• English
  • Business News
Thursday, June 26, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ra’ayoyinku A Kan Batun Hako Man Fetur A Yankin Bauchi Da Gombe

by Aisha Seyoji
3 years ago
in Rahotonni
0
Ra’ayoyinku A Kan Batun Hako Man Fetur A Yankin Bauchi Da Gombe
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Wannan makon mun kawo ra’ayoyin masu bibiyar mu a kan kaddamar da fara hakar Man Fetur a yankin jihohin Bauchi da Gombe da Shugaba Buhari ya yi. Ko wannan zai taimaka wajen tsamo al’ummar yankin daga kangin talauci?

Sani Ladan

Masha Allah, wannan babban lamari ne kullum addu’ar mu Allah ya azurta yankin nan namu na arewa da dukiyar da ake mana takama da ita, muna farin ciki kuma muna baiwa shugabanin mu na arewa su dage su sa ido, lallai kada wani abu ya kawo cikas a kan wannan muhimmin aiki, koda Buhari yana jan kafa to ya dace su fizgeshi a guje don ya kammala aikin kafin wa’adinsa na sauka. Allah ya bamu sa a ya taimake mu, mun gode.

Comr Hassan S Umar

Alhamdulillahi, daga karamar Hukumar Minjibir. Wannan batu na hako man fetur a yankin Arewa. Mun dade muna dakon ranar domin idan baki, Mantaba tun kusan lokacin Gwamnatin Dr. Goodluck E Jonathan ake ikirarin gano rijiyoyin Man Fetur musammnan a Jihar Borno, a matsayinmu na yan gwagwarmaya da eman kawo cigaban al’umma, muna murna kuma tunda gwamnatin Shugaba Muhammadu Buhari ta fara ikirarin Man Fetur din musamman jihohin Bauchi da Gombe muke cike da fatan samun haka domin rikicin da ke faruwa a kudu maso gabas din kasarnan. Babbar silarsa shi ne ‘Crude Oil Resources’.

Labarai Masu Nasaba

Sarkakiyar Da Ke Tattare Da Zaben 2027 Da Yadda Za Ta Kaya

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

Wanda batu ne me matukar fadi da ba zan iya tafashi awannan shafin ba.

Amma nasan akwai abubuwa a takaice kamar haka

-Tashe Tashen Hankula

-Samun aikin yi

-Makarkashiyar EU

Babu lokacin yin bkyani filla-filla amma abinda ba lallai kinsani ba akwai yankuna da suke da Man Fetur a kasa kamar Kano, Zamfara, Borno, Gombe da Bauchi, akwai sharshi da yawa gaskiya amma a takaice

Wannan ba karamar nasara bace, Allah ya tabbatar.

Amb Ibrahim Adam Dan-Sarauta

Idan har da gaske ne abin zai yi wu to lallai an dauko hanya ta kusa da ke shirin kawo ci gaba a Jihohin Bauchi da Gombe da ma Arewa baki daya.

Irin wannan ayyyukan na gayaran ma’adanan tattalin arizikin Arewa ba tun yanzu ya kamata a ce ana yi ba, domin su ne za su samar da habakar tattalin arzikin na Arewa da kuma magance zaman kashe wando da wasu daga cikin matasan mu suke fama da shi sannan kuma ina mai tabbatar miki da cewa za a rage harkokin ta’addanci.

Domin kashi casa’in na ‘dan ta’adda da suka addabi Arewacin kasar nan talauci ne ya ke jefa su.

Allah ya sa mu dace ya kuma ba da ikon aiwatarwa amin.

 Sulaiman Muhammad

Gaskiya na yi farin ciki sosai da jin wannan labarin domin zai haifar da cigaba sosai ta fannoni da dama

Kabo Idris Saminu

Gaskiya indan da gaske wannan aikin zai tabbata ina sa rai da cewa taulaci da ake fama dashi zai ragu matuka da gaske domin za a samu ayyukan yi, babu zaman banza ya kare.

Wannan ra’ayi nane nagode da daukar sako na. Bissalam.

Zainab Danyaya

Toh Alhamdulillah Allah ya sa ya zame mana alkhairi

Baban Khairat

Wannan labari abin farin ciki ne ga al’umma yankin Arewa, amma inda gizo ke saka shi ne a cikin watanni nawa ne aikin zai kammalu? Ki duba aikin hanyar Abuja zuwa Kano har yanzu ba a gama ba, Allah ya bada Ikon yi abinda ya dace fatanmu kenan,

Yusuf Muhammad Jalingo

Muna matukar farin ciki da wannan yunkuri na shugaban kasa shi dai ya yi nashi saura kuma sanatoci da wanda abin ya shafa su cigaba da bibiyar abubuwan kamar yadda ‘yan kudu suke yi kuma kada susa son zuciya wajen kula da kuma yin aikin. Muna fatan Allah ya sa ya amfani Arewa dama Nijeriya baki daya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: BauchiBuhariGombeMan fetur
ShareTweetSendShare
Previous Post

Abubuwan Da Ake Sa Ran Kwamitin Binciken Kananan Asibitoci Zai Gano

Next Post

Ban Taba Nadamar Shiga Harkar Fim Ba -Hussain Bacci

Related

jam'iyyu
Rahotonni

Sarkakiyar Da Ke Tattare Da Zaben 2027 Da Yadda Za Ta Kaya

2 weeks ago
Man Fetur
Rahotonni

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

3 weeks ago
Tsadar Rayuwa: Yadda Al’umma Suka Yi Sallah Cikin Kunci
Rahotonni

Tsadar Rayuwa: Yadda Al’umma Suka Yi Sallah Cikin Kunci

3 weeks ago
Ana Fargabar Boko Haram Ta Kara Mamaye Wasu Kananan Hukumomi A Borno
Rahotonni

Ana Fargabar Boko Haram Ta Kara Mamaye Wasu Kananan Hukumomi A Borno

4 weeks ago
Kokarin Minista Tuggar Na Mayar Da Hijirar Masana Daga Nijeriya Zuwa Kasashen Waje Alhairi
Rahotonni

Kokarin Minista Tuggar Na Mayar Da Hijirar Masana Daga Nijeriya Zuwa Kasashen Waje Alhairi

4 weeks ago
Faduwar Jarrabawar JAMB Ta Tayar Da Bukatar Neman Sake Fasalin Hukumar
Rahotonni

Faduwar Jarrabawar JAMB Ta Tayar Da Bukatar Neman Sake Fasalin Hukumar

1 month ago
Next Post
Ban Taba Nadamar Shiga Harkar Fim Ba -Hussain Bacci

Ban Taba Nadamar Shiga Harkar Fim Ba -Hussain Bacci

LABARAI MASU NASABA

Kashim Shettima Ya Tafi Habasha Ziyarar Aiki

Kashim Shettima Ya Tafi Habasha Ziyarar Aiki

June 26, 2025
Afirka CDC Ta Yaba Da Hadin Gwiwa Kan Kiwon Lafiya Da Kasar Sin

Afirka CDC Ta Yaba Da Hadin Gwiwa Kan Kiwon Lafiya Da Kasar Sin

June 26, 2025
Sabbin Dokokin Haraji Za Su Fara Aiki A Janairun 2026 — Adedeji

Sabbin Dokokin Haraji Za Su Fara Aiki A Janairun 2026 — Adedeji

June 26, 2025
An Watsa Shirin Talabijin Mai Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” A Italiya

An Watsa Shirin Talabijin Mai Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” A Italiya

June 26, 2025
Wannan Imanin Ne Ya Kai Likitocin Sin Nahiyar Afirka…

Wannan Imanin Ne Ya Kai Likitocin Sin Nahiyar Afirka…

June 26, 2025
Jami’an Tsaro Sun Kashe Mayaƙan Bello Turji Da Yawa A Zamfara

Jami’an Tsaro Sun Kashe Mayaƙan Bello Turji Da Yawa A Zamfara

June 26, 2025
Sanatan Neja Ta Arewa Ya Yi Allah Wadai Da Kashe Sojoji A Mariga

Sanatan Neja Ta Arewa Ya Yi Allah Wadai Da Kashe Sojoji A Mariga

June 26, 2025
Kawayen amarya

Da Ɗumi-ɗumi: ‘Yan Bindiga Sun Ƙwace Iko Da Jagorancin Ƙaramar Hukuma A Katsina

June 26, 2025
An Damke Basarake Da Wasu Mutum 10 Bisa Zargin Hada Baki Da ‘Yan Bindiga A Kudancin Kaduna

Musayar Wuta Tsakanin Sojoji Da ‘Yan Bindiga Ta Ci Rayuka Da Dama A Jihar Neja

June 26, 2025
Tinubu

Tinubu Zai Rattaba Hannu Kan Kudirorin Sauya Fasalin Haraji 4 A Yau Alhamis 

June 26, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.