ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Motoci 3 Masu Amfani Da Gas (CNG) Sun Yi Bindiga A Tashar Mota A Kaduna

by Abubakar Sulaiman
5 months ago
Kaduna

Aƙalla motoci uku na alfarma masu amfani da iskar gas (Compressed Natural Gas (CNG), mallakar kamfanin sufuri na Silver Transport, sun ƙone ƙurmus sakamakon wata fashewa da ta auku da asubahin ranar Lahadi a tashar mota ta Kawo da ke jihar Kaduna, lamarin da ya tayar da hankalin jama’a tare da jawo damuwa kan tsaron amfani da irin wannan fasahar makamashi.

Rahotannin shaidu sun nuna cewa lamarin ya faru ne da misalin ƙarfe 3:00 na dare yayin da aka ajiye motocin domin shirin ɗaukar fasinjoji zuwa jihohi daban-daban da safe, inda fashewar ta auku a lokaci guda ta janyo gobara da ta ƙone motocin gaba ɗaya, duk da cewa babu wani mutum a ciki a lokacin da abin ya faru.

  • Gwamna Uba Sani Ya Tsawaita Shirin Sufurin Motocin CNG Kyauta Ga Al’ummar Jihar Kaduna
  • Gwamna Yusuf Ya Mika Motocin Bas Na CNG Guda 10 Ga Kungiyar NLC Reshen Kano

Wani manaja a ɗaya daga cikin kamfanonin sufurin da ke aiki a yankin Mando Motor Park, wanda ya nemi a sakaya sunansa, ya bayyana cewa motocin sabbi ne kuma suna cikin shirin fara aiki ne kafin wannan ibtila’i, yana mai godewa Allah da babu wanda ya jikkata ko ya rasa ransa, duk da girman ɓarnar da aka yi.

ADVERTISEMENT

Sai dai ya bayyana damuwa kan amfani da motocin CNG, yana mai cewa akwai buƙatar ƙarin shiri da tsauraran matakan tsaro kafin a rungumi wannan fasaha gaba ɗaya, inda ya ce “har yanzu ba mu kai matakin da za mu iya sarrafa wannan tsarin ba yadda ya kamata,” yana mai nuni da yiwuwar matsalolin fasaha ko rashin isasshen horo.

A halin yanzu, jami’an ƴansanda da sauran hukumomin da abin ya shafa sun isa wurin domin gudanar da bincike kan musabbabin fashewar, yayin da ake sa ran sakamakon binciken zai fayyace ko matsalar ta samo asali ne daga tsarin gas ɗin ko wasu dalilai na daban, yayin da aka tabbatar da cewa babu asarar rayuka a lamarin.

LABARAI MASU NASABA

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

Kaduna
Abubakar Sulaiman
Website |  + postsBio
  • Abubakar Sulaiman
    Iyalin El-Rufai Sun Bai Ministan Tsaro Wa’adin Kwana 7 Kan Zargin Rikicin Kudancin Kaduna
  • Abubakar Sulaiman
    Atiku Ya Zargi Gwamnatin Tarayya Da Cin Bashi Kamar Mashayin Da Kuɗi Ya Ƙarewa
  • Abubakar Sulaiman
    Boko Haram Ta Kai Hari Adamawa, Ana Fargabar Mutuwar Mutane 11
  • Abubakar Sulaiman
    Ƴan Bindiga Sun Kai Hari Sokoto, Sun Kashe Mutane 7, Sun Yi Garkuwa Da 12

MASU ALAKA

Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja
Labarai

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji
Manyan Labarai

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
'Yan Bindiga
Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Next Post
Sin Da Tanzania Sun Karrama Ma’aikatan Da Suka Rasu Yayin Gina Layin Dogo Na TAZARA 

Sin Da Tanzania Sun Karrama Ma’aikatan Da Suka Rasu Yayin Gina Layin Dogo Na TAZARA 

LABARAI MASU NASABA

Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.