Tsohon Ministan Sadarwa da Tattalin Arzikin Zamani, Isa Ali Ibrahim Pantami, ya zama ɗan takarar gwamna na jam’iyyar PDP a jihar Gombe.
Pantami ya samu tikitin jam’iyyar ne ta hanyar amincewar baka daga wakilai yayin zaɓen fidda gwani na gwamna da PDP ta gudanar ranar Talata a Gombe.
Da yake sanar da sakamakon, shugaban kwamitin zaɓen PDP, Gregory Yenlong, ya bayyana Pantami a matsayin wanda ya lashe zaben, yana mai cewa shi ne kadai dan takarar da ya tsaya takara a zaben fidda gwanin.
Da yake jawabi jim kadan bayan bayyana shi a matsayin wanda ya yi nasara, Pantami ya ce shawarar da ya dauka ta tsayawa takarar gwamna ta samo asali ne daga burinsa na yi wa al’ummar jihar Gombe hidima.














