ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, September 10, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mece Ce Matsalar Manchester United?

by Abba Ibrahim Wada
2 years ago
Manchester

Tun bayan komawar Ruben Amorim kungiyar kwallon kafa ta Manchester United yake fuskantar kalubale kala-kala musamman na rashin nasara da kuma labarin fitar ‘yan wasa 11 na farko da za su buga wasan da kungiyar ta doke Manchester City a filin wasa na Ettihad, laifin da aka dora shi a kan ‘yan wasa Alejandro Garnacho da Marcus Rashford da kuma Amad Diallo.

Kawo yanzu Manchester United ta yi rashin nasara a wasanni 10 cikin wasanni 22 da ta buga wanda hakan ya sa take zaune a mataki na 12 a kan teburin gasar duk da cewa tana kokari a gasar cin kofin Europa League amma hakan ba shi yake nuna cewa komai yana tafiya daidai ko yadda ya kamata ba a kungiyar kuma ya nuna yadda gagarumin aiki yake kan kociyan kungiyar.

  • Kasar Sin Ta Harba Sabon Tauraron Dan Adam Na Gwaji A Kan Fasahar Sadarwa
  • ‘Yan Nijeriya Za Su Maka Gwamnati A Kotu Kan Karin Kudin Kiran Waya

Cikin fushi bayan tashi daga wasan da kungiyar tta yi rashin nasara a hannun kungiyar Brighton Albion da ci 3-1 mai koyarwa Ruben Amorim ya ce watakila wannan ce kaka mafi muni a tarihin kungiyar a Premier League kuma hakan ne ya sa United tana ta 13 a teburin gasar ta Ingila da maki 26, kuma ya bayyana cewa nan gaba kungiyar za ta ci gaba da yin rashin nasara.

ADVERTISEMENT

Wane Mummunan Tarihi Kungiyar take kafawa?

Bayan da Brighton ta yi nasara a kan Manchester United a filin wasa na Old Trafford, karo na shida kenan da aka doke kungiyar a gida a wasa na 12 tun bayan 1893/94. United ta kare a karshen teburi, lamarin da ya kai ga ta bar buga gasar ta rukunin farko a lokacin da ake kiranta da sunan Newton Heath.

LABARAI MASU NASABA

Yaya Toure Na Dab Da Kafa Tarihi A Gasar Zakarun Turai

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

A shekarar 1914/1915 aka sauya sunan kungiyar zuwa Manchester United, wadda ta kare a gurbi na 18 a cikin kungiyoyi 20 – da maki 30 a karawa 38 kuma wani rashin kokarin da United ta yi a kakar shi ne lashe wasa tara wato kaso 24 cikin 100, idan ka kwatanta da 32 cikin 100 a kakar nan sannan sau biyar jimilla United tana zuwa fadowa daga buga gasar Firimiya a Ingila, wadda ta yi ta karshe a 1921/22 da maki takwas da kara yin ta karshe a 1930/31 da maki 10.

Manchester United ta taba komawa buga gasar rukunin farko da faduwa daga wasannin a 1935 da kuma 1938 – kaka ta baya-baya ita ce 1973/74 lokacin da ta kare ta 21 daga kungiyoyi 22, har ila yau wannan ce kaka mafi muni a United da take ta 13 a kan teburi tun bayan 1989/90 da take kan irin wannan matakin kuma kungiyar da Amorim ke jan ragama tana da maki 26 daga wasa 22, wato tazarar maki takwas daga rashin kwazo a gasar baya.

Manchester United ta hada maki 34 a 2019/20 a irin wannan lokacin, amma sai ta kara kwazo da ta kare a mataki na uku da maki 66 kuma bayan hada maki 35 daga karawa 22 a bara, United ta kare a mataki na takwas da maki 60 da lashe FA Cup karkashin tsohon kociyan kungiyar da ta kora, wato Erik ten Hag. Haka kuma United ta kare kakar Premier League a mataki na shida karo uku da yin ta bakwai a 2013/2014. Kungiyar kwallon kafa ta Manchester United ta dauki kofin Premier League 13 daga kaka 21 karkashin tsohon kociyan kungiyar wato Sir Aled Ferguson, wannan ce kaka ta 12 rabon ta da lashe babbar gasar firimiya ta Ingila, tun bayan da ya yi ritaya duk da irin makudan kudaden da kungiyar ta kashe a lokutan Erik ten Hag da Dabid Moyes da Jose Mourinho da Luis Ban gaal da Ole Gunner Solkjaer.

Manchester
Abba Ibrahim Wada
Website |  + postsBio
  • Abba Ibrahim Wada
    Yaushe Za A Fara Kofin Zakarun Turai
  • Abba Ibrahim Wada
    Messi Ya Yi Ritaya A Argentina: Da Me Za Mu Iya Tuna Gwarzon Duniyar?
  • Abba Ibrahim Wada
    Su Waye ‘Yan wasan Nijeriya Da Za Su Buga Gasar Firimiyar Ingila Ta Bana?
  • Abba Ibrahim Wada
    Chelsea A Ƙarƙashin Xavi Alonso

MASU ALAKA

Yaya Toure Na Dab Da Kafa Tarihi A Gasar Zakarun Turai
Wasanni

Yaya Toure Na Dab Da Kafa Tarihi A Gasar Zakarun Turai

September 9, 2026
Ballon D'or
Manyan Labarai

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

September 8, 2026
Ƙungiyoyi 5 Da Ke Takarar Gwarzuwar Ƙungiya Ta Bana
Wasanni

Ƙungiyoyi 5 Da Ke Takarar Gwarzuwar Ƙungiya Ta Bana

September 8, 2026
Next Post
Zantawa Da Shugaban Kasar Sri Lanka Anura Kumara Dissanayake

Zantawa Da Shugaban Kasar Sri Lanka Anura Kumara Dissanayake

LABARAI MASU NASABA

Xi Ya Bukaci A Kara Azamar Dakile Aukuwar Muggan Hadurra Sakamakon Aukuwar Gobara A Wani Jirgin Ruwan Dakon Kayayyaki

Xi Ya Bukaci A Kara Azamar Dakile Aukuwar Muggan Hadurra Sakamakon Aukuwar Gobara A Wani Jirgin Ruwan Dakon Kayayyaki

September 10, 2026
Manchester

Jerin Bankuna 32 Da Aka Amince Su Sayar Da Hannun Jarin Matatar Dangote

September 10, 2026
Manchester

Uganda Za Ta Fara Fitar Da Man Fetur Zuwa Ƙasashen Waje

September 10, 2026
Cutar Mashaƙo Ta Ɓarke A Kano, Katsina Da Filato

Mashaƙo: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Sun Kai 27 A Filato

September 10, 2026
An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

Wane Ne Dan Shagamu: Su Wane Ne Suka Kashe Shi A Kano?

September 10, 2026
Al’umma Sun Yaba Wa Sojoji Kan Yaƙar ’Yan Bindiga A Zamfara

Al’umma Sun Yaba Wa Sojoji Kan Yaƙar ’Yan Bindiga A Zamfara

September 10, 2026
Ambaliyar Ruwa Ta Tafi Da Ɗalibai 2 A Abuja Da Abia

Ambaliyar Ruwa Ta Tafi Da Ɗalibai 2 A Abuja Da Abia

September 10, 2026
’Yansanda Sun Kama Wadda Ta Yaɗa Labarin OPay Zai Daina Aiki A Nijeriya

’Yansanda Sun Kama Wadda Ta Yaɗa Labarin OPay Zai Daina Aiki A Nijeriya

September 10, 2026
2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato

2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato

September 10, 2026
Zabe: Gwamnatin Kano Ta Taƙaita Zirga-zirgar Mutane Da Ababen Hawa

Gwamna Yusuf Ya Umarci Jami’an Tsaro Su Gano Waɗanda Suka Kashe Danshagamu

September 10, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.