ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ramadan: Kamfanin Indomie Ya Shirya Shan Ruwa A Gidajen Kwastomominsa A Kaduna

by Leadership Hausa
3 months ago
Ramadan

Kamfanin taliyar Indomie ya shirya wani taron shan ruwa na musamman a Jihar Kaduna domin karrama mutanen da suka yi nasara a gasar tambayoyin Ramadan da aka gudanar ta gidajen rediyo a jihar, kamar yadda ake yi a jihohin Kano da Sakkwato, tare da ƙara ƙarfafa alaƙa da al’umma a wannan wata mai alfarma.

Shirin na daga cikin shirye-shiryen da kamfanin ya tsara domin samar da farin ciki a lokacin buɗa-baki tare da kwastomominsa da suka halarci gasar amsa tambayoyin da aka gabatar a gidajen rediyo a lokacin watan Ramadan.

  • Indomie Ta Taka Muhimmiyar Rawa Wajen Raya Al’adu A Bikin Kamun Kifi Na Argungu Karo Na 61
  • NAFDAC Ta Haramta Shigo Da Indomie Saboda Zargin Sanya Ciwon Daji

Nura Yusuf Muhammad da Maryam Husaini ne suka zama zakarun gasar tambayoyin a Jihar Kaduna, bayan sun nuna ƙwarewa wajen amsa tambayoyin da aka gabatar a shirin.

ADVERTISEMENT

Domin murnar wannan nasara tasu, Indomie ta shirya wani taron shan ruwa na musamman a Unguwar Millennium City da ke jihar, inda waɗanda suka yi nasara tare da iyalansu da sauran al’ummar yankin suka taru domin buɗa-baki tare da Indomie.

Taron ya samar da yanayi na farin ciki da annashuwa ga mahalarta, inda aka raba abinci da kuma kyaututtuka a lokacin buɗa-baki.

LABARAI MASU NASABA

Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

A yayin taron, waɗanda suka yi nasara sun bayyana farin cikinsu tare da nuna godiya ga kamfanin Indomie bisa wannan karramawa da aka yi musu. Sun ce shirin ya ƙara sanya musu farin ciki a watan Ramadan tare da ba su damar yin buɗa-baki tare da iyalansu da maƙwabta cikin annashuwa.

Ɗaya daga cikin waɗanda suka yi nasara ya bayyana cewa wannan kyakkyawan shiri ya sa watan Ramadan ya zama abin tunawa a gare su, tare da ƙarfafa zumunci da haɗin kai a tsakanin al’umma.

Wasu daga cikin mahalarta taron sun yaba da wannan shiri, inda suka ce irin wannan ɗawainiya ta kamfanoni masu zaman kansu irin Indomie na taimakawa wajen ƙarfafa zumunci da haɗin kai da taimakon juna a tsakanin al’umma a wannan lokaci na Ramadan.

Da yake jawabi a wajen taron, wakilin kamfanin Indomie, Gabriel Ajeh, ya ce wannan shiri wani ɓangare ne na ƙoƙarin kamfanin na kusantar al’umma tare da karrama waɗanda suka halarci gasar tambayoyin Ramadan.

Ya ƙara da cewa karrama waɗanda suka yi nasara a irin wannan taro na shan ruwa na taimakawa wajen sanya shirin ya zama abin tunawa, tare da ƙarfafa alaƙa tsakanin kamfanin da kwastomominsa.

Har ila yau, kamfanin Indomie ya faɗaɗa damar shiga gasar ta hanyar shafukansa na sada-zumunta na yanar gizo mai suna Indomie Arewa, inda ake wallafa tambayoyi a kowace rana domin bai wa waɗanda ba su samu damar sauraron shirin rediyo ba damar shiga gasar.

Mutanen da suka amsa tambayoyin daidai a waɗannan shafuka na sada-zumunta suna samun kyautar kwalin taliyar Indomie domin taimaka wa iyalai a wannan lokaci na watan Ramadan.

Kamfanin ya bayyana cewa wannan shiri na nuna ƙudurinsa na tallafa wa al’umma da kuma samar da farin ciki a tsakanin jama’a a watan Ramadan mai alfarma.

Ramadan
Leadership Hausa
Website |  + postsBio
  • Leadership Hausa
    Batun Dakile Shan Taba Sigari A Tsakanin Yara A Nijeriya
  • Leadership Hausa
    Har Yanzu Akwai Sauran Rina A Kaba Game Da Makomar Yara A Nijeriya
  • Leadership Hausa
    Yadda Arsenal Ta Lashe Gasar Firimiya Bayan Shekara 22
  • Leadership Hausa
    Bukatar Kawo Karshen Akidar Kyamar Baki A Kasar Afirka Ta Kudu

MASU ALAKA

Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi
Manyan Labarai

Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

June 25, 2026
EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53
Manyan Labarai

EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

June 25, 2026
Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya
Labarai

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

June 25, 2026
Next Post
Hobbasar Gwamna Abba Kan Titunan Birnin Kano

Hobbasar Gwamna Abba Kan Titunan Birnin Kano

LABARAI MASU NASABA

Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

June 25, 2026
EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

June 25, 2026
Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

June 25, 2026
Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa — Atiku

June 25, 2026
Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.