ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ramadan: Kamfanin Indomie Ya Shirya Shan Ruwa A Gidajen Kwastomominsa A Kaduna

by Leadership Hausa
4 months ago
Ramadan

Kamfanin taliyar Indomie ya shirya wani taron shan ruwa na musamman a Jihar Kaduna domin karrama mutanen da suka yi nasara a gasar tambayoyin Ramadan da aka gudanar ta gidajen rediyo a jihar, kamar yadda ake yi a jihohin Kano da Sakkwato, tare da ƙara ƙarfafa alaƙa da al’umma a wannan wata mai alfarma.

Shirin na daga cikin shirye-shiryen da kamfanin ya tsara domin samar da farin ciki a lokacin buɗa-baki tare da kwastomominsa da suka halarci gasar amsa tambayoyin da aka gabatar a gidajen rediyo a lokacin watan Ramadan.

  • Indomie Ta Taka Muhimmiyar Rawa Wajen Raya Al’adu A Bikin Kamun Kifi Na Argungu Karo Na 61
  • NAFDAC Ta Haramta Shigo Da Indomie Saboda Zargin Sanya Ciwon Daji

Nura Yusuf Muhammad da Maryam Husaini ne suka zama zakarun gasar tambayoyin a Jihar Kaduna, bayan sun nuna ƙwarewa wajen amsa tambayoyin da aka gabatar a shirin.

ADVERTISEMENT

Domin murnar wannan nasara tasu, Indomie ta shirya wani taron shan ruwa na musamman a Unguwar Millennium City da ke jihar, inda waɗanda suka yi nasara tare da iyalansu da sauran al’ummar yankin suka taru domin buɗa-baki tare da Indomie.

Taron ya samar da yanayi na farin ciki da annashuwa ga mahalarta, inda aka raba abinci da kuma kyaututtuka a lokacin buɗa-baki.

LABARAI MASU NASABA

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

A yayin taron, waɗanda suka yi nasara sun bayyana farin cikinsu tare da nuna godiya ga kamfanin Indomie bisa wannan karramawa da aka yi musu. Sun ce shirin ya ƙara sanya musu farin ciki a watan Ramadan tare da ba su damar yin buɗa-baki tare da iyalansu da maƙwabta cikin annashuwa.

Ɗaya daga cikin waɗanda suka yi nasara ya bayyana cewa wannan kyakkyawan shiri ya sa watan Ramadan ya zama abin tunawa a gare su, tare da ƙarfafa zumunci da haɗin kai a tsakanin al’umma.

Wasu daga cikin mahalarta taron sun yaba da wannan shiri, inda suka ce irin wannan ɗawainiya ta kamfanoni masu zaman kansu irin Indomie na taimakawa wajen ƙarfafa zumunci da haɗin kai da taimakon juna a tsakanin al’umma a wannan lokaci na Ramadan.

Da yake jawabi a wajen taron, wakilin kamfanin Indomie, Gabriel Ajeh, ya ce wannan shiri wani ɓangare ne na ƙoƙarin kamfanin na kusantar al’umma tare da karrama waɗanda suka halarci gasar tambayoyin Ramadan.

Ya ƙara da cewa karrama waɗanda suka yi nasara a irin wannan taro na shan ruwa na taimakawa wajen sanya shirin ya zama abin tunawa, tare da ƙarfafa alaƙa tsakanin kamfanin da kwastomominsa.

Har ila yau, kamfanin Indomie ya faɗaɗa damar shiga gasar ta hanyar shafukansa na sada-zumunta na yanar gizo mai suna Indomie Arewa, inda ake wallafa tambayoyi a kowace rana domin bai wa waɗanda ba su samu damar sauraron shirin rediyo ba damar shiga gasar.

Mutanen da suka amsa tambayoyin daidai a waɗannan shafuka na sada-zumunta suna samun kyautar kwalin taliyar Indomie domin taimaka wa iyalai a wannan lokaci na watan Ramadan.

Kamfanin ya bayyana cewa wannan shiri na nuna ƙudurinsa na tallafa wa al’umma da kuma samar da farin ciki a tsakanin jama’a a watan Ramadan mai alfarma.

Ramadan
Leadership Hausa
Website |  + postsBio
  • Leadership Hausa
    Tallafa Wa Yara Masu Buƙatu Na Musamman Shi Ne Burina
  • Leadership Hausa
    Dole Mata Su Rungumi Sana’o’i Domin Tsira Daga Takaicin Zamani —Ramatu Bello
  • Leadership Hausa
    Batun Dakile Shan Taba Sigari A Tsakanin Yara A Nijeriya
  • Leadership Hausa
    Har Yanzu Akwai Sauran Rina A Kaba Game Da Makomar Yara A Nijeriya

MASU ALAKA

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya
Manyan Labarai

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

July 15, 2026
Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221
Labarai

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi
Labarai

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

July 15, 2026
Next Post
Hobbasar Gwamna Abba Kan Titunan Birnin Kano

Hobbasar Gwamna Abba Kan Titunan Birnin Kano

LABARAI MASU NASABA

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

July 15, 2026
Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

July 15, 2026
Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.