• English
  • Business News
Thursday, September 18, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ra’ayoyinku A Kan Batun Hako Man Fetur A Yankin Bauchi Da Gombe

by Aisha Seyoji
3 years ago
in Rahotonni
0
Ra’ayoyinku A Kan Batun Hako Man Fetur A Yankin Bauchi Da Gombe
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Wannan makon mun kawo ra’ayoyin masu bibiyar mu a kan kaddamar da fara hakar Man Fetur a yankin jihohin Bauchi da Gombe da Shugaba Buhari ya yi. Ko wannan zai taimaka wajen tsamo al’ummar yankin daga kangin talauci?

Sani Ladan

Masha Allah, wannan babban lamari ne kullum addu’ar mu Allah ya azurta yankin nan namu na arewa da dukiyar da ake mana takama da ita, muna farin ciki kuma muna baiwa shugabanin mu na arewa su dage su sa ido, lallai kada wani abu ya kawo cikas a kan wannan muhimmin aiki, koda Buhari yana jan kafa to ya dace su fizgeshi a guje don ya kammala aikin kafin wa’adinsa na sauka. Allah ya bamu sa a ya taimake mu, mun gode.

Comr Hassan S Umar

Alhamdulillahi, daga karamar Hukumar Minjibir. Wannan batu na hako man fetur a yankin Arewa. Mun dade muna dakon ranar domin idan baki, Mantaba tun kusan lokacin Gwamnatin Dr. Goodluck E Jonathan ake ikirarin gano rijiyoyin Man Fetur musammnan a Jihar Borno, a matsayinmu na yan gwagwarmaya da eman kawo cigaban al’umma, muna murna kuma tunda gwamnatin Shugaba Muhammadu Buhari ta fara ikirarin Man Fetur din musamman jihohin Bauchi da Gombe muke cike da fatan samun haka domin rikicin da ke faruwa a kudu maso gabas din kasarnan. Babbar silarsa shi ne ‘Crude Oil Resources’.

Labarai Masu Nasaba

Yadda Ahlul Faidhati Mai Diwani Group Suka Yi Maulidin Cikar Annabi (SAW) Shekara 1,500 Da Haihuwa 

Abin Fargaba Ne Yadda Bashin Nijeriya Ya Haura Tiriliyan 149 – Shugaban Majalisar Wakilai 

Wanda batu ne me matukar fadi da ba zan iya tafashi awannan shafin ba.

Amma nasan akwai abubuwa a takaice kamar haka

-Tashe Tashen Hankula

-Samun aikin yi

-Makarkashiyar EU

Babu lokacin yin bkyani filla-filla amma abinda ba lallai kinsani ba akwai yankuna da suke da Man Fetur a kasa kamar Kano, Zamfara, Borno, Gombe da Bauchi, akwai sharshi da yawa gaskiya amma a takaice

Wannan ba karamar nasara bace, Allah ya tabbatar.

Amb Ibrahim Adam Dan-Sarauta

Idan har da gaske ne abin zai yi wu to lallai an dauko hanya ta kusa da ke shirin kawo ci gaba a Jihohin Bauchi da Gombe da ma Arewa baki daya.

Irin wannan ayyyukan na gayaran ma’adanan tattalin arizikin Arewa ba tun yanzu ya kamata a ce ana yi ba, domin su ne za su samar da habakar tattalin arzikin na Arewa da kuma magance zaman kashe wando da wasu daga cikin matasan mu suke fama da shi sannan kuma ina mai tabbatar miki da cewa za a rage harkokin ta’addanci.

Domin kashi casa’in na ‘dan ta’adda da suka addabi Arewacin kasar nan talauci ne ya ke jefa su.

Allah ya sa mu dace ya kuma ba da ikon aiwatarwa amin.

 Sulaiman Muhammad

Gaskiya na yi farin ciki sosai da jin wannan labarin domin zai haifar da cigaba sosai ta fannoni da dama

Kabo Idris Saminu

Gaskiya indan da gaske wannan aikin zai tabbata ina sa rai da cewa taulaci da ake fama dashi zai ragu matuka da gaske domin za a samu ayyukan yi, babu zaman banza ya kare.

Wannan ra’ayi nane nagode da daukar sako na. Bissalam.

Zainab Danyaya

Toh Alhamdulillah Allah ya sa ya zame mana alkhairi

Baban Khairat

Wannan labari abin farin ciki ne ga al’umma yankin Arewa, amma inda gizo ke saka shi ne a cikin watanni nawa ne aikin zai kammalu? Ki duba aikin hanyar Abuja zuwa Kano har yanzu ba a gama ba, Allah ya bada Ikon yi abinda ya dace fatanmu kenan,

Yusuf Muhammad Jalingo

Muna matukar farin ciki da wannan yunkuri na shugaban kasa shi dai ya yi nashi saura kuma sanatoci da wanda abin ya shafa su cigaba da bibiyar abubuwan kamar yadda ‘yan kudu suke yi kuma kada susa son zuciya wajen kula da kuma yin aikin. Muna fatan Allah ya sa ya amfani Arewa dama Nijeriya baki daya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: BauchiBuhariGombeMan fetur
ShareTweetSendShare
Previous Post

Abubuwan Da Ake Sa Ran Kwamitin Binciken Kananan Asibitoci Zai Gano

Next Post

Ban Taba Nadamar Shiga Harkar Fim Ba -Hussain Bacci

Related

Ahlul Faidhati Mai Diwani Group
Rahotonni

Yadda Ahlul Faidhati Mai Diwani Group Suka Yi Maulidin Cikar Annabi (SAW) Shekara 1,500 Da Haihuwa 

6 days ago
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace
Rahotonni

Abin Fargaba Ne Yadda Bashin Nijeriya Ya Haura Tiriliyan 149 – Shugaban Majalisar Wakilai 

1 week ago
Arewa
Rahotonni

Matsalar Tsaro: Gwamnonin Arewa Sun Bullo Da Sabbin Matakan Yaki Da Ta’addanci

2 weeks ago
'Yan Bindiga
Rahotonni

Sulhu Da ‘Yan Bindiga Ya Fara Haifar Da Da Mai Ido A Katsina

2 weeks ago
Gidauniyar ‘Ya’yan Sarakunan Arewa Sun Marawa Sarkin Musulmi A Matsayin Shugaban Majalisar Sarakuna
Rahotonni

Babban Taron Lauyoyi Na Kasa: Sarkin Musulmi Ya Gargadi Alkalai Kan Tabbatar Da Adalci

3 weeks ago
Sin Ta Fara Amfani Da Tauraron Dan Adam Wajen Duba Manyan Hanyoyin Wutar Lantarki A Karo Na Farko
Rahotonni

Cire Tallafin Wutar Lantarki Zai Kara Kuntata Rayuwar ‘Yan Nijeriya – Kungiyar Kwadago

3 weeks ago
Next Post
Ban Taba Nadamar Shiga Harkar Fim Ba -Hussain Bacci

Ban Taba Nadamar Shiga Harkar Fim Ba -Hussain Bacci

LABARAI MASU NASABA

Kotun Sojin Nijeriya Ta Yanke Hukuncin Kisa Kan Wani Soja Da Ya Kashe Ɗan Adaidaita

Kotun Sojin Nijeriya Ta Yanke Hukuncin Kisa Kan Wani Soja Da Ya Kashe Ɗan Adaidaita

September 18, 2025
Sashen Raya Kimiyya Da Fasaha Na Sin Ya Kai Babban Matsayi Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-biyar Karo Na 14

Sashen Raya Kimiyya Da Fasaha Na Sin Ya Kai Babban Matsayi Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-biyar Karo Na 14

September 18, 2025
Jose Mourinho Ya Zama Sabon Kocin Benfica

Jose Mourinho Ya Zama Sabon Kocin Benfica

September 18, 2025
An Bude Taron Dandalin Tattauna Batun Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Birnin Beijing

An Bude Taron Dandalin Tattauna Batun Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Birnin Beijing

September 18, 2025
NNPP

Gwamna Yusuf Ya Nuna Jin Daɗinsa Kan Yadda Kano Ta Zarce Legas, Oyo A Sakamakon NECO Na 2025

September 18, 2025
Shugaban Guinea-Bissau Ya Goyi Bayan Shawarar Tsarin Shugabancin Duniya Da Sin Ta Gabatar

Shugaban Guinea-Bissau Ya Goyi Bayan Shawarar Tsarin Shugabancin Duniya Da Sin Ta Gabatar

September 18, 2025
An Damke Basarake Da Wasu Mutum 10 Bisa Zargin Hada Baki Da ‘Yan Bindiga A Kudancin Kaduna

Sojoji Sun Tarwatsa Wata Haramtacciyar Masana’antar Ƙera Makamai A Filato

September 18, 2025
Ci Gaban Tattalin Arzikin Sin Na Taimaka Ga Bunkasa Al’adunta Da Mu’amalar Al’adu Tsakaninta Da Kasashen Duniya

Ci Gaban Tattalin Arzikin Sin Na Taimaka Ga Bunkasa Al’adunta Da Mu’amalar Al’adu Tsakaninta Da Kasashen Duniya

September 18, 2025
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

’Yansanda Sun Kama Sojan Gona Da Motocin Sata 3 A Jigawa

September 18, 2025
Yadda Muka Zama Bayin ‘Yan Bindiga -Mazaunin Wani Kauye

’Yan Bindiga Sun Sako Ma’aurata A Katsina Bayan Karɓar N50m A Matsayin Kuɗin Fansa

September 18, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.