Aƙalla mutane 23 sun mutu yayin da wasu 146 suka samu raunuka sakamakon jerin fashewar bama-bamai da suka girgiza birnin Maiduguri, babban birnin jihar Borno, a daren Litinin.
Fashe-fashen sun faru ne a ƙofar shiga ta Asibitin Koyarwa na Jami’ar Maiduguri (UMTH), Kasuwar Litinin da kuma yankin Ofishin Wasiku na tsohon birnin.
- Kasashen Sin Da Amurka Na Tuntubar Juna Dangane Da Ziyarar Shugaba Trump
- Zulum Ya Yi Allah-Wadai Da Fashewar Bam A Maiduguri, Ya Buƙaci A Ƙara Tsaro A Wuraren Ibada
Surajo Abdullahi, mai kula da shiyyar Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta Kasa (NEMA), wanda ya tabbatar da alkaluman, ya ce an kwashe mutane 169 zuwa asibitoci uku a Maiduguri.
“Mutane 108 na karɓar magani a Asibitin Koyarwa na Jami’ar Maiduguri (UMTH), 20 a Asibitin Umaru Shehu, sannan 17 a Asibitin Kwararru na Maiduguri,” in ji shi.















Discussion about this post