Gwamnatin jamhuriyar Nijar ta rattaba hannu kan wata yarjeniyar gina sabuwar matatar man fetur tsakaninta da kamfanin ƙasar Canada Zimar Group a jihar Dosso da ke kudu maso yammacin Kasar.
Ranar sanar da ta gabata, ministan harakokin wajen Nijar kana shugaban ƙwamitin tattaunawa da abokan hulɗa Bakary Yaou Sangaré, shi da Darakta Janar na kamfanin Benjamin Day Mark suka sanya a yarjejeniyar a Yamai fadar Gwamnatin Kasar.
Sabuwar matatar man wadda za ta laƙume kusan dala biliyan 2 kwatankwacin CFA Triliyan 1 da biliyan 77 idan aikinta ya kammala ana saran za ta rika tace ganga mai dubu 100 kowace rana.
Yarjejeniyar da bangarorin biyu suka cimma ta soma aiki nan take sannan za ta ɗauki tsawon shekaru 16, uku na aikin ginata sai 13 na tace man fetur ɗin.
Wannan dai na zuwa ƙasa da mako guda bayan ƙasar ta yammacin Afirka ta ƙulla wata yarjeniyar da kamfanin Sonatrach na ƙasar Aljeriya don soma aikin hako man fetur a yankin Kafra da ke jihar Agadas.














