Shugaban ƙasa Bola Tinubu ya bayyana goyon bayansa ga hukumar zaɓe mai zaman kanta ta ƙasa (INEC) ƙarƙashin jagorancin Farfesa Joash Amupitan, yana jaddada cewa hukumar ba ta aikin san kai.
Amma matakin shugaban ƙasa kaɗai ba za su yiwu su sa mutane su amince ba kafin zaɓen 2027. Ya kamata hukumar INEC ta zama mai cin gashin kanta.
Kafin zaɓen da ya gabata na baya, Attahiru Jega da Mahmood Yakubu sun yi haɗin gwiwa da masu ruwa da tsaki a matsayin muhimmin ginshiƙi na gudanar da zaɓe.
Suna gudanar da tarurrukan shawarwari na yau da kullum tare da jam’iyyun siyasa, ƙungiyoyin al’umma, ƴan jarida, hukumomin tsaro, shugabannin gargajiya, abokan hulɗa da masu sa ido kan zaɓe. Yawancin irin wannan tattaunawar mai tasiri a yanzu ba ta nan.
Waɗannan mu’amaloli na baya sun bai wa INEC damar bayyana sauye-sauye, magance damuwa, tabbatar wa ƴan Nijeriya da cewa tana da rashin son kai, da ƙara ƙarfafa amincewar jama’a.
Jagorancin na yanzu na fuskantar wani ƙalubalen sadarwa na daban. Yin hulɗa da masu ruwa da tsaki a bayyane, tare da tattaunawa a fili a kai a kai, zai iya taimakawa sosai wajen ƙarfafa amincewa da tsarin zaɓen 2027.














