ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, July 17, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

NIS Ta Fara Sintirin Fatattakar Baƙin Haure Mai Taken “Saukar Shaho” A Bayelsa

by Yusuf Shuaibu
4 years ago
Bayelsa

Hukumar shige da fice ta ƙasa (NIS) reshen Jihar Bayelsa ta samu amincewar shugaban hukumar na ƙasa, Isah Jere Idris wajen ƙaddamar da sintiri na musamman domin fatattakar baƙin haure a Jihar Bayelsa da aka yi wa laƙabi da “Saukar Shaho”.

An ƙaddamar da sintirin ne, saboda tsaftace jihar daga kwararowar baƙin haure da ke keta dokokin shige da fice da ƙungiyar ECOWAS ta tanadar wa mambobinta, wanda hakan ya sa dole a ƙarfafa tsaron rayukan ‘yan Nijeriya da dukiyoyinsu, sakamakon irin matsalolin tsaro da ake fuskanta wanda dole hukumomi da ke bakin iyakokin ƙasar nan su ɗauki matakan da suka kamata.

  • Rayuwata A Shekara 70 -Mai Martaba Etsu Nupe

Hukumar ta bayyana haka ne a cikin wata sanarwa da ta fitar a ranar 9 ga watan Satumbar 2022 da jami’in hulɗa da jama’a na hukumar NIS reshen Jihar Bayelsa ya rattaba wa hannu.

ADVERTISEMENT

Sanarwar ta ce shirin ya samu amincewar Shugaban NIS, Isah Jere Idris da mai girma gwamnan Jihar Bayelsa, Sanata Douye Diri domin ganin ya gudana kan kare haƙƙin baƙi da adalci da ‘yancinsu tare da fahimtar dangantakan da ke tsakanin yankuna na ƙasa da ƙasa wanda su ne za a yi la’akari da su wajen gudanar da sintirin.

A cewar sanarwar, ana tsammanin shirin zai gudana ne na tsawan mako guda da zai karaɗe ɗungu da saƙo da ke faɗin Jihar Bayelsa da dukkan ƙananan hukumominta.

LABARAI MASU NASABA

Mata Manoma Sun Gina Gada, Rijiyar Burtsatse A Danbare, Kano

An Ceto Wasu Mutane Huɗu Da Aka Sace A Kogi

Haka kuma ta ce wannan zai bayar da dama taskace duk wani bayanan baƙi da hana waɗanda ba ‘yan ƙasa su karya dokokin Nijeriya wajen ganin ba su jefa ƙuri’a a zaɓe mai zuwa ba.

Sanarwar ta ƙara da cewa tun a gwajin farko a lamu na nuna cewa za a kawo ƙarshen karya dokokin shige da fice da tsaftace lamarin shige da fice tare da tabbatar da bin dokikin shige da fice wanda ya haɗa da bayar da izinin zama da sake sabunta takardun waɗanda aka ba su izinin zama a Jihar Bayelsa.

Bayelsa
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Sautin Muryar Da Aka Fallasa Kan El-Rufai Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Ci-ma-zaunen Ƴan Siyasa Ne Ke Tunanin Yin Maguɗi A Zaɓen 2027 – Makarfi
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    An Samu Ruɗani Kan Rashin Bayyana Jerin Ƴan Takarar Jam’iyyun Siyasa Na Zaɓen 2027

MASU ALAKA

Mata Manoma Sun Gina Gada, Rijiyar Burtsatse A Danbare, Kano
Labarai

Mata Manoma Sun Gina Gada, Rijiyar Burtsatse A Danbare, Kano

July 17, 2026
An Ceto Wasu Mutane Huɗu Da Aka Sace A Kogi
Labarai

An Ceto Wasu Mutane Huɗu Da Aka Sace A Kogi

July 17, 2026
Yunkurin Dauda Lawal Na Bunkasa Bangaren Ma’adanan Jihar Zamfara
Rahotonni

Yunkurin Dauda Lawal Na Bunkasa Bangaren Ma’adanan Jihar Zamfara

July 17, 2026
Next Post
Jihohin Arewa Da Suka Fi Noma Waken Soya A Nijeriya

Jihohin Arewa Da Suka Fi Noma Waken Soya A Nijeriya

LABARAI MASU NASABA

Mata Manoma Sun Gina Gada, Rijiyar Burtsatse A Danbare, Kano

Mata Manoma Sun Gina Gada, Rijiyar Burtsatse A Danbare, Kano

July 17, 2026
Yadda NDLEA Ke Fatattakar Dillalan Miyagun Kwayoyi Na Kudancin Amurka

Yadda NDLEA Ke Fatattakar Dillalan Miyagun Kwayoyi Na Kudancin Amurka

July 17, 2026
Gwamnan Da Bai Taba Samun Mulkin Jihar Kano Ba

Gwamnan Da Bai Taba Samun Mulkin Jihar Kano Ba

July 17, 2026
An Ceto Wasu Mutane Huɗu Da Aka Sace A Kogi

An Ceto Wasu Mutane Huɗu Da Aka Sace A Kogi

July 17, 2026
NPA Ta Tara Kudin Shiga Naira Biliyan 758.2 A 2024

Dalilin Da Ya Sa Kungiyar NCTR Ta Jinjina Wa Shugaban NPA

July 17, 2026
Yunkurin Dauda Lawal Na Bunkasa Bangaren Ma’adanan Jihar Zamfara

Yunkurin Dauda Lawal Na Bunkasa Bangaren Ma’adanan Jihar Zamfara

July 17, 2026
Gbajabiamila Ya Maka Daraktan Bogi Na PFIPC Kotu, Ya Nemi Diyyar Biliyan 15

Gbajabiamila Ya Maka Daraktan Bogi Na PFIPC Kotu, Ya Nemi Diyyar Biliyan 15

July 17, 2026
Bayan Ceto Daliban Oyo: Kallo Ya Koma Borno Da Yobe

Bayan Ceto Daliban Oyo: Kallo Ya Koma Borno Da Yobe

July 17, 2026
Batun Yawan Bashin Da Nijeriya Ke Ciyowa Daga Ketare

Batun Yawan Bashin Da Nijeriya Ke Ciyowa Daga Ketare

July 17, 2026
Pew: Sin Ta fi Amurka Samun Amincewar Al’ummun Duniya

Pew: Sin Ta fi Amurka Samun Amincewar Al’ummun Duniya

July 16, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.