ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ramadan: Za A Ci Gaba Da Bai Wa ‘Yan Wasa Musulmi Damar Buda Baki A Lokacin Buga Firimiyar Ingila

by Abba Ibrahim Wada and Sulaiman
4 months ago
Ramadan

A wannan shekarar ma, gasar firimiya ta Ingila da kuma English Football League za su ci gaba da aiwatar da tsarinsu na watan Ramadan, inda za a rika dakatar da wasa na dan lokaci, domin bai wa ‘yan wasa Musulmi damar buda baki. An fara Azumin watan Ramadan a wannan mako kuma zai dauki tsawon wata guda. A wannan lokaci, Musulmai na kaurace wa abinci da abin sha daga fitowar alfijir har zuwa faduwar rana.

Da yake faduwar rana a Birtaniya tana tsakanin karfe 17:00 zuwa 19:00 agogon GMT a wannan lokaci, wasannin da za a iya dakatarwa zai fi shafar na ranar Asabar da karfe 17:30 da kuma na ranar Lahadi da karfe 16:30.

  • Ƴansanda Sun Gayyaci Bello Ado Bayero Kan Zargin Damfarar Kuɗin Fili Naira Miliyan 70
  • ’Yar Wasan Kasar Sin Gu Ailing Ta Kare Kambunta A Gasar Olympics Ta Milan Cortina

Kamar yadda aka saba a shekarun baya, shugabannin kungiyoyi tare da alkalai za su cimma matasaya kan lokacin da ya kamata a tsayar da wasan domin bai wa ‘yan wasa ko jami’ai Musulmi damar buda baki.

ADVERTISEMENT

Kungiyoyi da alkalai za su tattauna tun kafin a fara wasa, domin cimma matsaya kan lokacin da ya kamata a dakatar da wasa domin bude bakin. Kuma ba za a tsayar da wasa ba a lokacin da ake gara kwallo, sai idan an samu damar bugun tazara ko jifa da dai sauransu. A shekarar 2021 ne aka cimma yarjejeniya da ta bai wa ‘yan wasa Musulmi damar buda baki yayin wasan Firimiya.

An kuma fara ne a wasa tsakanin Leicester City da Crystal Palace a watan Afrilu 2021. An dakatar da wasan a lokacin bugun falan daya a minti na 30 da fara wasan, domin bai wa Wesley Fofana na Leicester da Cheikhou Kouyate na Palace damar bude baki. Daga cikin sunayen ‘yan wasa Musulmi a gasar Firimiya akwai Mohamed Salah da William Saliba da Rayan Ait-Nouri da Amad Diallo da sauransu.

LABARAI MASU NASABA

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

Lionel Messi Ya Kafa Tarihin Wanda Yafi Kowa Zura Kwallaye A Tarihin Gasar Cin Kofin Duniya

A shekarar 2023, tsohon dan wasan EBerton Abdoulaye Doucoure ya ce: A gasar Firimiya mutum yana da ‘yancin yin abin da ya dace. Ba za su taBa yin wani abu da ya saBa wa addininka ba, kuma wannan abu ne mai kyau. Ya ce yana azumi kullum, bai taBa kin yi ko da rana guda ba. Yanzu ya zama al’ada a gare shi, kuma abu ne mai sauki. Horarwa tana tafiya kamar yadda aka saba a Ramadan, amma idan sun je wasannin waje, suna iya cin abinci daga baya fiye da sauran ‘yan wasa, don haka mai girki yana shirya musu abinci yadda ya kamata, kamar yadda suke samu a gida. Suna samun abinci halal, don haka babu wata matsala.

Haka kuma a shekarar 2022, tsohon dan wasan LiBerpool Sadio Mane ya bayyana cewa kungiyarsa tana sauya jadawalin atisaye domin tallafa wa ‘yan wasa Musulmi a watan Ramadan wanda ya yabi shugabannin kungiyar da masu bayar da horo, sai dai kawo yanzu abun haka yake a kasashe da daman a duniya.

Ramadan
Abba Ibrahim Wada
Website |  + posts Bio
  • Abba Ibrahim Wada
    Ɗanwasa Thomas Partey Ya Yi Rashin Nasara A Kotun Canada
  • Abba Ibrahim Wada
    FIFA Za Ta Biya Omar Artan Alawus Ɗin Da Za A Bai Wa Kowanne Alƙalin Wasa
  • Abba Ibrahim Wada
    Duk Da Rashin Halartar ‘Super Eagles’ Gasar Kofin Duniya, Nijeriya Ba Ta Rasa Wakilai Ba
  • Abba Ibrahim Wada
    Su Waye Wakilan Afirka A Kofin Duniya?
Ramadan
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci
  • Sulaiman
    Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026
  • Sulaiman
    Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara
  • Sulaiman
    Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

MASU ALAKA

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino
Wasanni

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

June 24, 2026
Lionel Messi Ya Kafa Tarihin Wanda Yafi Kowa Zura Kwallaye A Tarihin Gasar Cin Kofin Duniya
Wasanni

Lionel Messi Ya Kafa Tarihin Wanda Yafi Kowa Zura Kwallaye A Tarihin Gasar Cin Kofin Duniya

June 22, 2026
Ɗanwasa Thomas Partey Ya Yi Rashin Nasara A Kotun Canada
Wasanni

Ɗanwasa Thomas Partey Ya Yi Rashin Nasara A Kotun Canada

June 21, 2026
Next Post
Yadda Duniya Ke “Jin Dadin Sayayya A Bikin Bazara”

Yadda Duniya Ke "Jin Dadin Sayayya A Bikin Bazara"

LABARAI MASU NASABA

Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

June 24, 2026
Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

June 24, 2026
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

June 24, 2026
An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

June 24, 2026
Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

June 24, 2026
Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

June 23, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.