Lissafin siyasa tare da ƙarfin halin da wasu daga cikin Ministocin Shugaba Bola Tinubu suka yi gabanin zaɓen 2027, ya rikiɗe zuwa wani abu mai kama da caca, domin kuwa ya haifar da sakamako maras daɗi.
Bisa umarnin fadar shugaban ƙasa, wasu ministoci da dama sun yi murabus daga majalisar zartarwa ta tarayya, domin ci gaba da gudanar da zaɓukan fid da gwani na jam’iyyar APC mai mulki.
Sai dai, maimakon samun nasara a takarkarun, da dama daga cikin tsoffin ministocin, sun tsinci kansu a cikin halin ƙaƙa-na-ka-yi, inda suka rasa muƙamansu na majalisar ministoci da kuma burinsu na samun tikitin jam’iyya.
Ya zuwa yanzu dai, biyu ne kaɗai daga cikin biyar da suka sauka daga muƙamansu, suka samu tikitin tsayawa takara a zaɓen fid da gwani.
Wasu kuma sun sha kashi na wulaƙanci, jayayya ko rashin tabbas, kan makomar siyasarsu.
Daga cikin waɗanda suka yi murabus ɗin, akwai tsohon ministan wutar lantarki, Adebayo Adelabu; tsohon ministan sufuri, Saidu Alkali; tsohon ministan harkokin waje, Yusuf Tuggar; tsohuwar ministar kwadago da samar da ayyuka, Nkeiruka Onyejeocha; da kuma tsohon ƙaramin ministan harkokin jin ƙai, Yusuf Sununu.
Yayin da Onyejeocha da Sununu suka yi nasarar samun tikitin jam’iyyar APC a Jihohin Abia da Kebbi, inda cikar burin siyasar sauran ta durƙushe ko kuma ta ci tura.
Adebayo Adelabu
Adelabu ya yi murabus a matsayin Ministan Wutar Lantarki, domin neman tikitin takarar gwamna a APC a Jihar Oyo. Sai dai, tsohon ministan ya sha kaye a hannun Sanata Sarafadeen Alli, a lokacin zaɓen fid da gwani.
Alli ya samu ƙuri’u 578,143, yayin da Adelabu ya samu ƙuri’u 19,193 kacal.
Jim kaɗan bayan ya yi murabus ne, ƴan jarida suka tambaye shi ko ya ji labari yana ta yawo cewa; Shugaba Bola Tinubu na mara wa Alli baya, sai tsohon ministan ya ƙaryata faruwar hakan.
“Duk wanda ya ce, ya yi ganawa da shugaban ƙasa kuma ya amince da shi ko yana goyon bayansa, ƙarya yake yi,” in ji shi.
Tsohon ministan ya ƙara da cewa, ya jinkirta yin murabus daga majalisar ministocin tarayya ne, domin samun ganawa da shugaban ƙasar, inda ya ce; a tattaunawarsu ta gudana a bayan fage, Tinubu ya ƙarfafa masa gwiwar ci gaba da burinsa na tsayawa takarar gwamna.
“Ya ce min, ‘Bayo, lokaci ya yi, ba zan hana ka wannan dogon buri naka ba, ka je ka yi murabus ka fara aiki tuƙuru,” in ji Adelabu.
A cewarsa, “Idan har shugaban ƙasa zai marawa wani baya, to ni ne”.
Bayan rashin samun nasarar da ya yi, Adelabu ya yi watsi da sakamakon, sannan kuma ya yi zargin cewa; an tafka kura-kurai tare da cin zarafi da kuma maguɗi a lokacin zaɓen fid da gwanin.
Sa’idu Ahmed Alkali
Tsohon Ministan Sufuri, ya sauka ne daga muƙaminsa na majalisar ministoci, domin neman tikitin takarar gwamna a Jam’iyyar APC, a Jihar Gombe. Sai dai, matakin ya kasa samar da sakamakon da ake sa ran za a iya samu, inda ya sha kaye a hannun Jamilu Gwamna, wanda ya samu goyon bayan Gwamna Inuwa Yahaya.
Daga baya, Alkali ya kauracewa tsarin, yana mai zargin rashin yin adalci da gaskiya a al’amarin.
Koda-yake, Alkali ya zo na uku ne a zaɓen na fid da gwani, bayan tsohon ministan sadarwa, Farfesa Isa Ali Ibrahim Pantami. Yayin da Pantami ya samu ƙuri’u 12,120 a matsayin wanda ya zo na biyu, Alkali ya samu ƙuri’u 11,612 a matsayin wanda ya zo na uku.
Da yake sanar da sakamakon zaɓen, shugaban kwamitin zaɓen, Sanata Abubakar Danladi, ya bayyana cewa; kwamitin ya samu rubutacciyar sanarwar janyewa daga Pantami da Alkali, sai dai ya ce; an miƙa wasiƙun janyewar ne, bayan da aka fara gudanar da zaɓen, inda ya ce; tuni sunayensu ya bayyana a rijistar zaɓe, don haka, sunayensu na nan rubuce a sakamakon zaɓen.
Yusuf Tuggar
Yayin da wasu ministocin suka jinkirta yin murabus ɗinsu, har ma suka kasa bin umarnin na ranar 31 ga Maris, Ambasada Yusuf Maitama Tuggar, ya bayyana matsayinsa a jajibirin cikar wa’adin, yayin da ya miƙa wa shugaban ƙasa takardar murabus ɗinsa a hukumance ta ofishin sakataren gwamnati, a ranar 30 ga watan Maris, 2026.
“A yau, na miƙa takardar murabus ɗina a hukumance a matsayina na Ministan Harkokin Waje na Nijeriya a ofishin Sakataren Gwamnatin Tarayya, bisa ga umarnin Shugaba Bola Ahmed Tinubu, GCFR, da kuma tanade-tanaden dokar zaɓe,” ya rubuta.
Ya bayyana cewa, wannan lokacin ya kawo ƙarshen wani muhimmin babi na hidimarsa, sannan kuma ya gode wa shugaban ƙasar, “saboda amincewa da damar yin aiki a ƙarƙashin ‘Renewed Hope Agenda’, da kuma bayar da gudummawa ga ciyar da manufofin waje na Nijeriya ta hanyar ‘4D Doctrine’”.
Tuggar, wanda tsohon ɗan majalisar wakilai ne, an zaɓe shi a matsayin wakilin mazaɓar tarayya ta Gamawa a shekarar 2007.
Bayan shekara goma, tsohon shugaban ƙasa Muhammadu Buhari, ya naɗa shi jakadan Nijeriya a ƙasar Jamus. Ya riƙe wannan muƙamin daga 2017 zuwa 2023.
Har ila yau, ya rasa tikitin APC a hannun Mohammed Abubakar, tsohon Gwamnan Jihar Bauchi.
A cewar shugaban kwamitin zaɓen gwamnan APC na Bauchi, AIG John Bassey Abang (rtd), Abubakar ya samu ƙuri’u 57,517, inda ya doke Tuggar wanda ya samu ƙuri’u 26,001.














Discussion about this post