Tsohon Sanatan Kaduna ta tsakiya, Sanata Shehu Sani, ya bukaci al’ummar Arewacin Nijeriya da su kara bai wa Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu cikakken goyon baya domin ya samu damar kammala sauran shekaru hudu da suka rage masa a wa’adi na biyu.
Shehu Sani, ya bayyana hakan ne yayin da yake zantawa da manema labarai jim kadan bayan kammala sallar Idi a jihar Kaduna . Ya ce kamar yadda al’ummar Arewa suka tsaya tsayin daka wajen bai wa marigayi tsohon shugaban kasa Muhammadu Buhari damar yin mulki na tsawon shekaru takwas, haka ma Shugaba Tinubu ya cancanci irin wannan goyon baya domin ci gaba da jagorantar kasar nan.A cewarsa, gwamnatin APC karkashin jagorancin Tinubu ta kawo sauye-sauye masu anfani a bangarori daban-daban, musamman a fannin tsaro da ayyukan ci gaba da suka shafi rayuwar jama’a.
Tsohon sanatan, wanda kuma shine dan takarar kujerar Sanatan Kaduna ta Tsakiya a karkashin jam’iyyar APC , ya bayyana cewa ya dace al’ummar Arewa su hada kai wajen tabbatar da nasarar jam’iyyar a babban zaben shekarar 2027.
Ya ce duk da cewa a lokacin gwamnatin Buhari manyan mukamai da dama sun kasance a hannun ‘yan Arewa, amma yankin bai samu irin ci gaban da ake tsammani ba, musamman a bangaren tsaro.“Yau idan aka kwatanta da baya, an samu saukin matsalar rashin tsaro a wurare da dama.
Haka kuma gwamnati na aiwatar da muhimman ayyukan raya kasa da jama’a ke anfani da su,” inji Shehu Sani.Ya kuma bayar da misali da jihar Kaduna, inda ya ce a gwamnatin baya an samu korafe-korafe masu yawa kan rushe-rushen gidaje da shagunan jama’a, amma a yanzu karkashin jagorancin Gwamna Uba Sani an samu sauyi domin babu irin wadannan korafe-korafe kamar yadda aka saba gani a baya.A cewarsa, baya ga inganta harkokin tsaro, gwamnatin jihar Kaduna a yanzu na kokarin samar da zaman lafiya da hada kan al’umma domin tabbatar da ci gaba mai dorewa.
Dangane da zabukan fidda gwani na jam’iyyar APC, Shehu Sani ya yi kira ga duk wadanda suka shiga takara amma ba su samu nasara ba da su rungumi sakamakon zaben cikin kwanciyar hankali tare da hada kai domin ci gaban jam’iyyar.
Ya ce samun mulki ko rashin sa yana karkashin ikon Allah, don haka ya kamata ‘ya’yan jam’iyyar su fifita hadin kai da goyon bayan APC domin tabbatar da nasara a zabukan da ke tafe.Shehu Sani ya kara da cewa hadin kai tsakanin shugabanni da magoya baya shi ne zai tabbatar da dorewar mulki da kuma ci gaban Nijeriya baki daya.















Discussion about this post