ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Na Bar Harƙoƙin Siyasa Gaba Ɗaya – Ɗan Takarar Gwamnan Bauchi, Air Marshal Saddique Baba

by Khalid Idris Doya
3 weeks ago

Ɗan takarar gwamnan jihar Bauchi wa jam’iyyar APC a zaɓen 2023, Air Marshal Saddique Baba Abubakar (mai ritaya) ya sanar da barin harƙoƙin siyasa daga yanzu sakamakon wasu dalilai da bai bayyana su ba.

Saddique tsohon shugaban sojojin saman Nijeriya (CAS) ne ya shiga harƙoƙin siyasa a 2021 bayan kammala aikin sojan sama.

A zaɓen 2023 ya yi tashe sosai har an sanya masa ran zama gwamnan jihar Bauchi amma Bala Mohammed na jam’iyyar PDP ya kayar da shi.

ADVERTISEMENT

Hakazalika, Saddique Baba Abubakar yana daga cikin waɗanda ake sa ran za su sake fitowa takarar gwamnan jihar Bauchi a zaɓen 2027 a ƙarƙashin jam’iyyar Action Democratic Party (ADP) kwatsam sai ya fito ya sanar da yin murabus daga harƙoƙin siyasa.

Wannan lamarin ya zo da abun mamaki musamman ga magoya bayansa, inda ya shaida cewar matsayar da ya ɗauka ta kasance masa mai wuyan gaske, sai ya bai wa masoya da magoya bayansa hakuri bisa wannan matsayar nasa.

LABARAI MASU NASABA

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Gwamnatin Zamfara Ta Shirya Tallafa Wa Mata Da Masu Ƙaramin Ƙarfi Fiye Da Miliyan Ɗaya

A wani gajeren saƙon bidiyo da ya fitar wa al’ummar jihar Bauchi a ranar Asabar 16 ga watan Maris 2027, Saddique Baba ya ce duk da ya daina harƙoƙin siyasa, amma zai ci gaba da bayar da gudunmawarsa wajen ci gaban al’umman jihar Bauchi musamman ta ɓangaren kiwon lafiya da ilimi ƙarƙashin gidauniyarsa ta ‘Marshal Care Foundation’.

A saƙon na cewa: “Dukkanin godiya da yabo sun tabbata ga Allah Subhanahu wata’ala; Allah shi kaɗansa ke tabbatar da al’amura.

Abun da Allah ya tabbatar ba mai iya gusar da shi, haka kuma abun da Allah ya gusar ba mai iya tabbatar da shi. “Bayan godiya wa Allah subhanahu wata’ala.

A yau, ina cike da zuciya mai nauyi na yanke mawuyacin shawara barin al’amuran siyasa saboda wasu dalilai nawa.

“Wannan mawuyacin shawarar bai zo mini da sauƙi ba, ganin mutane masu ɗumbin yawa da suka nuna min so da ƙauna a jihar Bauchi da ma ƙasa baki ɗaya tun shigowata siyasa a shekara 2021 har ya zuwa yau,” ya shaida.

“Ina matuƙar godiya marar iyaka. Ina bada haƙuri ga dukkanin masoya da magoya baya game da wannan mawuyacin shawarar da na ɗauka; ina kuma musu fatan alkairi baki ɗaya.

“Ina roƙon Allah Subhanahu wata’ala ya saka wa kowa da mafificin alkairi.

“Ya ci gaba da cewa a kowani lokaci a shirya yake wajen ci gaba da taimaka wa al’umma musamman a ɓangaren ilimin da kiwon lafiya.

“Kasancewar na bar siyasa ba zai hanani ci gaba da taimaka wa al’umma ba ta gidauniyata ta Marshal Care Foundation musamman a fannonin ilimi, da kiwon lafiya.”

“A ƙarshe ina sake miƙa godiya ta ga dukkanin al’umma; Allah saka wa kowa da alkairi. Allah ya zaunar da kasa lafiya, Allah ya shiga cikin al’amuranmu baki daya.”

Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Zaɓen Fidda Gwani Na Gwamna: Ba Za Mu Lamunci Kaƙaba Mana Ɗan Takara A Bauchi Ba – Mambobin APC
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Sanata Buba Ya Janye Daga Takarar Fidda Gwani Ta Gwamnan APC A Bauchi, Ya Zargi Cewa ‘Ɗauki Ɗaura Ake Yi Ba Zaɓe Ba”
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Shugaban Kwamitin Yaɗa Labarai Na Aikin Hajjin Bana Na Bauchi Ya Rasu A Saudiyya
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Gwamna Bala Ya Sayi Fom Ɗin Takarar Sanatan Bauchi ta Kudu A Jam’iyyar APM

MASU ALAKA

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro
Manyan Labarai

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Zamfara Ta Shirya Tallafa Wa Mata Da Masu Ƙaramin Ƙarfi Fiye Da Miliyan Ɗaya
Manyan Labarai

Gwamnatin Zamfara Ta Shirya Tallafa Wa Mata Da Masu Ƙaramin Ƙarfi Fiye Da Miliyan Ɗaya

June 3, 2026
Kotu Ta Yanke Wa Waɗanda Suka Kai Hari Cocin Owo Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya
Manyan Labarai

Kotu Ta Yanke Wa Waɗanda Suka Kai Hari Cocin Owo Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya

June 3, 2026
Next Post
Tawagogin Sin Da Amurka Masu Tattauna Batutuwan Tattalin Arziki Da Cinikayya Sun Cimma Sakamako Mai Gamsarwa

Tawagogin Sin Da Amurka Masu Tattauna Batutuwan Tattalin Arziki Da Cinikayya Sun Cimma Sakamako Mai Gamsarwa

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026
Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

June 3, 2026
An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Magadan Gari Na 2026 A Beijing

An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Magadan Gari Na 2026 A Beijing

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.