ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Na Bar Harƙoƙin Siyasa Gaba Ɗaya – Ɗan Takarar Gwamnan Bauchi, Air Marshal Saddique Baba

by Khalid Idris Doya
1 month ago

Ɗan takarar gwamnan jihar Bauchi wa jam’iyyar APC a zaɓen 2023, Air Marshal Saddique Baba Abubakar (mai ritaya) ya sanar da barin harƙoƙin siyasa daga yanzu sakamakon wasu dalilai da bai bayyana su ba.

Saddique tsohon shugaban sojojin saman Nijeriya (CAS) ne ya shiga harƙoƙin siyasa a 2021 bayan kammala aikin sojan sama.

A zaɓen 2023 ya yi tashe sosai har an sanya masa ran zama gwamnan jihar Bauchi amma Bala Mohammed na jam’iyyar PDP ya kayar da shi.

ADVERTISEMENT

Hakazalika, Saddique Baba Abubakar yana daga cikin waɗanda ake sa ran za su sake fitowa takarar gwamnan jihar Bauchi a zaɓen 2027 a ƙarƙashin jam’iyyar Action Democratic Party (ADP) kwatsam sai ya fito ya sanar da yin murabus daga harƙoƙin siyasa.

Wannan lamarin ya zo da abun mamaki musamman ga magoya bayansa, inda ya shaida cewar matsayar da ya ɗauka ta kasance masa mai wuyan gaske, sai ya bai wa masoya da magoya bayansa hakuri bisa wannan matsayar nasa.

LABARAI MASU NASABA

Hajjin 2026: NAHCON Ta Kammala Jigilar Alhazan Nijeriya Daga Saudiyya

Yan Bindiga Sun Kashe Manoma Shida A Birnin Gwari Ta Jihar Kaduna

A wani gajeren saƙon bidiyo da ya fitar wa al’ummar jihar Bauchi a ranar Asabar 16 ga watan Maris 2027, Saddique Baba ya ce duk da ya daina harƙoƙin siyasa, amma zai ci gaba da bayar da gudunmawarsa wajen ci gaban al’umman jihar Bauchi musamman ta ɓangaren kiwon lafiya da ilimi ƙarƙashin gidauniyarsa ta ‘Marshal Care Foundation’.

A saƙon na cewa: “Dukkanin godiya da yabo sun tabbata ga Allah Subhanahu wata’ala; Allah shi kaɗansa ke tabbatar da al’amura.

Abun da Allah ya tabbatar ba mai iya gusar da shi, haka kuma abun da Allah ya gusar ba mai iya tabbatar da shi. “Bayan godiya wa Allah subhanahu wata’ala.

A yau, ina cike da zuciya mai nauyi na yanke mawuyacin shawara barin al’amuran siyasa saboda wasu dalilai nawa.

“Wannan mawuyacin shawarar bai zo mini da sauƙi ba, ganin mutane masu ɗumbin yawa da suka nuna min so da ƙauna a jihar Bauchi da ma ƙasa baki ɗaya tun shigowata siyasa a shekara 2021 har ya zuwa yau,” ya shaida.

“Ina matuƙar godiya marar iyaka. Ina bada haƙuri ga dukkanin masoya da magoya baya game da wannan mawuyacin shawarar da na ɗauka; ina kuma musu fatan alkairi baki ɗaya.

“Ina roƙon Allah Subhanahu wata’ala ya saka wa kowa da mafificin alkairi.

“Ya ci gaba da cewa a kowani lokaci a shirya yake wajen ci gaba da taimaka wa al’umma musamman a ɓangaren ilimin da kiwon lafiya.

“Kasancewar na bar siyasa ba zai hanani ci gaba da taimaka wa al’umma ba ta gidauniyata ta Marshal Care Foundation musamman a fannonin ilimi, da kiwon lafiya.”

“A ƙarshe ina sake miƙa godiya ta ga dukkanin al’umma; Allah saka wa kowa da alkairi. Allah ya zaunar da kasa lafiya, Allah ya shiga cikin al’amuranmu baki daya.”

Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ɗan Majalisar Dokokin Bauchi, Hon. Wanzam, Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Tsohon Mataimakin Gwamnan Bauchi, Audu Sule Katagum Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Kotu Ta Umarci DSS Ta Mutunta Umarninta Kan Shari’ar Filin Firo Na Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ana Zargin Jami’in Kwastam Da Kashe Kansa A Bauchi Saboda Damuwa

MASU ALAKA

Maniyyatan Nijeriya
Manyan Labarai

Hajjin 2026: NAHCON Ta Kammala Jigilar Alhazan Nijeriya Daga Saudiyya

June 23, 2026
'Yan Bindiga
Manyan Labarai

Yan Bindiga Sun Kashe Manoma Shida A Birnin Gwari Ta Jihar Kaduna

June 23, 2026
Cire Tallafin Mai: Za A Fara Bai Wa Talakawa Dubu 8 Duk Wata
Manyan Labarai

Tinubu Ya Aike Da Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi Zuwa Majalisar Dattawa

June 23, 2026
Next Post
Tawagogin Sin Da Amurka Masu Tattauna Batutuwan Tattalin Arziki Da Cinikayya Sun Cimma Sakamako Mai Gamsarwa

Tawagogin Sin Da Amurka Masu Tattauna Batutuwan Tattalin Arziki Da Cinikayya Sun Cimma Sakamako Mai Gamsarwa

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

June 23, 2026
Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

June 23, 2026
Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

June 23, 2026
Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

June 23, 2026
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

’Yansanda Sun Kama Mutane 57 Da Ake Zargi Da Ayyukan Ta’addanci A Adamawa

June 23, 2026
Li Qiang Ya Gana Da Firaministan Kasar Guinea

Li Qiang Ya Gana Da Firaministan Kasar Guinea

June 23, 2026
Maniyyatan Nijeriya

Hajjin 2026: NAHCON Ta Kammala Jigilar Alhazan Nijeriya Daga Saudiyya

June 23, 2026
Kamfanin Sin Ya Kammala Babban Aikin Samar Da Ruwa A Babban Birnin Nijeriya

Kamfanin Sin Ya Kammala Babban Aikin Samar Da Ruwa A Babban Birnin Nijeriya

June 23, 2026
Binciken CGTN: Fasahohin Zamani Sun Habaka Ayyuka Yayin Da Tsarin Cin Moriya Tare Ya Yi Fintinkau

Binciken CGTN: Fasahohin Zamani Sun Habaka Ayyuka Yayin Da Tsarin Cin Moriya Tare Ya Yi Fintinkau

June 23, 2026
'Yan Bindiga

Yan Bindiga Sun Kashe Manoma Shida A Birnin Gwari Ta Jihar Kaduna

June 23, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.