Ɗan takarar gwamnan jihar Bauchi wa jam’iyyar APC a zaɓen 2023, Air Marshal Saddique Baba Abubakar (mai ritaya) ya sanar da barin harƙoƙin siyasa daga yanzu sakamakon wasu dalilai da bai bayyana su ba.
Saddique tsohon shugaban sojojin saman Nijeriya (CAS) ne ya shiga harƙoƙin siyasa a 2021 bayan kammala aikin sojan sama.
A zaɓen 2023 ya yi tashe sosai har an sanya masa ran zama gwamnan jihar Bauchi amma Bala Mohammed na jam’iyyar PDP ya kayar da shi.
Hakazalika, Saddique Baba Abubakar yana daga cikin waɗanda ake sa ran za su sake fitowa takarar gwamnan jihar Bauchi a zaɓen 2027 a ƙarƙashin jam’iyyar Action Democratic Party (ADP) kwatsam sai ya fito ya sanar da yin murabus daga harƙoƙin siyasa.
Wannan lamarin ya zo da abun mamaki musamman ga magoya bayansa, inda ya shaida cewar matsayar da ya ɗauka ta kasance masa mai wuyan gaske, sai ya bai wa masoya da magoya bayansa hakuri bisa wannan matsayar nasa.
A wani gajeren saƙon bidiyo da ya fitar wa al’ummar jihar Bauchi a ranar Asabar 16 ga watan Maris 2027, Saddique Baba ya ce duk da ya daina harƙoƙin siyasa, amma zai ci gaba da bayar da gudunmawarsa wajen ci gaban al’umman jihar Bauchi musamman ta ɓangaren kiwon lafiya da ilimi ƙarƙashin gidauniyarsa ta ‘Marshal Care Foundation’.
A saƙon na cewa: “Dukkanin godiya da yabo sun tabbata ga Allah Subhanahu wata’ala; Allah shi kaɗansa ke tabbatar da al’amura.
Abun da Allah ya tabbatar ba mai iya gusar da shi, haka kuma abun da Allah ya gusar ba mai iya tabbatar da shi. “Bayan godiya wa Allah subhanahu wata’ala.
A yau, ina cike da zuciya mai nauyi na yanke mawuyacin shawara barin al’amuran siyasa saboda wasu dalilai nawa.
“Wannan mawuyacin shawarar bai zo mini da sauƙi ba, ganin mutane masu ɗumbin yawa da suka nuna min so da ƙauna a jihar Bauchi da ma ƙasa baki ɗaya tun shigowata siyasa a shekara 2021 har ya zuwa yau,” ya shaida.
“Ina matuƙar godiya marar iyaka. Ina bada haƙuri ga dukkanin masoya da magoya baya game da wannan mawuyacin shawarar da na ɗauka; ina kuma musu fatan alkairi baki ɗaya.
“Ina roƙon Allah Subhanahu wata’ala ya saka wa kowa da mafificin alkairi.
“Ya ci gaba da cewa a kowani lokaci a shirya yake wajen ci gaba da taimaka wa al’umma musamman a ɓangaren ilimin da kiwon lafiya.
“Kasancewar na bar siyasa ba zai hanani ci gaba da taimaka wa al’umma ba ta gidauniyata ta Marshal Care Foundation musamman a fannonin ilimi, da kiwon lafiya.”
“A ƙarshe ina sake miƙa godiya ta ga dukkanin al’umma; Allah saka wa kowa da alkairi. Allah ya zaunar da kasa lafiya, Allah ya shiga cikin al’amuranmu baki daya.”















Discussion about this post