ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Saboda In Nuna Wa Duniya Asalin Al’adar Bahaushe Ya Sa Na Fara Fina-finan Turanci A Arewacin Nijeriya – Jammaje

by Rabilu Sanusi Bena and Sulaiman
1 year ago
Jammaje

Da yawa masu sha’awar kallon fina finan da ake shiryawa a masana’antar Kannywood sun saba gani ko jin ana amfanin da harshen Hausa wajen isar da duk wani sako da fim din yake dauke dashi, ba kasafai aka saba ganin fina finan da ake shiryawa a masana’antar Kannywood sun fito da wani yare na daban ba illa Hausa.

 

Amma kuma daya daga cikin Hausawa da suka kware a turancin Ingilishi kuma furodusan fina-finai a masana’antar Kannywood Kabiru Musa Jammaje ya dukufa wajen ganin ya canza wannan tunani da mutane ke yi na cewa masana’antar Kannywood bata da wata hanyar isar da sako sai ta hanyar harshen uwa (Hausa).

ADVERTISEMENT
  • Daga Kaina An Gama Harkar Fim A Zuri’ata – Moda
  • Shugaban Kasar Azerbaijan Ya Tattauna Da Wakiliyar CMG

Inda a shekarar 2010 ya fara tunanin fara shirya fina finai da za a dauka a arewacin Nijeriya amma kuma a yi magana da yaren Ingilishi, wanda a tunaninsa zai sa sakon da fim din zai isar ya isa zuwa sauran sassan Duniya, ma’ana ba ya tsaya a iya inda ake jin harshen Hausa ba ya tafi zuwa ga wata al’ummar da ke jin yaren Ingilishi.

 

LABARAI MASU NASABA

Daraktan Hollywood Carl Rinsch Zai Shafe Watanni 30 A Gidan Gyaran Hali

Zan Iya Auren Namiji Komai Talaucinsa Muddin Muna Son Junanmu -Maryam Labarina

A wata hira da Jammaje ya yi da rfI Hausa an jiyo shi ya na cewa sunana Kabiru Musa Jammaje haifaffen Jihar Kano, nayi karatu a Bayero Unibersity da ke birnin Kano inda na karanci English kafin in tafi kasar Amurka domin zurfafa karatu, bayan na dawo gida Nijeriya kuma na shiga Jami’ar koyo daga gida ta NOUN inda na karanci ‘Education Administration and Planning’.

 

Jammaje ya ci gaba da cewa a yawace yawacen da na yi na tafi kasashe irinsu Afirika Ta Kudu da kasar Kenya inda a wancan lokacin sai na lura cewa mutanen wadannan kasashen biyu suna yi wa duk wani dan Nijeriya wani kallo na daban sakamakon abin da suka ga ana nunawa a wasu fina finan da suke kallo da ake shiryawa a kudancin Nijeriya (Nollywood, ganin ana nuna abubuwa kamar tsafe-tsafe, fashi da makami, damfara ko kuma mutane masu shan jini.

 

Hakan yasa suke yi wa duk wani da ya zo daga Nijeriya irin wannan kallon, wannan sai ya ja hankalina na ce to mi zai hana mu da muke yin fina-finai da babu duk wadannan abubuwa marasa kyau a cikinsu a nan Arewacin Nijeriya (Kannywood) mu kawo masu namu fina-finan su kalla, sai kuma naga cewar babu wata hanya da hakan za ta iya faruwa sai idan wadannan mutane za su ji abin da muke fadi a fina-finan.

 

Wannan ne ya kara mani kwarin gwuiwar tunkarar wannan aiki gadan-gadan, sai na tuntubi wasu daga cikin abokaina da ke a masana’antar kamar su Falalu Dorayi, Abba El Mustapha da sauransu domin zakulo hanyoyin da za su kaimu ga samun nasara, kuma Alhamdulillahi hakan ya matukar tasiri domin kuwa abin da muke yi a yanzu ya samu karbuwa a ciki da wajen Nijeriya in ji Jammaje.

 

Jammaje wanda yanzu haka yake da makarantun koyar da harshen Turanci a mafi yawancin jihohin Arewacin Nijeriya ya ci gaba da cewa, a lokacin da na shigo masana’antar Kannywood ban yi tunanin bayan Ali Nuhu akwai wadanda suke jin turanci ba, amma kuma bayan na shiga sai na gano akwai wadanda su ka kware sosai a turanci a masana’antar wanda hakan sai ya sau kaka mana aikin.

 

Da yake amsa tambaya a kan wace irin nasara ya samu tun bayan fara wannan yunkurin Kabiru Musa Jammaje ya ce akwai tarin nasarori da aka samu, domin kuwa a shekarar 2017 a wata ziyara da ya kai kasar Ingila akwai wasu iyali da ya nuna masu fim din There Is A Way, sai suke mamaki har suna tambaya dama akwai wani yanki da ake kira Arewa a Nijeriya, sai suke cewa basu taba jin wani yare wai Hausa ba, sai na ce masu ai wannan fim fin kacokan dinsa an yi shi ne a arewacin Nijeriya kuma duka abin da suka gani shi ne asalin abin da bahaushe ya kunsa, kama daga zamantakewa, al’ada da kuma yanayin sutura sai suka dinga mamaki.

 

Sannan kuma fina finan da muka yi sun samu daukaka sosai don kuwa har da kyautuka muka dinga samu a ta sanadiyarsu kamar fim din ‘In Search Of The King’ da ya taba lashe kyautar Fim Mafi Kyawu a wani bikin karramawa da aka yi, sai kuma sabon fim dinmu mai suna Nanjala wanda yanzu haka akwai wani wurin yawon bude ido da ke kasar Turkey da suka saye fim din domin su nunawa bakinsu (Tourist) irin yadda al’adar mutanen kasashen Afirika musamman Arewacin Nijeriya ta ke.

Jammaje
Rabilu Sanusi Bena
+ posts Bio
  • Rabilu Sanusi Bena
    https://hausa.leadership.ng/author/rabilu-sanusi-bena/
    FIFA Na Nazarin Faɗaɗa Gasar Kofin Duniya Zuwa Ƙasashe 64
  • Rabilu Sanusi Bena
    https://hausa.leadership.ng/author/rabilu-sanusi-bena/
    Harry Kane: Lashe Kofin Duniya Ya Fi Mini Muhimmanci Fiye da Takalmin Zinare
  • Rabilu Sanusi Bena
    https://hausa.leadership.ng/author/rabilu-sanusi-bena/
    Kofin Duniya: Na fi Son Faransa Ta Kara Da Argentina A Wasan Ƙarshe A Kan Ingila — Vieira
  • Rabilu Sanusi Bena
    https://hausa.leadership.ng/author/rabilu-sanusi-bena/
    Argentina Ta Kai Zagayen Kwata Fainal Bayan Nunawa Egypt Ƙwanji
Jammaje
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya
  • Sulaiman
    Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026
  • Sulaiman
    An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”
  • Sulaiman
    Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

MASU ALAKA

Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Labarai

Daraktan Hollywood Carl Rinsch Zai Shafe Watanni 30 A Gidan Gyaran Hali

July 12, 2026
Zan Iya Auren Namiji Komai Talaucinsa Muddin Muna Son Junanmu -Maryam Labarina
Nishadi

Zan Iya Auren Namiji Komai Talaucinsa Muddin Muna Son Junanmu -Maryam Labarina

June 14, 2026
Gidajen Gala Ne Kadai Mafita Ga Masana’antar Kannywood – Falalu Dorayi
Nishadi

Gidajen Gala Ne Kadai Mafita Ga Masana’antar Kannywood – Falalu Dorayi

June 14, 2026
Next Post
Ribar Wasu Manyan Kamfanonin Masana’antun Sin Ta Karu Da 0.8% a Farkon Watanni Uku Na Bana

Ribar Wasu Manyan Kamfanonin Masana’antun Sin Ta Karu Da 0.8% a Farkon Watanni Uku Na Bana

LABARAI MASU NASABA

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

July 15, 2026
Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

July 15, 2026
Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.