Ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar ADC a zaben 2027, Atiku Abubakar, ya soki gwamnatin shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu, yana mai cewa abin da ya fi bayyana cikin shekaru uku na mulkinsa shi ne yunwa, da talauci da kuma hawayen iyalan yaran da aka sace.
A wata sanarwa da mai taimaka masa kan harkokin sadarwa, Phrank Shaibu, ya fitar, Atiku ya ce alƙawarin “Sabon Fata” da gwamnatin ta yi wa ‘yan Nijeriya ya rikiɗe zuwa tsadar rayuwa, da rashin tsaro, da talauci da rashin kulawa. Ya ce miliyoyin ‘yan ƙasa na fama da hauhawar farashin kayan masarufi, da durƙushewar kasuwanci da raguwar darajar kuɗi.
Tsohon mataimakin shugaban ƙasar ya kuma zargi gwamnatin da fifita farfaganda kan shugabanci, yana mai cewa babu wata alama da ke nuna cewa ɗimbin basussukan da gwamnati ke karɓa sun inganta rayuwar talakawa. Ya ce ‘yan Nijeriya na da hakkin tambayar inda kuɗaɗen da aka aro suka tafi idan har ba a ga gagarumin ci gaba a rayuwar jama’a ba.
Kan batun tsaro, Atiku Abubakar ya ce sace-sacen ɗalibai da hare-haren ‘yan bindiga a sassan ƙasar nan na nuna gazawar gwamnati wajen kare rayuka da dukiyoyi. Ya bayyana cewa babu wata farfaganda da za ta iya boye yunwa ko tsoron da jama’a ke ciki.
Ya kuma yi kira ga ‘yan Nijeriya da su yi amfani da ƙuri’arsu wajen neman canji, yana mai bayyana cewa jam’iyyar ADC za ta gabatar da cikakken tsarin manufofinta nan ba da jimawa ba domin magance matsalolin tattalin arziƙi, da tsaro, da ilimi, da lafiya da samar da ayyukan yi a ƙasar nan.















Discussion about this post