ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sabbin Hare-haren Ta’addanci: Ba Za Mu Yarda Matsalar Tsaro Ta Dakushe Kokarinmu Na Bunkasa Kasa Ba –Tinubu

by Sani Anwar and Sulaiman
3 months ago
Tinubu

Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu, ya yi ikirarin cewa; gwamnatinsa za ta kara zage damtse, wajen tunkarar kalubalen rashin tsaro a fadin kasar nan, inda ya bayar da tabbacin kare lafiyar ‘yan kasar a tarukan da aka gudanar a Kasar Birtaniya.

Tinubu, wanda ya karbi bakuncin mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima da gwamnoni 23 a gidansa da ke Legas, domin gudanar da bukukuwan Sallah Karama ya ce, ya bi diddigi tare kuma da goyon bayan matakan tsaro na zamani tare da Shugaban Kasar Faransa, Emmanuel Macron.

  • Trump Ya Yi Barazanar Kwace Man Iran Yayin Da Rikici Ke Sake Ruruwa
  • CMG Ya Yi Taron Tattaunawa Na Duniya Na “Sin A Lokacin Bazara” A Hadaddiyar Daular Larabawa

Kasancewarku a nan a yau, yana nuna gaskiya, sadaukarwa da kuma darajar da kuke da ita wajen aiwatar da hadin kai.

ADVERTISEMENT

“Babban abin da muke fuskanta, yake kuma ci mana tuwo a kwarya a halin yanzu shi ne, batun kalubalen rashin tsaro a kasar.

“Ina yin dukkan kokarin da ya dace, domin ganin mun samu nasara a kan wannan ta’addanci da rashin tsaro da muke fama da shi.

LABARAI MASU NASABA

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

“Kazalika, na himmatu wajen karfafa abokan hulda da hanyoyin sadarwa, wadanda suka zama dole, sannan daya daga cikin manyan abubuwan da muka tattaunawa a Burtaniya, sun hada da samar da kayan aiki da kuma tallafi.

“Zan kuma iya yi muku albishir na cewa, a jiya na yi doguwar tattaunawa da shugaban Faransa, Emmanuel Macron, a kan batun samar da kayan aiki da kuma tallafi. Ina kuma ci gaba da yunkurin tuntubar wasu kasashen,” in ji shi.

A ranar Juma’a ne, shugaba Tinubu da uwargidansa, Oluremi Tinubu, suka dawo daga ziyarar aiki ta kwanaki uku da suka kai Kasar Birtaniya, inda Sarki Charles III da Sarauniya Camila suka karbe su.

Shugaban ya kuma yi wata ganawa da Firaministan Kasar Birtaniya, Keir Starmer, kafin ya dawo Nijeriya, domin gudanar da bikin sallah karama.

“Ya kamata mu kara kula da masu rauni. Dalili kuwa, na san wannan rikicin na Gabas ta Tsakiya, zai haifar da hauhawar farashin kayayyaki. Haka zalika, kungiyar kwadago da sauran wasu kungiyoyi, za su yi shiri domin neman karin tallafi, sakamakon wannan rikici na Gabas ta Tsakiya, “in ji shugaban.

Har ila yau, shugaban ya kuma bukaci gwamnonin jihohin, su dage tare da juriya wajen aiwatar da tsare-tsaren da suka dace, domin sama wa ‘yan kasa sauki kai tsaye, tare da mara wa gwamnati baya wajen tinkarar “zalunci” na masu aikata laifuka.

Shugaba Tinubu ya shawarci gwamnonin da su kara bayar da kwarin guiwa, domin dakile illar hauhawar farashin kayayyaki, sakamakon wannan yaki da ake yi a Gabas ta Tsakiya.

Haka zalika, ya mika godiyarsa ga mataimakin shugaban kasa, Sanata. Kashim Shettima, bisa ziyarar jaje da ya kai Jihar Borno, inda ya bai wa jama’ar jihar tabbacin samun karin kariya ta hanyar fasahar zamani.

A nasa jawabin, shugaban kungiyar gwamnonin Nijeriya, kuma Gwamnan Jihar Kwara, AbdulRahman AbdulRazak, ya gode wa shugaban kasar, kan tsoma bakin da ya yi a jihohin tare da aiwatar da ajandar shirin nan na ‘Renewed Hope’.

A madadin takwarorina, gwamnoni, muna miko gaisuwa tare da yi maka barka da sallah, muna kuma godiya ga Allah Madaukakin Sarki, da ya nuna mana karshen watan Ramadan lafiya.”

Haka zaliika, shugaban ya taya shugaban kasar murnar nasarar da ya samu ta ziyarar aiki da ya kai Kasar Birtaniya da kuma yarjejeniyar zuba jari da aka cimma.

“Babbar manufarmu ita ce, kulla kyakkyawar alaka da Burtaniya, ziyarar kasar ta farko a cikin shekara 37 na da matukar muhimmanci tare da kulla sabuwar alaka da Nijeriya, muna matukar godiya.

“Dole ne mu tabbatar da cewa, batun rashin tsaro ya zo karshe, sannan batun ‘yansandan jihohi, ana ci gaba da tattaunawa da hukumomin tsaro daban-daban a karkashin jagorancin mai bayar da shawara a kan harkokin tsaro, kungiyar gwamnoni kuma tana ba da gudunmawar da ta dace domin tabbatar da al’amarin, kazalika kungiyar za ta kai takardar zuwa Majalisar Dokoki ta Kasa, domin ganin yadda za mu iya samun tsarin doka ga ‘yansandan jihohin,” in ji gwamnan.

Gwamnonin da suka halarci taron sun hada da: Sanata Hope Uzodinma, Jihar Imo; Aled Otti, Jihar Abia; Umo Eno, Jihar Akwa Ibom; Douye Diri, Jihar Bayelsa; Hyacinth Alia, Jihar Benue; Bassey Otu, Jihar Kuros Riba; Sheriff Oborebwori, Jihar Delta; Francis Nwifuru, Jihar Ebonyi; Monday Okpebolo, Jihar Edo; Peter Mbah, Jihar Enugu; Mohammed Inuwa Yahaya, Jihar Gombe; da Umar Namadi, Jihar Jigawa.

Sauran kuma sun hada da: Abba Kabir Yusuf, Jihar Kano; Dikko Umaru Radda, Jihar Katsina; Ahmed Usman Ododo, Jihar Kogi; Babajide Sanwo-Olu, Jihar Legas; Abdullahi Sule, Jihar Nasarawa; Caleb Mufwang, Jihar Filato; Siminalayi Fubara, Jihar Ribas; Agbu Keffas, Jihar Taraba; Mai Mala Buni na Jihar Yobe da Lucky Aiyedatiwa, Jihar Ondo.

Mataimakin Gwamnan Jihar Borno, Umar Usman Kadafur, shi ma ya halarci taron.

Tinubu
Sani Anwar
+ posts Bio
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Tattalin Arziƙin Ƙasa: Masana Sun Buƙaci Tinubu Ya Yi Hattara Da Shawarar IMF
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (2)
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (1)
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF
Tinubu
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace
  • Sulaiman
    ’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin
  • Sulaiman
    Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
  • Sulaiman
    Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

MASU ALAKA

Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso
Manyan Labarai

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku
Manyan Labarai

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Next Post
Zamfara

Gwamnatin Tarayya Ta Yi Alkawarin Kawo Karshen Matsalar Tsaro A Zamfara

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.