ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, September 10, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Nazari A Kan Noman Agwaluma

by Abubakar Abba
6 months ago
Noman

LABARAI MASU NASABA

Kha’amuna Khadi Ta Karɓi Jagorancin Gudanarwa Ta Bankin Noma

Dalilin Da Ya Sa Aka Horar Da Manoman Tumatir 100 A Garin Zariya

Ba a cika bai wa noman Agwaluma muhimmanci kamar yadda ake bai wa sauran amfanin gonar da ake shukawa a Nijeriya ba.

 A yaren Yarbanci, ana kiran ta da Agbalumo, da Iyamuranci; ana kiran ta da Udara, a Jihar Edo; ana kiran ta Otien, inda a yaran Hausa kuma ake kiran ta da Agwaluma.

  • Wang Yi Ya Zanta Ta Wayar Tarho Da Ministar Harkokin Wajen Birtaniya 
  • Aikin Zamantar Da Tashoshin Jiragen Ruwan Nijeriya Zai Rage Wa Kasa Asasar Naira Tiriliyan Daya —Dantsoho

Manoman da suka shiga cikin fannin, musamman a Nijeriya, na samar wa da kawunansu kudaden shiga masu yawa, haka a daukacin Nijeriya, babu wani  addini da ya haramta yin amfani da ita, haka nan kuma; tana kara samun karbuwa a kasuwannin kasar nan.

Yadda Ake Shuka Irin Agwaluma:

Za ka iya shuka Irin nomanta, inda ake bukatar kada Irin ya wuce  tsawon wata hudu, inda a lokacin da za ka yi shukar ake bukatar ka tabbatar da ka yi a lokacin rani.

Har ila yau, nau’in Agwaluma na agbalumo ko kuma na Udara, na bukatar yi masa ban ruwa sosai, musamman don ya yi saurin nuna a cikin kasar noman da aka shuka shi.

Bugu da kari, idan manomi zai sayo Irin nomansa, ya tabbatar da ya sayo a gurin da aka fi sani, musamman don ya samu ingantacce kuma mai lafiya.

Ba Ta Kariya Daga Kamuwa Da Kwari Ko Sauran Cututtukan Da Ke Harbin Amfanin Gona:

Ana bukatar manomi ya tabbatar da yana ba ta kariya daga harbin kwari ko cututtukan da ke yi mata illa bayan ana shuka ta, domin irin wadannan cututtukan ko kwarin na iya hana Irinta da aka shuka ruba a cikin kasar noman da aka shuka Irin.

Zuwa Tsawon Wane Lokaci Agwaluma Ke Kammala Girma?

Bayan an shuka Agwaluma, musamman Gona na fara fitar da ‘ya’yanta ne daga shekara biyar zuwa 10, inda kuma ake saran saiwar  jikinta, domin adana wa ta fi bukatar yanayin da ya kai ma’unin yanayi daga 60 zuwa 70.

Har ila yau, wasu sun yi hasashen cewa, ba za a iya yin noman Agwaluma a Nijeriya ba, amma maganar ba haka take ba; domin ana iya yin nomanta kuma ta yi kyau sosai har dimbin wacce za a yi hada-hadar kasuwancinta abin da kawai ake bukata shi ne, mayar da hankali kan shuka ta da aka yi da nuna kwarin gwiwa da kuma ba ta kulawar da ta dace.

Abubuwan Da Ya Kamata A Tanada Na Noman Agwaluma Don Samun Riba A Nijeriya

Samar Da Kyakkyawan Tsari:

Kafin ka fara yin nomanta, ka tabbatar ka tsara  yadda noman nata zai kasance, musamman domin kaucewa yin asara bayan ka  zuba jarinka a ciki.

Gyaran Gonar Shuka Ta:

Kafin ka shuka Irinta, ana bukatar ka tabbatar da kasar noman nata mai kyau ce.

Zabo Nau’in Da Ya Dace:

Na bukatar ka zabo daga cikin nau’ukanta biyu, wato na  Udara ko kuma na Agbalumo, inda ake iya gano su ta hanyar girmansu.

Amfanin na kai wa tsawon shekara takwas kafin ta kammala girma, inda kuma aka kara habaka nau’insa wanda zai iya girma bayan shekara uku.

Yadda Ake Girbe Agwaluma:

Akasari, ana  girbe ta ne a watan Disamba, sai dai a wannan lokaci, ba ta yin dadi sosai; saboda haka, ana so a bar ta a gonar da aka shuka ta har wani ruwan saman ya kara dukan ta kafin a girbe ta, inda ake  yi mata girbin bayan Ganyen ta ya rikide zuwa ruwan dorawa.

Tsara Dabarun Hada-Hadar Kasuwancinta:

Bayan an shuka ta ta girma, za a iya kai ta kasuwa don sayarwa, domin ana nuna ci gaba da batan ta a kasuwa ganin cewa, ana yawan yin amfani da ita. Haka kuma manomi, zai iya wallafa tallan ta a kafar yanar gizo, don masu bukata su gani su kuma saya.

Noman
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Tun Ina Karama Marigayi Tumbuleke Ke Sa Ni Dariya —Hannatu Musawa
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    NPA Ta Bayyana Cewa Kirkiro Da Sabuwar Hukumar NPERA Ba Zai Zame Mata Tarnaki Ba
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Yadda Bikin Girke-girke Ya Karfafa Alaka Tsakanin Musulmai Da Kiristoci A Kaduna
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Nazari Kan Wasu Dalilan Da Ke Haddasa Sabanin Abotakar Jarumi Ko Jaruma A Kannywood
ADVERTISEMENT

MASU ALAKA

Abin Da Ya Sa Gidauniyar NADF Da Bankin Manoma Suka Yi Haḍaka
Noma Da Kiwo

Kha’amuna Khadi Ta Karɓi Jagorancin Gudanarwa Ta Bankin Noma

August 1, 2026
Dalilin Da Ya Sa Aka Horar Da Manoman Tumatir 100 A Garin Zariya
Noma Da Kiwo

Dalilin Da Ya Sa Aka Horar Da Manoman Tumatir 100 A Garin Zariya

July 18, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Noma Da Kiwo

Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa

July 11, 2026
Next Post
Ƙasashen Afirka Sun Fara Neman Man Fetur Daga Nijeriya, Dangote Ya Ƙara Farashi

Ƙasashen Afirka Sun Fara Neman Man Fetur Daga Nijeriya, Dangote Ya Ƙara Farashi

LABARAI MASU NASABA

Cutar Mashaƙo Ta Ɓarke A Kano, Katsina Da Filato

Mashaƙo: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Sun Kai 27 A Filato

September 10, 2026
An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

Wane Ne Dan Shagamu: Su Wane Ne Suka Kashe Shi A Kano?

September 10, 2026
Al’umma Sun Yaba Wa Sojoji Kan Yaƙar ’Yan Bindiga A Zamfara

Al’umma Sun Yaba Wa Sojoji Kan Yaƙar ’Yan Bindiga A Zamfara

September 10, 2026
Ambaliyar Ruwa Ta Tafi Da Ɗalibai 2 A Abuja Da Abia

Ambaliyar Ruwa Ta Tafi Da Ɗalibai 2 A Abuja Da Abia

September 10, 2026
’Yansanda Sun Kama Wadda Ta Yaɗa Labarin OPay Zai Daina Aiki A Nijeriya

’Yansanda Sun Kama Wadda Ta Yaɗa Labarin OPay Zai Daina Aiki A Nijeriya

September 10, 2026
2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato

2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato

September 10, 2026
Zabe: Gwamnatin Kano Ta Taƙaita Zirga-zirgar Mutane Da Ababen Hawa

Gwamna Yusuf Ya Umarci Jami’an Tsaro Su Gano Waɗanda Suka Kashe Danshagamu

September 10, 2026
Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

September 9, 2026
An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

September 9, 2026
Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba

Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba

September 9, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.