk masu ba da shawara ne, hakika wannan wani abu ne daban. Watakila Ribadu ba zai sake jin dadin amincewa da Tinubu ba,” in ji shi. Majiyar ta ce, ra’ayin bai goyi bayan Ribadu ba.

“A haka ne sannu a hankali, Tinubu ya bata wa Wale Edun rai, har sai da ya fita (Edun), na farko, duk wani muhimmin aiki da Edun ya kamata ya yi, an karbe an bai wa wani karamin minista daban ya yi.

Tinubu
Sani Anwar
+ postsBio
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Sojoji Sun Ceto Mutum 92 Tare Da Daƙile Harin Ƴan Ta’adda A Borno
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Uzodimma: Babu Dimokraɗiyya Idan Babu Hamayya
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Alamomin Fara Ruɓewar Hannu Bayan Ɗorin Gida
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Ministocin Da Suka Ajiye Muƙamansu Ba Su Samu Tikitin Takara Ba

MASU ALAKA

Matsalar Tsaro Da Tsadar Kayan Noma Na Barazana Ga Samar Da Abinci A Daminar Bana
Rahotonni

Matsalar Tsaro Da Tsadar Kayan Noma Na Barazana Ga Samar Da Abinci A Daminar Bana

June 6, 2026
Ban Sha Wata Wahala Ba A Gwagwarmayar Shiga Harkar Fim —Hadiza
Labarai

Ban Sha Wata Wahala Ba A Gwagwarmayar Shiga Harkar Fim —Hadiza

June 6, 2026
Sanata Wamakko Ya Koka Kan Taɓarɓarewar Sha’anin Tsaro
Manyan Labarai

Sanata Wamakko Ya Koka Kan Taɓarɓarewar Sha’anin Tsaro

June 6, 2026
Next Post
Zan Bai Wa Al’ummar Filato Fifiko – Mai Neman Takarar Gwamna A PDP

Zan Bai Wa Al’ummar Filato Fifiko - Mai Neman Takarar Gwamna A PDP

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Ba Zai Yiwu A Cimma Yarjejeniya Ba Tare Da Sanya Batun Lebanon Ba —Iran

Ba Zai Yiwu A Cimma Yarjejeniya Ba Tare Da Sanya Batun Lebanon Ba —Iran

June 6, 2026
Kasashen Da Darajar Kudadensu Suka Fadi Da Wadanda Nasu Suka Tashi Sanadiyyar Yakin Iran

Kasashen Da Darajar Kudadensu Suka Fadi Da Wadanda Nasu Suka Tashi Sanadiyyar Yakin Iran

June 6, 2026
An Gudanar Da Taron Tattaunawa Mai Taken “Tides And Voices” A Birnin Sanya Na Sin

An Gudanar Da Taron Tattaunawa Mai Taken “Tides And Voices” A Birnin Sanya Na Sin

June 6, 2026
Real Madrid Ce Tafi Kowacce Kungiya Daraja A Duniya

Real Madrid Ce Tafi Kowacce Kungiya Daraja A Duniya

June 6, 2026
Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai A Yankin Arewa Maso Gabashin Sin Ya Zarce 3,000 A Bana

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai A Yankin Arewa Maso Gabashin Sin Ya Zarce 3,000 A Bana

June 6, 2026
Kofin Duniya: Sababbin Dokokin Da FIFA Ta Kawo

Kofin Duniya: Sababbin Dokokin Da FIFA Ta Kawo

June 6, 2026
Kafar CMG Ta Kulla Yerjeniyoyin Hadin Gwiwa Da Hukumomin Kasar Laos

Kafar CMG Ta Kulla Yerjeniyoyin Hadin Gwiwa Da Hukumomin Kasar Laos

June 6, 2026
Rundunar Sojan Kasar Sin Ta Sa Ido Kan Jirgin Ruwan Yakin Kasar Holland Da Ya Tsallake Mashigin Tekun Taiwan

Rundunar Sojan Kasar Sin Ta Sa Ido Kan Jirgin Ruwan Yakin Kasar Holland Da Ya Tsallake Mashigin Tekun Taiwan

June 6, 2026
Sin Tana Adawa Da Karin Takunkumin Da Amurka Ta Sanya Wa Cuba

Sin Tana Adawa Da Karin Takunkumin Da Amurka Ta Sanya Wa Cuba

June 6, 2026
Matsalar Tsaro Da Tsadar Kayan Noma Na Barazana Ga Samar Da Abinci A Daminar Bana

Matsalar Tsaro Da Tsadar Kayan Noma Na Barazana Ga Samar Da Abinci A Daminar Bana

June 6, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.