ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sabbin Hare-haren Ta’addanci: Ba Za Mu Yarda Matsalar Tsaro Ta Dakushe Kokarinmu Na Bunkasa Kasa Ba –Tinubu

by Sani Anwar and Sulaiman
4 months ago
Tinubu

Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu, ya yi ikirarin cewa; gwamnatinsa za ta kara zage damtse, wajen tunkarar kalubalen rashin tsaro a fadin kasar nan, inda ya bayar da tabbacin kare lafiyar ‘yan kasar a tarukan da aka gudanar a Kasar Birtaniya.

Tinubu, wanda ya karbi bakuncin mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima da gwamnoni 23 a gidansa da ke Legas, domin gudanar da bukukuwan Sallah Karama ya ce, ya bi diddigi tare kuma da goyon bayan matakan tsaro na zamani tare da Shugaban Kasar Faransa, Emmanuel Macron.

  • Trump Ya Yi Barazanar Kwace Man Iran Yayin Da Rikici Ke Sake Ruruwa
  • CMG Ya Yi Taron Tattaunawa Na Duniya Na “Sin A Lokacin Bazara” A Hadaddiyar Daular Larabawa

Kasancewarku a nan a yau, yana nuna gaskiya, sadaukarwa da kuma darajar da kuke da ita wajen aiwatar da hadin kai.

ADVERTISEMENT

“Babban abin da muke fuskanta, yake kuma ci mana tuwo a kwarya a halin yanzu shi ne, batun kalubalen rashin tsaro a kasar.

“Ina yin dukkan kokarin da ya dace, domin ganin mun samu nasara a kan wannan ta’addanci da rashin tsaro da muke fama da shi.

LABARAI MASU NASABA

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

Tsohon Sanatan Gombe, Bayero Nafada, Ya Fice Daga PDP Bayan Ganawa da Shugabannin APC

“Kazalika, na himmatu wajen karfafa abokan hulda da hanyoyin sadarwa, wadanda suka zama dole, sannan daya daga cikin manyan abubuwan da muka tattaunawa a Burtaniya, sun hada da samar da kayan aiki da kuma tallafi.

“Zan kuma iya yi muku albishir na cewa, a jiya na yi doguwar tattaunawa da shugaban Faransa, Emmanuel Macron, a kan batun samar da kayan aiki da kuma tallafi. Ina kuma ci gaba da yunkurin tuntubar wasu kasashen,” in ji shi.

A ranar Juma’a ne, shugaba Tinubu da uwargidansa, Oluremi Tinubu, suka dawo daga ziyarar aiki ta kwanaki uku da suka kai Kasar Birtaniya, inda Sarki Charles III da Sarauniya Camila suka karbe su.

Shugaban ya kuma yi wata ganawa da Firaministan Kasar Birtaniya, Keir Starmer, kafin ya dawo Nijeriya, domin gudanar da bikin sallah karama.

“Ya kamata mu kara kula da masu rauni. Dalili kuwa, na san wannan rikicin na Gabas ta Tsakiya, zai haifar da hauhawar farashin kayayyaki. Haka zalika, kungiyar kwadago da sauran wasu kungiyoyi, za su yi shiri domin neman karin tallafi, sakamakon wannan rikici na Gabas ta Tsakiya, “in ji shugaban.

Har ila yau, shugaban ya kuma bukaci gwamnonin jihohin, su dage tare da juriya wajen aiwatar da tsare-tsaren da suka dace, domin sama wa ‘yan kasa sauki kai tsaye, tare da mara wa gwamnati baya wajen tinkarar “zalunci” na masu aikata laifuka.

Shugaba Tinubu ya shawarci gwamnonin da su kara bayar da kwarin guiwa, domin dakile illar hauhawar farashin kayayyaki, sakamakon wannan yaki da ake yi a Gabas ta Tsakiya.

Haka zalika, ya mika godiyarsa ga mataimakin shugaban kasa, Sanata. Kashim Shettima, bisa ziyarar jaje da ya kai Jihar Borno, inda ya bai wa jama’ar jihar tabbacin samun karin kariya ta hanyar fasahar zamani.

A nasa jawabin, shugaban kungiyar gwamnonin Nijeriya, kuma Gwamnan Jihar Kwara, AbdulRahman AbdulRazak, ya gode wa shugaban kasar, kan tsoma bakin da ya yi a jihohin tare da aiwatar da ajandar shirin nan na ‘Renewed Hope’.

A madadin takwarorina, gwamnoni, muna miko gaisuwa tare da yi maka barka da sallah, muna kuma godiya ga Allah Madaukakin Sarki, da ya nuna mana karshen watan Ramadan lafiya.”

Haka zaliika, shugaban ya taya shugaban kasar murnar nasarar da ya samu ta ziyarar aiki da ya kai Kasar Birtaniya da kuma yarjejeniyar zuba jari da aka cimma.

“Babbar manufarmu ita ce, kulla kyakkyawar alaka da Burtaniya, ziyarar kasar ta farko a cikin shekara 37 na da matukar muhimmanci tare da kulla sabuwar alaka da Nijeriya, muna matukar godiya.

“Dole ne mu tabbatar da cewa, batun rashin tsaro ya zo karshe, sannan batun ‘yansandan jihohi, ana ci gaba da tattaunawa da hukumomin tsaro daban-daban a karkashin jagorancin mai bayar da shawara a kan harkokin tsaro, kungiyar gwamnoni kuma tana ba da gudunmawar da ta dace domin tabbatar da al’amarin, kazalika kungiyar za ta kai takardar zuwa Majalisar Dokoki ta Kasa, domin ganin yadda za mu iya samun tsarin doka ga ‘yansandan jihohin,” in ji gwamnan.

Gwamnonin da suka halarci taron sun hada da: Sanata Hope Uzodinma, Jihar Imo; Aled Otti, Jihar Abia; Umo Eno, Jihar Akwa Ibom; Douye Diri, Jihar Bayelsa; Hyacinth Alia, Jihar Benue; Bassey Otu, Jihar Kuros Riba; Sheriff Oborebwori, Jihar Delta; Francis Nwifuru, Jihar Ebonyi; Monday Okpebolo, Jihar Edo; Peter Mbah, Jihar Enugu; Mohammed Inuwa Yahaya, Jihar Gombe; da Umar Namadi, Jihar Jigawa.

Sauran kuma sun hada da: Abba Kabir Yusuf, Jihar Kano; Dikko Umaru Radda, Jihar Katsina; Ahmed Usman Ododo, Jihar Kogi; Babajide Sanwo-Olu, Jihar Legas; Abdullahi Sule, Jihar Nasarawa; Caleb Mufwang, Jihar Filato; Siminalayi Fubara, Jihar Ribas; Agbu Keffas, Jihar Taraba; Mai Mala Buni na Jihar Yobe da Lucky Aiyedatiwa, Jihar Ondo.

Mataimakin Gwamnan Jihar Borno, Umar Usman Kadafur, shi ma ya halarci taron.

Tinubu
Sani Anwar
+ posts Bio
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Shugaban Rundunar Sojojin Nijeriya Ya Nemi Haɗin Kan Fararen Hula
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Ƴan Ƙwadago Sun Buƙaci Naira 300,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    NiMet Ta Gargaɗi Jihohi 27 Kan Barazanar Ambaliyar Ruwa A Farkon Watan Yuli
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    2027: Masu Ruwa Da Tsaki Sun Amince Da Jamilu Gwamna A Matsayin Gwamnan Gombe
Tinubu
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya
  • Sulaiman
    Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026
  • Sulaiman
    An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”
  • Sulaiman
    Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

MASU ALAKA

Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga
Manyan Labarai

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
Tsohon Sanatan Gombe, Bayero Nafada, Ya Fice Daga PDP Bayan Ganawa da Shugabannin APC
Manyan Labarai

Tsohon Sanatan Gombe, Bayero Nafada, Ya Fice Daga PDP Bayan Ganawa da Shugabannin APC

July 14, 2026
Sojoji Sun Kashe ’Yan Ta’adda 3, Sun Ƙwato Makamai A Sakkwato
Manyan Labarai

Sojoji Sun Daƙile Harin ISWAP A Borno

July 14, 2026
Next Post
Zamfara

Gwamnatin Tarayya Ta Yi Alkawarin Kawo Karshen Matsalar Tsaro A Zamfara

LABARAI MASU NASABA

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

July 14, 2026
Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

July 14, 2026
Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

July 14, 2026
CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.