ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ramadan: Kamfanin Indomie Ya Shirya Shan Ruwa A Gidajen Kwastomominsa A Kaduna

by Leadership Hausa
6 months ago
Ramadan

Kamfanin taliyar Indomie ya shirya wani taron shan ruwa na musamman a Jihar Kaduna domin karrama mutanen da suka yi nasara a gasar tambayoyin Ramadan da aka gudanar ta gidajen rediyo a jihar, kamar yadda ake yi a jihohin Kano da Sakkwato, tare da ƙara ƙarfafa alaƙa da al’umma a wannan wata mai alfarma.

Shirin na daga cikin shirye-shiryen da kamfanin ya tsara domin samar da farin ciki a lokacin buɗa-baki tare da kwastomominsa da suka halarci gasar amsa tambayoyin da aka gabatar a gidajen rediyo a lokacin watan Ramadan.

  • Indomie Ta Taka Muhimmiyar Rawa Wajen Raya Al’adu A Bikin Kamun Kifi Na Argungu Karo Na 61
  • NAFDAC Ta Haramta Shigo Da Indomie Saboda Zargin Sanya Ciwon Daji

Nura Yusuf Muhammad da Maryam Husaini ne suka zama zakarun gasar tambayoyin a Jihar Kaduna, bayan sun nuna ƙwarewa wajen amsa tambayoyin da aka gabatar a shirin.

ADVERTISEMENT

Domin murnar wannan nasara tasu, Indomie ta shirya wani taron shan ruwa na musamman a Unguwar Millennium City da ke jihar, inda waɗanda suka yi nasara tare da iyalansu da sauran al’ummar yankin suka taru domin buɗa-baki tare da Indomie.

Taron ya samar da yanayi na farin ciki da annashuwa ga mahalarta, inda aka raba abinci da kuma kyaututtuka a lokacin buɗa-baki.

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

A yayin taron, waɗanda suka yi nasara sun bayyana farin cikinsu tare da nuna godiya ga kamfanin Indomie bisa wannan karramawa da aka yi musu. Sun ce shirin ya ƙara sanya musu farin ciki a watan Ramadan tare da ba su damar yin buɗa-baki tare da iyalansu da maƙwabta cikin annashuwa.

Ɗaya daga cikin waɗanda suka yi nasara ya bayyana cewa wannan kyakkyawan shiri ya sa watan Ramadan ya zama abin tunawa a gare su, tare da ƙarfafa zumunci da haɗin kai a tsakanin al’umma.

Wasu daga cikin mahalarta taron sun yaba da wannan shiri, inda suka ce irin wannan ɗawainiya ta kamfanoni masu zaman kansu irin Indomie na taimakawa wajen ƙarfafa zumunci da haɗin kai da taimakon juna a tsakanin al’umma a wannan lokaci na Ramadan.

Da yake jawabi a wajen taron, wakilin kamfanin Indomie, Gabriel Ajeh, ya ce wannan shiri wani ɓangare ne na ƙoƙarin kamfanin na kusantar al’umma tare da karrama waɗanda suka halarci gasar tambayoyin Ramadan.

Ya ƙara da cewa karrama waɗanda suka yi nasara a irin wannan taro na shan ruwa na taimakawa wajen sanya shirin ya zama abin tunawa, tare da ƙarfafa alaƙa tsakanin kamfanin da kwastomominsa.

Har ila yau, kamfanin Indomie ya faɗaɗa damar shiga gasar ta hanyar shafukansa na sada-zumunta na yanar gizo mai suna Indomie Arewa, inda ake wallafa tambayoyi a kowace rana domin bai wa waɗanda ba su samu damar sauraron shirin rediyo ba damar shiga gasar.

Mutanen da suka amsa tambayoyin daidai a waɗannan shafuka na sada-zumunta suna samun kyautar kwalin taliyar Indomie domin taimaka wa iyalai a wannan lokaci na watan Ramadan.

Kamfanin ya bayyana cewa wannan shiri na nuna ƙudurinsa na tallafa wa al’umma da kuma samar da farin ciki a tsakanin jama’a a watan Ramadan mai alfarma.

Ramadan
Leadership Hausa
Website |  + postsBio
  • Leadership Hausa
    Karuwar Farin Jinin Gwamna Umaru Bago A Siyasar Jihar Neja
  • Leadership Hausa
    Kyakkyawan Tsarin Laken Asiri Zai Dakile Shirin Magudin Zabe A Nijeriya —Mohammed
  • Leadership Hausa
    Batun Dawo Da Tallafin Mai Da Atiku Ya Yi Na Ci Gaba Da Tayar Da Kura
  • Leadership Hausa
    Batun Guguwar Kakar Yakin Neman Zabukan 2027 A Nijeriya

MASU ALAKA

Sojoji
Manyan Labarai

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
'Yan Bindiga
Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina
Labarai

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Next Post
Hobbasar Gwamna Abba Kan Titunan Birnin Kano

Hobbasar Gwamna Abba Kan Titunan Birnin Kano

LABARAI MASU NASABA

Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.