ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ramadan: Za A Ci Gaba Da Bai Wa ‘Yan Wasa Musulmi Damar Buda Baki A Lokacin Buga Firimiyar Ingila

by Abba Ibrahim Wada and Sulaiman
7 months ago
Ramadan

A wannan shekarar ma, gasar firimiya ta Ingila da kuma English Football League za su ci gaba da aiwatar da tsarinsu na watan Ramadan, inda za a rika dakatar da wasa na dan lokaci, domin bai wa ‘yan wasa Musulmi damar buda baki. An fara Azumin watan Ramadan a wannan mako kuma zai dauki tsawon wata guda. A wannan lokaci, Musulmai na kaurace wa abinci da abin sha daga fitowar alfijir har zuwa faduwar rana.

Da yake faduwar rana a Birtaniya tana tsakanin karfe 17:00 zuwa 19:00 agogon GMT a wannan lokaci, wasannin da za a iya dakatarwa zai fi shafar na ranar Asabar da karfe 17:30 da kuma na ranar Lahadi da karfe 16:30.

  • Ƴansanda Sun Gayyaci Bello Ado Bayero Kan Zargin Damfarar Kuɗin Fili Naira Miliyan 70
  • ’Yar Wasan Kasar Sin Gu Ailing Ta Kare Kambunta A Gasar Olympics Ta Milan Cortina

Kamar yadda aka saba a shekarun baya, shugabannin kungiyoyi tare da alkalai za su cimma matasaya kan lokacin da ya kamata a tsayar da wasan domin bai wa ‘yan wasa ko jami’ai Musulmi damar buda baki.

ADVERTISEMENT

Kungiyoyi da alkalai za su tattauna tun kafin a fara wasa, domin cimma matsaya kan lokacin da ya kamata a dakatar da wasa domin bude bakin. Kuma ba za a tsayar da wasa ba a lokacin da ake gara kwallo, sai idan an samu damar bugun tazara ko jifa da dai sauransu. A shekarar 2021 ne aka cimma yarjejeniya da ta bai wa ‘yan wasa Musulmi damar buda baki yayin wasan Firimiya.

An kuma fara ne a wasa tsakanin Leicester City da Crystal Palace a watan Afrilu 2021. An dakatar da wasan a lokacin bugun falan daya a minti na 30 da fara wasan, domin bai wa Wesley Fofana na Leicester da Cheikhou Kouyate na Palace damar bude baki. Daga cikin sunayen ‘yan wasa Musulmi a gasar Firimiya akwai Mohamed Salah da William Saliba da Rayan Ait-Nouri da Amad Diallo da sauransu.

LABARAI MASU NASABA

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

Ƙungiyoyi 5 Da Ke Takarar Gwarzuwar Ƙungiya Ta Bana

A shekarar 2023, tsohon dan wasan EBerton Abdoulaye Doucoure ya ce: A gasar Firimiya mutum yana da ‘yancin yin abin da ya dace. Ba za su taBa yin wani abu da ya saBa wa addininka ba, kuma wannan abu ne mai kyau. Ya ce yana azumi kullum, bai taBa kin yi ko da rana guda ba. Yanzu ya zama al’ada a gare shi, kuma abu ne mai sauki. Horarwa tana tafiya kamar yadda aka saba a Ramadan, amma idan sun je wasannin waje, suna iya cin abinci daga baya fiye da sauran ‘yan wasa, don haka mai girki yana shirya musu abinci yadda ya kamata, kamar yadda suke samu a gida. Suna samun abinci halal, don haka babu wata matsala.

Haka kuma a shekarar 2022, tsohon dan wasan LiBerpool Sadio Mane ya bayyana cewa kungiyarsa tana sauya jadawalin atisaye domin tallafa wa ‘yan wasa Musulmi a watan Ramadan wanda ya yabi shugabannin kungiyar da masu bayar da horo, sai dai kawo yanzu abun haka yake a kasashe da daman a duniya.

Ramadan
Abba Ibrahim Wada
Website |  + posts Bio
  • Abba Ibrahim Wada
    Yaushe Za A Fara Kofin Zakarun Turai
  • Abba Ibrahim Wada
    Messi Ya Yi Ritaya A Argentina: Da Me Za Mu Iya Tuna Gwarzon Duniyar?
  • Abba Ibrahim Wada
    Su Waye ‘Yan wasan Nijeriya Da Za Su Buga Gasar Firimiyar Ingila Ta Bana?
  • Abba Ibrahim Wada
    Chelsea A Ƙarƙashin Xavi Alonso
Ramadan
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
  • Sulaiman
    Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana
  • Sulaiman
    ‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna
  • Sulaiman
    Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

MASU ALAKA

Ballon D'or
Manyan Labarai

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

September 8, 2026
Ƙungiyoyi 5 Da Ke Takarar Gwarzuwar Ƙungiya Ta Bana
Wasanni

Ƙungiyoyi 5 Da Ke Takarar Gwarzuwar Ƙungiya Ta Bana

September 8, 2026
Kofin Duniya: Yau Falconets Za Su Kece Raini Da Spain
Wasanni

Kofin Duniya: Yau Falconets Za Su Kece Raini Da Spain

September 7, 2026
Next Post
Yadda Duniya Ke “Jin Dadin Sayayya A Bikin Bazara”

Yadda Duniya Ke "Jin Dadin Sayayya A Bikin Bazara"

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.