ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ramadan: Coci Ta Raba Kayan Abinci Ga Makarantun Tsangaya A Kaduna

by Bello Hamza and Sulaiman
4 months ago
Buru

Cocin Evangelica da ke Sabon Tasha, Kaduna, ta raba buhunhunan shinkafa, masara da sauran kayan abinci ga Musulmai, makarantun Islamiyya na Tsangaya da kuma wasu mutane da suka rasa matsugunansu (IDPs), kafin azumin Ramadana.

Babban Limamin cocin, Yohanna Buru, wanda ya jagoranci rabon kayan a masallacin Kano Road da ke Kaduna, ya ce; an yi hakan ne domin inganta zaman lafiya da kuma karfafa jituwa a tsakanin addinai daban-daban a fadin jihar.

  • Neymar Na Duba Yiwuwar Ritaya Daga Ƙwallon Ƙafa A Ƙarshen Shekara
  • Sin Ta Ba Da Shawarar Tsayawa Kan Ra’ayoyin Bai Daya Guda Biyar Don Warware Rikicin Sudan

Buru ya ce, cocin kusan tsawon shekaru 20 da suka gabata, ta tallafa wa Musulmai marasa galihu da makarantun Tsangaya a jihohi biyar na Arewa da kayayyakin abinci, domin ba su damar gudanar da azumin watan Ramadana na kwana 30 a cikin sauki.

ADVERTISEMENT

Ya kara da cewa, baya ga shinkafa da masara, cocin tana kuma samar da tabarmun sallah da butoci a kowace shekara, inda yake kira ga wadanda suka amfana da kayayyakin da su yi amfani da lokacin wajen addu’ar neman zaman lafiya, kwanciyar hankali da kuma kawo karshen rashin tsaro da wahalhalun tattalin arziki a kasar.

“Yayin da farashin kayayyaki ke ci gaba da hauhawa, mun tattara fastoci da limamai kimanin 50 masu aikin sa kai, domin yin wani gangamin wayar da kan jama’a na tsawon kwana bakwai, don karfafa ‘yan kasuwa su rage farashin kayayyakin abinci a lokacin na Ramadana,” in ji shi.

LABARAI MASU NASABA

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

Ya kara da cewa, cocin yana kuma taimakawa wajen fitar da wasu fursunoni Musulmai a kowace shekara, domin ba su damar yin azumin Ramadana tare da iyalansu.

Haka zalika, Buru ya yaba da goyon bayan wata mai taimakon jama’a Musulmai, Hajiya Ramatu Tijjani, wacce ke ba da gudummawa ga zawarawa da marayu a lokacin bukukuwan kirsimeti da dabuwar shekara, yana mai bayyana wannan a matsayin nuna girmamawa tsakanin addinai.

Ya yi wa Musulmai fatan alheri a watan Ramadana mai cike da zaman lafiya, sannan kuma ya yi kira da a yi addu’o’i don, hadin kai a kasar baki-daya.

A cikin jawabinsa, shugaban kungiyar nakasassu a Jihar Kaduna, Mallam Hassan Lawal, ya yaba wa cocin bisa wannan tallafi, yana mai kira ga sauran Musulmai masu hannu da shuni, da su taimaki marasa galihu a wannan lokaci na Azumi.

Ramadan
Bello Hamza
+ posts Bio
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Hijira 1448:Za A Samu Yalwar Tattalin Arziƙi A Nijeriya —Sheikh Muhajjadina
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    NPA Ta Samar Da Tashoshin Jiragen Ruwan Da Za Su Ƙarfafa Kasuwanci Da Ƙasashen Duniya – Dantsoho
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Gwanjon Kadarori: Kotun Daukaka Kara Ta Kori Karar Da Sani Sha’aban Ya Shigar
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Amfani Da Matar Soja Wajen Isar Da Sakon Bukata
Ramadan
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu
  • Sulaiman
    Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani
  • Sulaiman
    Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100
  • Sulaiman
    Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

MASU ALAKA

‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba
Labarai

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

June 24, 2026
An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi
Labarai

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

June 24, 2026
Next Post
Darussa Daga Ramadan Na (1)

Darussa Daga Ramadan Na (3)

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

June 24, 2026
An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

June 24, 2026
Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

June 24, 2026
Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

June 23, 2026
Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

June 23, 2026
Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

June 23, 2026
Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

June 23, 2026
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

’Yansanda Sun Kama Mutane 57 Da Ake Zargi Da Ayyukan Ta’addanci A Adamawa

June 23, 2026
Li Qiang Ya Gana Da Firaministan Kasar Guinea

Li Qiang Ya Gana Da Firaministan Kasar Guinea

June 23, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.