Wata ƙungiya mai goyon bayan tsohon Ministan Sadarwa, Isa Ali Ibrahim Pantami, ta yi watsi da abin da ta kira “naɗa ‘yan takara ta hanyar yarjejeniya” da ake zargin an yi a dukkan muƙaman zaɓe a Jihar Gombe.
A cikin wata sanarwa da Farfesa Suleiman Mohammed ya fitar a ranar 3 ga Mayu, 2026, ya ce babu wata ingantacciyar yarjejeniya da za a iya yi ba tare da amincewar dukkan ‘yan takarar da suka sayi fom ɗin nuna sha’awa da na tsayawa takara ba.
Sanarwar ta jaddada cewa dokar zaɓe ta Nijeriya ta 2026 ta tanadi hanyoyi biyu kacal na zaɓen ‘yan takara, wato yarjejeniya ko kuma zaɓen fidda gwani kai tsaye.A cewarta, yarjejeniya tana yiwuwa ne kawai idan dukkan ‘yan takara sun amince a rubuce su janye, idan ba haka ba dole ne jam’iyya ta koma zaɓen fidda gwani kai tsaye.
Ƙungiyar ta zargi matakin da aka ɗauka da saba wa dokar zaɓe da umarnin jam’iyya da kuma jagorancin Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu.Ta kuma buƙaci magoya bayanta su kwantar da hankalinsu su kuma kasance masu bin doka, yayin da ta ce tana shirye-shiryen shiga zaɓen fidda gwani kai tsaye bayan shawo kan matsalolin jam’iyyar APC a jihar.
Sanarwar ta ƙara da cewa tawagar lauyoyinsu na aiki domin duba matakan da suka dace dangane da lamarin.A ƙarshe, ƙungiyar ta yi addu’ar Allah ya albarkaci Jihar Gombe da kuma ƙasar Nijeriya baki ɗaya.















Discussion about this post