• English
  • Business News
Tuesday, September 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ra’ayoyinku A Kan Batun Hako Man Fetur A Yankin Bauchi Da Gombe

by Aisha Seyoji
3 years ago
in Rahotonni
0
Ra’ayoyinku A Kan Batun Hako Man Fetur A Yankin Bauchi Da Gombe
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Wannan makon mun kawo ra’ayoyin masu bibiyar mu a kan kaddamar da fara hakar Man Fetur a yankin jihohin Bauchi da Gombe da Shugaba Buhari ya yi. Ko wannan zai taimaka wajen tsamo al’ummar yankin daga kangin talauci?

Sani Ladan

Masha Allah, wannan babban lamari ne kullum addu’ar mu Allah ya azurta yankin nan namu na arewa da dukiyar da ake mana takama da ita, muna farin ciki kuma muna baiwa shugabanin mu na arewa su dage su sa ido, lallai kada wani abu ya kawo cikas a kan wannan muhimmin aiki, koda Buhari yana jan kafa to ya dace su fizgeshi a guje don ya kammala aikin kafin wa’adinsa na sauka. Allah ya bamu sa a ya taimake mu, mun gode.

Comr Hassan S Umar

Alhamdulillahi, daga karamar Hukumar Minjibir. Wannan batu na hako man fetur a yankin Arewa. Mun dade muna dakon ranar domin idan baki, Mantaba tun kusan lokacin Gwamnatin Dr. Goodluck E Jonathan ake ikirarin gano rijiyoyin Man Fetur musammnan a Jihar Borno, a matsayinmu na yan gwagwarmaya da eman kawo cigaban al’umma, muna murna kuma tunda gwamnatin Shugaba Muhammadu Buhari ta fara ikirarin Man Fetur din musamman jihohin Bauchi da Gombe muke cike da fatan samun haka domin rikicin da ke faruwa a kudu maso gabas din kasarnan. Babbar silarsa shi ne ‘Crude Oil Resources’.

Labarai Masu Nasaba

Abin Fargaba Ne Yadda Bashin Nijeriya Ya Haura Tiriliyan 149 – Shugaban Majalisar Wakilai 

Matsalar Tsaro: Gwamnonin Arewa Sun Bullo Da Sabbin Matakan Yaki Da Ta’addanci

Wanda batu ne me matukar fadi da ba zan iya tafashi awannan shafin ba.

Amma nasan akwai abubuwa a takaice kamar haka

-Tashe Tashen Hankula

-Samun aikin yi

-Makarkashiyar EU

Babu lokacin yin bkyani filla-filla amma abinda ba lallai kinsani ba akwai yankuna da suke da Man Fetur a kasa kamar Kano, Zamfara, Borno, Gombe da Bauchi, akwai sharshi da yawa gaskiya amma a takaice

Wannan ba karamar nasara bace, Allah ya tabbatar.

Amb Ibrahim Adam Dan-Sarauta

Idan har da gaske ne abin zai yi wu to lallai an dauko hanya ta kusa da ke shirin kawo ci gaba a Jihohin Bauchi da Gombe da ma Arewa baki daya.

Irin wannan ayyyukan na gayaran ma’adanan tattalin arizikin Arewa ba tun yanzu ya kamata a ce ana yi ba, domin su ne za su samar da habakar tattalin arzikin na Arewa da kuma magance zaman kashe wando da wasu daga cikin matasan mu suke fama da shi sannan kuma ina mai tabbatar miki da cewa za a rage harkokin ta’addanci.

Domin kashi casa’in na ‘dan ta’adda da suka addabi Arewacin kasar nan talauci ne ya ke jefa su.

Allah ya sa mu dace ya kuma ba da ikon aiwatarwa amin.

 Sulaiman Muhammad

Gaskiya na yi farin ciki sosai da jin wannan labarin domin zai haifar da cigaba sosai ta fannoni da dama

Kabo Idris Saminu

Gaskiya indan da gaske wannan aikin zai tabbata ina sa rai da cewa taulaci da ake fama dashi zai ragu matuka da gaske domin za a samu ayyukan yi, babu zaman banza ya kare.

Wannan ra’ayi nane nagode da daukar sako na. Bissalam.

Zainab Danyaya

Toh Alhamdulillah Allah ya sa ya zame mana alkhairi

Baban Khairat

Wannan labari abin farin ciki ne ga al’umma yankin Arewa, amma inda gizo ke saka shi ne a cikin watanni nawa ne aikin zai kammalu? Ki duba aikin hanyar Abuja zuwa Kano har yanzu ba a gama ba, Allah ya bada Ikon yi abinda ya dace fatanmu kenan,

Yusuf Muhammad Jalingo

Muna matukar farin ciki da wannan yunkuri na shugaban kasa shi dai ya yi nashi saura kuma sanatoci da wanda abin ya shafa su cigaba da bibiyar abubuwan kamar yadda ‘yan kudu suke yi kuma kada susa son zuciya wajen kula da kuma yin aikin. Muna fatan Allah ya sa ya amfani Arewa dama Nijeriya baki daya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: BauchiBuhariGombeMan fetur
ShareTweetSendShare
Previous Post

Abubuwan Da Ake Sa Ran Kwamitin Binciken Kananan Asibitoci Zai Gano

Next Post

Ban Taba Nadamar Shiga Harkar Fim Ba -Hussain Bacci

Related

Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace
Rahotonni

Abin Fargaba Ne Yadda Bashin Nijeriya Ya Haura Tiriliyan 149 – Shugaban Majalisar Wakilai 

9 hours ago
Arewa
Rahotonni

Matsalar Tsaro: Gwamnonin Arewa Sun Bullo Da Sabbin Matakan Yaki Da Ta’addanci

2 days ago
'Yan Bindiga
Rahotonni

Sulhu Da ‘Yan Bindiga Ya Fara Haifar Da Da Mai Ido A Katsina

3 days ago
Gidauniyar ‘Ya’yan Sarakunan Arewa Sun Marawa Sarkin Musulmi A Matsayin Shugaban Majalisar Sarakuna
Rahotonni

Babban Taron Lauyoyi Na Kasa: Sarkin Musulmi Ya Gargadi Alkalai Kan Tabbatar Da Adalci

1 week ago
Sin Ta Fara Amfani Da Tauraron Dan Adam Wajen Duba Manyan Hanyoyin Wutar Lantarki A Karo Na Farko
Rahotonni

Cire Tallafin Wutar Lantarki Zai Kara Kuntata Rayuwar ‘Yan Nijeriya – Kungiyar Kwadago

1 week ago
Akwai Bukatar Gwamnonin Arewa Su Yi Koyi Da Jihar Legas Wajen Bunkasa Albarkatun Fatu
Rahotonni

Akwai Bukatar Gwamnonin Arewa Su Yi Koyi Da Jihar Legas Wajen Bunkasa Albarkatun Fatu

1 week ago
Next Post
Ban Taba Nadamar Shiga Harkar Fim Ba -Hussain Bacci

Ban Taba Nadamar Shiga Harkar Fim Ba -Hussain Bacci

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Ta Zama Wurin Da Aka Fi Zaba Domin Warware Takaddamar Cinikayya Da Ta Shafi Kasa Da Kasa

Kasar Sin Ta Zama Wurin Da Aka Fi Zaba Domin Warware Takaddamar Cinikayya Da Ta Shafi Kasa Da Kasa

September 8, 2025
Sojoji

Sojoji Sun Kai Hare-hare 261, ‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 1,950 A Watan Agusta – NOA

September 8, 2025
Kasar Sin Ta Bayar Da Gaggarumar Gudunmuwa Ga Wanzuwar Zaman Lafiya Da Ci Gaba Mai Dorewa A Duniya

Kasar Sin Ta Bayar Da Gaggarumar Gudunmuwa Ga Wanzuwar Zaman Lafiya Da Ci Gaba Mai Dorewa A Duniya

September 8, 2025
'yansanda

An Kama Mutane 30 Da Zargin Laifin Aikin Dabanci A Yayin Zagayen Maulidi A Neja

September 8, 2025
Xi Jinping Ya Aika Da Sakon Taya Murnar Bude Taron Cifit Karo Na 25

Xi Jinping Ya Aika Da Sakon Taya Murnar Bude Taron Cifit Karo Na 25

September 8, 2025
Gwamnatin Tarayya, NUPENG Da Ɗangote Sun Fara Tattaunawa Don Kawo Ƙarshen Yajin Aikin Ma’aikatan Mai

Gwamnatin Tarayya, NUPENG Da Ɗangote Sun Fara Tattaunawa Don Kawo Ƙarshen Yajin Aikin Ma’aikatan Mai

September 8, 2025
Sin Ta Gabatar Da Sabon Injin Aiki A Manyan Na’urori Mai Amfani Da Iskar Gas Kirar Gida

Sin Ta Gabatar Da Sabon Injin Aiki A Manyan Na’urori Mai Amfani Da Iskar Gas Kirar Gida

September 8, 2025
Man Fetur

Jarin Da Sin Ta Zuba Kai Tsaye A Kasashe Cikin Shawarar Ziri Daya Da Hanya Daya Ya Karu Da Kashi 22.9% A 2024

September 8, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace

Abin Fargaba Ne Yadda Bashin Nijeriya Ya Haura Tiriliyan 149 – Shugaban Majalisar Wakilai 

September 8, 2025
Adadin Kamfanonin AI A Sin Sun Haura 5,000

Adadin Kamfanonin AI A Sin Sun Haura 5,000

September 8, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.