ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Tuesday, July 14, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Na Bar Harƙoƙin Siyasa Gaba Ɗaya – Ɗan Takarar Gwamnan Bauchi, Air Marshal Saddique Baba

by Khalid Idris Doya
2 months ago

Ɗan takarar gwamnan jihar Bauchi wa jam’iyyar APC a zaɓen 2023, Air Marshal Saddique Baba Abubakar (mai ritaya) ya sanar da barin harƙoƙin siyasa daga yanzu sakamakon wasu dalilai da bai bayyana su ba.

Saddique tsohon shugaban sojojin saman Nijeriya (CAS) ne ya shiga harƙoƙin siyasa a 2021 bayan kammala aikin sojan sama.

A zaɓen 2023 ya yi tashe sosai har an sanya masa ran zama gwamnan jihar Bauchi amma Bala Mohammed na jam’iyyar PDP ya kayar da shi.

ADVERTISEMENT

Hakazalika, Saddique Baba Abubakar yana daga cikin waɗanda ake sa ran za su sake fitowa takarar gwamnan jihar Bauchi a zaɓen 2027 a ƙarƙashin jam’iyyar Action Democratic Party (ADP) kwatsam sai ya fito ya sanar da yin murabus daga harƙoƙin siyasa.

Wannan lamarin ya zo da abun mamaki musamman ga magoya bayansa, inda ya shaida cewar matsayar da ya ɗauka ta kasance masa mai wuyan gaske, sai ya bai wa masoya da magoya bayansa hakuri bisa wannan matsayar nasa.

LABARAI MASU NASABA

“Buhari Ya Taɓa tambaya Ta Mutane Nawa Na Kashe Saboda Yawan Azumin Dana Ke Yi”

Kyawawan Manufofin Buhari Za Su Ci Gaba Da Yi Wa ’Yan Nijeriya Tasiri – Tinubu

A wani gajeren saƙon bidiyo da ya fitar wa al’ummar jihar Bauchi a ranar Asabar 16 ga watan Maris 2027, Saddique Baba ya ce duk da ya daina harƙoƙin siyasa, amma zai ci gaba da bayar da gudunmawarsa wajen ci gaban al’umman jihar Bauchi musamman ta ɓangaren kiwon lafiya da ilimi ƙarƙashin gidauniyarsa ta ‘Marshal Care Foundation’.

A saƙon na cewa: “Dukkanin godiya da yabo sun tabbata ga Allah Subhanahu wata’ala; Allah shi kaɗansa ke tabbatar da al’amura.

Abun da Allah ya tabbatar ba mai iya gusar da shi, haka kuma abun da Allah ya gusar ba mai iya tabbatar da shi. “Bayan godiya wa Allah subhanahu wata’ala.

A yau, ina cike da zuciya mai nauyi na yanke mawuyacin shawara barin al’amuran siyasa saboda wasu dalilai nawa.

“Wannan mawuyacin shawarar bai zo mini da sauƙi ba, ganin mutane masu ɗumbin yawa da suka nuna min so da ƙauna a jihar Bauchi da ma ƙasa baki ɗaya tun shigowata siyasa a shekara 2021 har ya zuwa yau,” ya shaida.

“Ina matuƙar godiya marar iyaka. Ina bada haƙuri ga dukkanin masoya da magoya baya game da wannan mawuyacin shawarar da na ɗauka; ina kuma musu fatan alkairi baki ɗaya.

“Ina roƙon Allah Subhanahu wata’ala ya saka wa kowa da mafificin alkairi.

“Ya ci gaba da cewa a kowani lokaci a shirya yake wajen ci gaba da taimaka wa al’umma musamman a ɓangaren ilimin da kiwon lafiya.

“Kasancewar na bar siyasa ba zai hanani ci gaba da taimaka wa al’umma ba ta gidauniyata ta Marshal Care Foundation musamman a fannonin ilimi, da kiwon lafiya.”

“A ƙarshe ina sake miƙa godiya ta ga dukkanin al’umma; Allah saka wa kowa da alkairi. Allah ya zaunar da kasa lafiya, Allah ya shiga cikin al’amuranmu baki daya.”

Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    ATBU Ta Janye Filin Ginin Masallaci Da Ta Bai wa TIMSAN, Ta Amince Kowa Ya Yi Addininsa Yadda Ya Fahimta
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ɗan Majalisar Dokokin Bauchi, Hon. Wanzam, Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Tsohon Mataimakin Gwamnan Bauchi, Audu Sule Katagum Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Kotu Ta Umarci DSS Ta Mutunta Umarninta Kan Shari’ar Filin Firo Na Bauchi

MASU ALAKA

“Buhari Ya Taɓa tambaya Ta Mutane Nawa Na Kashe Saboda Yawan Azumin Dana Ke Yi”
Manyan Labarai

“Buhari Ya Taɓa tambaya Ta Mutane Nawa Na Kashe Saboda Yawan Azumin Dana Ke Yi”

July 14, 2026
Tinubu Ya Gana da Gwamnan Kwara Bayan Harin Ta’addanci Da Ya Yi Ajalin Sama Da Mutane 160
Manyan Labarai

Kyawawan Manufofin Buhari Za Su Ci Gaba Da Yi Wa ’Yan Nijeriya Tasiri – Tinubu

July 14, 2026
Kotu Ta Hana INEC Amincewa Da Tarukan ADC Ƙarƙashin Jagorancin David Mark
Manyan Labarai

Kotu Ta Hana INEC Amincewa Da Tarukan ADC Ƙarƙashin Jagorancin David Mark

July 13, 2026
Next Post
Tawagogin Sin Da Amurka Masu Tattauna Batutuwan Tattalin Arziki Da Cinikayya Sun Cimma Sakamako Mai Gamsarwa

Tawagogin Sin Da Amurka Masu Tattauna Batutuwan Tattalin Arziki Da Cinikayya Sun Cimma Sakamako Mai Gamsarwa

LABARAI MASU NASABA

Tsaka mai wuyar Infantino da Koma bayan mulkin yamma

Tsaka mai wuyar Infantino da Koma bayan mulkin yamma

July 14, 2026
“Buhari Ya Taɓa tambaya Ta Mutane Nawa Na Kashe Saboda Yawan Azumin Dana Ke Yi”

“Buhari Ya Taɓa tambaya Ta Mutane Nawa Na Kashe Saboda Yawan Azumin Dana Ke Yi”

July 14, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Ce Za A Gurfanar Da Tubabbun ’Yan ta’addan Da Suka Sake Aikata Manyan Laifuka

Gwamnatin Tarayya Ta Ce Za A Gurfanar Da Tubabbun ’Yan ta’addan Da Suka Sake Aikata Manyan Laifuka

July 14, 2026
Tinubu Ya Gana da Gwamnan Kwara Bayan Harin Ta’addanci Da Ya Yi Ajalin Sama Da Mutane 160

Kyawawan Manufofin Buhari Za Su Ci Gaba Da Yi Wa ’Yan Nijeriya Tasiri – Tinubu

July 14, 2026
Abin Da Ake Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin” Da Aka Yanke Wa Sin Na Kashin Kanta Ba Shi Da Wani Amfani

Abin Da Ake Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin” Da Aka Yanke Wa Sin Na Kashin Kanta Ba Shi Da Wani Amfani

July 13, 2026
Tafiye-tafiyen Fasinjojin Jirgin Kasa A Kasar Sin Sun Haura Biliyan 2.3 A Rabin Farko Na Bana

Tafiye-tafiyen Fasinjojin Jirgin Kasa A Kasar Sin Sun Haura Biliyan 2.3 A Rabin Farko Na Bana

July 13, 2026
Gwamnatin Tarayya Za Ta Ƙaddamar Da Tsarin Daƙile Rugujewar Gine-Gine

Gwamnatin Tarayya Za Ta Ƙaddamar Da Tsarin Daƙile Rugujewar Gine-Gine

July 13, 2026
Me Ya Sa Ake Ganin Afrika Na Da Damar Taka Rawa A Tsarin Tattalin Arzikin Duniya?

Me Ya Sa Ake Ganin Afrika Na Da Damar Taka Rawa A Tsarin Tattalin Arzikin Duniya?

July 13, 2026
Jiragen Kasan Sin Sun Yi Tafiye-Tafiyen Fasinjoji Sama Da Biliyan 2.3 A Rabin Farko Na Bana

Jiragen Kasan Sin Sun Yi Tafiye-Tafiyen Fasinjoji Sama Da Biliyan 2.3 A Rabin Farko Na Bana

July 13, 2026
Kotu Ta Hana INEC Amincewa Da Tarukan ADC Ƙarƙashin Jagorancin David Mark

Kotu Ta Hana INEC Amincewa Da Tarukan ADC Ƙarƙashin Jagorancin David Mark

July 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.