ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Musulman Ƴan Wasan Da Suke Azumi A Turai

by Abba Ibrahim Wada
4 months ago
Wasa

A daidai lokacin da Azumi ke ci gaba da tafiya a sassan duniya, inda Musulmai ke ƙaurace wa cin abinci ko shan ruwa daga hudowar alfijir zuwa faɗuwar rana. Wani abu da ya ɗauki hankali shi ne canjin da aka samu a duniyar ƙwallon ƙafa, inda ake ɗan dakatawa ana tsaka da wasa domin bai wa ƴan ƙwallo Musulmai dama su sha ruwa idan rana ta faɗi.

Ɗan wasa Muhammad Salah mai shekara 33 a duniya ɗan asalin Masar ne da ya kasance ginshiƙin ɗan wasa a Liɓerpool a ƴan shekarun nan kuma ɗan wasan da ya kafa tarihi da dama a gasar Premier. Salah yana ɗaya daga cikin ƴan wasa musulmi kuma an daɗe ana ganinsa yana Azumi a lokacin wasa a cikin watan Ramadan.

  • Mahangar Wakiliya Mai Fasahar Wasan Kwaikwayo Game Da Dimokuradiyyar Dake Shafar Kowa Da Kowa A Nan Kasar Sin
  • Kwamitin Kolin JKS Da Majalisar Gudanarwa Ta Kasar Sin Sun Taya Tawagar Kasar Ta Wasannin Olympics Na Lokacin Hunturu Murna

Ɗan wasa William Saliba na ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Arsenal da tawagar ƴan wasan ƙasar Faransa mai shekara 24 na cikin ƴan wasan baya da suka fi ƙwazo a halin yanzu a duniya kuma Arsenal ta dogara da shi a ɓangaren tsaron baya. Shima ɗan wasa Yunus Dimoara Musah ɗan wasan ƙasar Amurka ne da aka haifa a ranar 29 ga watan Nuwamban 2002.

ADVERTISEMENT

Yanzu ɗan wasan yana buga ƙwallo ne a ƙungiyar Atalanta da ke fafatawa a gasar Serie A, a matsayin ɗan aro daga ƙungiyar AC Milan.

Ɗan wasa Hakan Çalhanoğlu ɗan wasan tawagar ƙasar Turkiyya ne da aka haifa a ranar 8 ga Fabrairun 1994. Yanzu haka ɗan wasan yana buga ƙwallo ne a ƙungiyar Inter Milan da ke fafatawa a gasar Seria A ta Italiya.

LABARAI MASU NASABA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Shima Antonio Rüdiger ɗan wasan ƙwallon ƙafa ne ɗan ƙasar Jamus da aka haifa a ranar 3 ga watan Maris na shekarar 1993. Yanzu haka ɗan wasan yana buga wasa ne a ƙungiyar Real Madrid da ke Spain, kuma take fafatawa a gasar La Liga.

Matashin ɗan wasa Lamine Yamal Nasraoui Ebana ɗan wasan tawagar Spain ne da aka haifa a ranar 13 ga watan Yulin shekarar 2007. Yanzu haka matashin ɗanwasan yana buga wasa ne a ƙungiyar Barcelona da ke ƙwallo a gasar La Liga, kuma yana cikin zaratan ƴanƙwallon ke alfahari da su a harkar ƙwallo.

Tsohon ɗan wasan Manchester United da Juɓentus, Paul Labile Pogba ma ɗan wasan ƙasar Faransa ne da aka haifa a ranar 15 ga watan Maris na shekarar 1993. Yanzu ɗan wasan yana buga wasa ne a ƙungiyar Monaco da ke fafatawa a gasar Ligue 1 ta Faransa.

Wasa
Abba Ibrahim Wada
Website |  + postsBio
  • Abba Ibrahim Wada
    Ɗanwasa Thomas Partey Ya Yi Rashin Nasara A Kotun Canada
  • Abba Ibrahim Wada
    FIFA Za Ta Biya Omar Artan Alawus Ɗin Da Za A Bai Wa Kowanne Alƙalin Wasa
  • Abba Ibrahim Wada
    Duk Da Rashin Halartar ‘Super Eagles’ Gasar Kofin Duniya, Nijeriya Ba Ta Rasa Wakilai Ba
  • Abba Ibrahim Wada
    Su Waye Wakilan Afirka A Kofin Duniya?

MASU ALAKA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
Labarai

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
Ra'ayi Riga

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma
Labarai

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Next Post
Me Ya Sa Aka Ki Karbar Tallafi Daga Kasar Amurka?

Me Ya Sa Aka Ki Karbar Tallafi Daga Kasar Amurka?

LABARAI MASU NASABA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026
Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.