ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, July 10, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

NIS Na Taka Muhimmiyar Rawa Wajen Bunkasa Zuba Jari A Nijeriya –CI James

by Khalid Idris Doya
3 years ago
NIS

Kwanturolan hukumar kula da shige da fice ta kasa (Immigration) a jihar Ribas, CI James Sunday, ya misalta ayyukan hukumar a matsayin wanda ke taka muhimmiyar rawa wajen bunkasa sashen zuba jari a Nijeriya.

Sunday wanda ke magana da ‘yan jarida kan rawar da hukumar ke takawa wajen kyautata tattalin arzikin kasa, ya ce, a matsayinsu na masu kula da shige da fice da iyakokin kasa, aikinsu na da alaka kai tsaye da tattalin arziki, siyasa, tsaro, ilimi, addini da kyautata kiwon lafiya a kasar nan.

  • Hukumar Raba Daidai Ta Nijeriya Ta Bukaci A Kara Wa Tinubu Da Gwamoni Albashi
  • Sauyin Gwamnati Zai Yi Sanadin Rasa Guraben Aiki 2,585 A Nijeriya

Sannan, da tsarin bin dokokin shigowa ko fita, kula da wadanda za su zo domin zuba jari da masu kawo ziyara cikin kasa.

ADVERTISEMENT

A kan hakan ne ya misalta jajircewa da kokarin da suke yi a matsayin hanyar da ke kyautata sashin zuba jari a cikin Nijeriya, yana mai cewa jami’ansu sun kware wajen gudanar da aikinsu da ake alfahari da su.

James ya bada misalin yadda suka taka rawa wajen kula da iyakokin kasa lokacin da annobar Korona ya barke a kwanakin baya, ta yadda suka kula da masu shigowa domin tabbatar da wadanda suke dauke da cutar ba su shigo sun yada wa al’ummar Nijeriya ba.

LABARAI MASU NASABA

‘Yansandan Jihohi Za Su Bai Wa Gwamnoni Cikakken Iko Wajen Yaƙi Da Matsalar Tsaro — Gwamna Dauda

Rashin Tsaro: Tinubu Ya Gana Da Shugabannin Hukumomin Tsaro

Ya kuma kara da cewa, hukumarsu ta taimaka wa tawagar sojojin wajen yaki da ‘yan ta’adda a shiyyar Arewa Maso Gabas ta fuskacin kula da wadanda aka yi garkuwa da su, agajin gaggawa ga ‘yan Nijeriya, ceto da aikin tallafi ga wadanda lamarin ya shafa da taimaka wa ‘yan gudun hijira a jihohin da suke Arewa Maso Gabas.

Ta fannin zuba jari kuwa, ya ce, hukumarsu ce ke bada izinin shigowa kasa ga masu son zuba jari, da masu kawo ziyara da tabbatar da tsawon lokacin zamansu ko wa’adi wanda ta hakan ana samun bunkasar tattalin arziki sosai.

Baya ga masu zuba jari da masu kawo ziyarar, ya ce, hukumarsu kuma tana kula da masu zuwa Nijeriya a bangaren kwararru wadanda ake kira domin su yi gyara ko aikin kwaskwarima na wasu muhimman abubuwa a cikin kasar nan.

“Hukumar NIS a karkashin jagorancin Kwanturola Janar, Isa Jere Idris, ta narka jami’ai sosai da suke taimaka wa tawagar jami’an tsaro, wadanda suke iyakokin kasa da filayen jiragen kasa da suke kasar nan, wuraren kula da iyakoki, wuraren sintirin ababen hawa a kokarinmu na tabbatar da dakile masu shigowa ba bisa ka’ida ba da tabbatar da tsaron kasa.”

Ya kara da cewa, sannan, an ware kwararrun jami’ai wadanda suke kula da jihohi a matsayin kwanturololin jihohi domin tabbatar ingancin aiki da tsaron kasa da kula da masu shige da fice da tabbatar da jama’a na bin cikakken ka’idar samun izinin zama ko shigowa Nijeriya a kowani lokaci.

A cewar James, suna kokarin tabbatar da jama’a na samun sauki da ingancin samun iznin shigowa ko zama cikin Nijeriya a kan lokaci, don haka ne ya tabbatar da cewa akwai kyakkawar tsari da suke da shi wajen inganta aiki a kowane lokaci.

NIS
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    ATBU Ta Janye Filin Ginin Masallaci Da Ta Bai wa TIMSAN, Ta Amince Kowa Ya Yi Addininsa Yadda Ya Fahimta
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ɗan Majalisar Dokokin Bauchi, Hon. Wanzam, Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Tsohon Mataimakin Gwamnan Bauchi, Audu Sule Katagum Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Kotu Ta Umarci DSS Ta Mutunta Umarninta Kan Shari’ar Filin Firo Na Bauchi

MASU ALAKA

‘Yansandan Jihohi Za Su Bai Wa Gwamnoni Cikakken Iko Wajen Yaƙi Da Matsalar Tsaro — Gwamna Dauda
Labarai

‘Yansandan Jihohi Za Su Bai Wa Gwamnoni Cikakken Iko Wajen Yaƙi Da Matsalar Tsaro — Gwamna Dauda

July 9, 2026
Rashin Tsaro: Tinubu Ya Gana Da Shugabannin Hukumomin Tsaro
Manyan Labarai

Rashin Tsaro: Tinubu Ya Gana Da Shugabannin Hukumomin Tsaro

July 9, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Ɗaga Albashin Sojoji Daga Naira 49,000 Zuwa Naira 100,000 – Ministan Tsaro
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Ɗaga Albashin Sojoji Daga Naira 49,000 Zuwa Naira 100,000 – Ministan Tsaro

July 9, 2026
Next Post
GORON JUMA’A

GORON JUMA’A

LABARAI MASU NASABA

Asusun IMF Ya Rage Hasashen Bunkasar Tattalin Arzikin Duniya, Ya Kuma Kara Na Sin

Asusun IMF Ya Rage Hasashen Bunkasar Tattalin Arzikin Duniya, Ya Kuma Kara Na Sin

July 9, 2026
Alkaluman Farashin Kayayyakin Masarufi Na Kasar Sin Sun Karu Da Kaso 1 A Watan Yuni

Alkaluman Farashin Kayayyakin Masarufi Na Kasar Sin Sun Karu Da Kaso 1 A Watan Yuni

July 9, 2026
‘Yansandan Jihohi Za Su Bai Wa Gwamnoni Cikakken Iko Wajen Yaƙi Da Matsalar Tsaro — Gwamna Dauda

‘Yansandan Jihohi Za Su Bai Wa Gwamnoni Cikakken Iko Wajen Yaƙi Da Matsalar Tsaro — Gwamna Dauda

July 9, 2026
Taron Intanet Na Sin Karo Na 25 Ya Bayyana Yadda Ake Amfani Da Fasahar AI A Rayuwar Yau Da Kullum

Taron Intanet Na Sin Karo Na 25 Ya Bayyana Yadda Ake Amfani Da Fasahar AI A Rayuwar Yau Da Kullum

July 9, 2026
Tunanin Xi Jinping kan JKS: Hikimar Mulki Ta Farfado Da Kasa Da Kuma Tasirinta A Duniya

Tunanin Xi Jinping kan JKS: Hikimar Mulki Ta Farfado Da Kasa Da Kuma Tasirinta A Duniya

July 9, 2026
Rashin Tsaro: Tinubu Ya Gana Da Shugabannin Hukumomin Tsaro

Rashin Tsaro: Tinubu Ya Gana Da Shugabannin Hukumomin Tsaro

July 9, 2026
Motoci Masu Aiki Da Lantarki Kirar Kasar Sin Na Kara Samun Tagomashi A Kasuwannin Duniya

Motoci Masu Aiki Da Lantarki Kirar Kasar Sin Na Kara Samun Tagomashi A Kasuwannin Duniya

July 9, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Ɗaga Albashin Sojoji Daga Naira 49,000 Zuwa Naira 100,000 – Ministan Tsaro

Gwamnatin Tarayya Ta Ɗaga Albashin Sojoji Daga Naira 49,000 Zuwa Naira 100,000 – Ministan Tsaro

July 9, 2026
An Gabatar Da Shirin Fadar Potala Ta Kafar CMG

An Gabatar Da Shirin Fadar Potala Ta Kafar CMG

July 9, 2026
kebbi

Makarantu Za Su Ci Gaba Da Zama A Rufe Har Sai Yanayin Tsaro Ya Inganta – Gwamnatin Kebbi

July 9, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.