Tsohon Ministan Sadarwa da Tattalin Arzikin Zamani, Isa Ali Ibrahim Pantami, ya zama ɗan takarar gwamna na jam’iyyar PDP a jihar Gombe.
Pantami ya samu tikitin jam’iyyar ne ta hanyar amincewar baka daga wakilai yayin zaɓen fidda gwani na gwamna da PDP ta gudanar ranar Talata a Gombe.
Da yake sanar da sakamakon, shugaban kwamitin zaɓen PDP, Gregory Yenlong, ya bayyana Pantami a matsayin wanda ya lashe zaben, yana mai cewa shi ne kadai dan takarar da ya tsaya takara a zaben fidda gwanin.
Da yake jawabi jim kadan bayan bayyana shi a matsayin wanda ya yi nasara, Pantami ya ce shawarar da ya dauka ta tsayawa takarar gwamna ta samo asali ne daga burinsa na yi wa al’ummar jihar Gombe hidima.














Discussion about this post