Peter Obi, ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar Labour Party a zaɓen 2023, ya yi wata ganawar sirri da gwamnan Jihar Oyo, Seyi Makinde, a ofishin gwamnan da ke Ibadan.
Wannan ganawar ta zo ne ‘yan kwanaki bayan babban taron jam’iyyun adawa da aka gudanar a babban birnin jihar a ƙarshen mako, inda manyan ‘yan siyasa da masu ruwa da tsaki daga sassa daban-daban na ƙasar suka tattauna kan makomar siyasar adawa gabanin zaɓen 2027.
Wasu majiyoyi da ke da masaniya kan lamarin sun bayyana cewa ganawar na daga cikin tattaunawa da ake ci gaba da yi domin ƙarfafa haɗin kan jam’iyyun adawa da kuma duba yiwuwar ƙulla haɗin gwiwa gabanin zaɓuɓɓuka masu zuwa.
Duk da cewa ba a bayyana manufar taron ba zuwa lokacin kammala wannan rahoto, wasu na kusa da lamarin sun ce tattaunawar na da matuƙar muhimmanci wajen tsara mataki na gaba na haɗin kan ‘yan adawa.















Discussion about this post