Nadin Adeyinka Famadewa, Manjo-Janar mai ritaya, a matsayin mai ba da shawara na musamman kan harkokin tsaron cikin gida, ya haifar da cece-kuce kan wani sabon salo na tsarin tsaro na Nijeriya, karkashin Gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu.
Tinubu, wanda a halin yanzu yana wajen kasar, ya sanar da nadin ne ta wata takardar sanarwa a ranar Litinin, mai dauke da sa hannun sakataren gwamnatin tarayya, George Akume, wadda kuma babban sakatare na ofishin kula da ayyuka Ibrahim Kana ya bayar.
A cewar Akume, nadin ya kara jaddada kudirin gwamnatin Tinubu, na karfafa hadin kan tsaro a cikin gida da inganta ayyukan sirri da zurfafa hadin gwiwar hukumomin tsaro, wajen magance matsalolin na tsaro da suka kunno kai a fadin kasar nan.
Daily trust ta ruwaito cewa, a ‘yan kwanakin nan, Nijeriya ta fuskanci kalubalen tsaro, inda sojoji da ‘yansanda da sauran jami’an tsaro, suka suka fuskanci babban kalubale daga ‘yan ta’adda tare kuma da kona na’urorin tsaro na zamani.
Yayin da wasu ‘yan Nijeriya ke ganin cewa, matakin da shugaban kasar ya dauka na kan hanya mai kyau, wasu kuma na ganin cewa; nadin na da nasaba da siyasa, kuma zai iya zama wani yunkuri na rage wa mai bai wa shugaban kasa shawara kan harkokin tsaro, Nuhu Ribadu, karfin iko.
Manyan Janar guda biyu da suka yi ritaya, sun ba da ra’ayoyi daban-daban kan dalilin da ya sa Shugaba Tinubu ya kirkiro ofishin mai ba da shawara na musamman kan harkokin tsaron cikin gida.
“Bana tunanin zai tsige Ribadu, na yi imani yana kokarin tabbatar da kafa ‘yansandan jiha ne, zai yi amfani da shi (sabon mai ba shi shawara) da Sufeto-Janar na ‘yan sanda (IGP), wajen kafa ‘yansandan,” daya daga cikin Janar din ya shaida wa Daily trust.
Wani Janar ya ce, “Ba zai sallami Ribadu da wuri ba, domin shi ne ke tsara tsare-tsaren hukumar leken asiri ta kasa, shi kuma Janar din zai kula da tsaron cikin gida.
“Duk da haka, idan aka yi la’akari da siyasar kabilanci da ake gani tun lokacin da gwamnati mai ci ta hau mulki, ba zan yi mamaki ba idan Ribadu ya koma gefe, watakila a kan kuri’un Arewa-maso-gabas, yana iya barin sa, duk da haka, kada wani ya gaya min cewa; wannan nadin an yi shi ne bisa cancanta, wace cancanta?”
Wani masani kan harkokin tsaro, wanda ba ya so a bayyana sunansa, ya ce; za a iya samun matsala.
A cewarsa, “Akwai ayyuka masu alaka da juna, babu shakka game da hakan. A Amurka, an raba su gida biyu, NSA mai ba da shawara ne, sannan kuma Sakataren Tsaron Cikin Gida, daidai yake da minista.
“Amma a ce Ribadu da wannan mutumin duk masu ba da shawara ne, hakika wannan wani abu ne daban. Watakila Ribadu ba zai sake jin dadin amincewa da Tinubu ba,” in ji shi. Majiyar ta ce, ra’ayin bai goyi bayan Ribadu ba.
“A haka ne sannu a hankali, Tinubu ya bata wa Wale Edun rai, har sai da ya fita (Edun), na farko, duk wani muhimmin aiki da Edun ya kamata ya yi, an karbe an bai wa wani karamin minista daban ya yi.















Discussion about this post