Hukumar Tsaro da Kariya ta Kasa (NSCDC) reshen Jihar Kano ta sallami ma’aikatan sa-kai biyar daga aiki bisa laifukan rashin da’a, rashin kwarewa a aiki da kuma munanan halaye na rashin bin ka’ida.
Ma’aikatan da abin ya shafa sun hada da Yakubu Mubarak Yusuf, Isma’il Muhd, Adamu Auwalu, Abdulrazak Suleiman da Ahmad Sarki.
Jami’in Hulda da Jama’a na rundunar NSCDC a jihar, Ibrahim Abdullahi, ne ya bayyana hakan cikin wata sanarwa da ya fitar ranar Talata.
Sanarwar ta ce Kwamandan NSCDC na Jihar Kano, Mohammed Agalama, ya amince da sallamar bayan an yi cikakken nazari kan laifukan da suka aikata, wadanda aka gano sun saba wa ka’idoji, dabi’u da kuma tsarin gudanar da ayyukan hukumar.
“Kwamandan NSCDC na Jihar Kano, Mohammed Hassan Agalama, ya amince da sallamar ma’aikatan sa-kai guda biyar saboda halayen rashin da’a da suka saba wa kimar hukumar, dabi’un aiki da kuma ka’idojin gudanar da ayyuka,” in ji sanarwar.
Sanarwar ta kara da cewa an kwace dukkan kayan aiki, kayan sawa na hukuma, katunan shaida da sauran kayayyakin da aka ba wadannan ma’aikata domin amfani da su a aikin NSCDC.
Kwamandan ya umarci dukkan kwamandojin yankuna, jami’an rassa da sauran jami’an da abin ya shafa a fadin jihar da su lura da wannan mataki tare da tabbatar da cewa ba a sake amincewa da ko daukar wadannan mutane a matsayin wakilan hukumar ba.
Ya kuma jaddada cewa rundunar ba za ta lamunci rashin da’a ba, yana mai gargadin cewa duk wani jami’i da aka samu da aikata abin da zai bata sunan hukumar zai fuskanci matakan ladabtarwa da suka dace.
“Rundunar NSCDC ta Jihar Kano na ci gaba da jajircewa wajen tabbatar da kwarewa, gaskiya da ingantaccen gudanar da ayyukanta na doka,” in ji sanarwar.














Discussion about this post