ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Saboda In Nuna Wa Duniya Asalin Al’adar Bahaushe Ya Sa Na Fara Fina-finan Turanci A Arewacin Nijeriya – Jammaje

by Rabilu Sanusi Bena and Sulaiman
1 year ago
Jammaje

Da yawa masu sha’awar kallon fina finan da ake shiryawa a masana’antar Kannywood sun saba gani ko jin ana amfanin da harshen Hausa wajen isar da duk wani sako da fim din yake dauke dashi, ba kasafai aka saba ganin fina finan da ake shiryawa a masana’antar Kannywood sun fito da wani yare na daban ba illa Hausa.

 

Amma kuma daya daga cikin Hausawa da suka kware a turancin Ingilishi kuma furodusan fina-finai a masana’antar Kannywood Kabiru Musa Jammaje ya dukufa wajen ganin ya canza wannan tunani da mutane ke yi na cewa masana’antar Kannywood bata da wata hanyar isar da sako sai ta hanyar harshen uwa (Hausa).

ADVERTISEMENT
  • Daga Kaina An Gama Harkar Fim A Zuri’ata – Moda
  • Shugaban Kasar Azerbaijan Ya Tattauna Da Wakiliyar CMG

Inda a shekarar 2010 ya fara tunanin fara shirya fina finai da za a dauka a arewacin Nijeriya amma kuma a yi magana da yaren Ingilishi, wanda a tunaninsa zai sa sakon da fim din zai isar ya isa zuwa sauran sassan Duniya, ma’ana ba ya tsaya a iya inda ake jin harshen Hausa ba ya tafi zuwa ga wata al’ummar da ke jin yaren Ingilishi.

 

LABARAI MASU NASABA

Ban Taɓa Fitowa A Fim Na Yi Da-na-sani Ba —Habibu Yaro

Ya Kamata Mawaƙa Su Guji Munafunci Da Hassada Su Rungumi Juna —Fati UK

A wata hira da Jammaje ya yi da rfI Hausa an jiyo shi ya na cewa sunana Kabiru Musa Jammaje haifaffen Jihar Kano, nayi karatu a Bayero Unibersity da ke birnin Kano inda na karanci English kafin in tafi kasar Amurka domin zurfafa karatu, bayan na dawo gida Nijeriya kuma na shiga Jami’ar koyo daga gida ta NOUN inda na karanci ‘Education Administration and Planning’.

 

Jammaje ya ci gaba da cewa a yawace yawacen da na yi na tafi kasashe irinsu Afirika Ta Kudu da kasar Kenya inda a wancan lokacin sai na lura cewa mutanen wadannan kasashen biyu suna yi wa duk wani dan Nijeriya wani kallo na daban sakamakon abin da suka ga ana nunawa a wasu fina finan da suke kallo da ake shiryawa a kudancin Nijeriya (Nollywood, ganin ana nuna abubuwa kamar tsafe-tsafe, fashi da makami, damfara ko kuma mutane masu shan jini.

 

Hakan yasa suke yi wa duk wani da ya zo daga Nijeriya irin wannan kallon, wannan sai ya ja hankalina na ce to mi zai hana mu da muke yin fina-finai da babu duk wadannan abubuwa marasa kyau a cikinsu a nan Arewacin Nijeriya (Kannywood) mu kawo masu namu fina-finan su kalla, sai kuma naga cewar babu wata hanya da hakan za ta iya faruwa sai idan wadannan mutane za su ji abin da muke fadi a fina-finan.

 

Wannan ne ya kara mani kwarin gwuiwar tunkarar wannan aiki gadan-gadan, sai na tuntubi wasu daga cikin abokaina da ke a masana’antar kamar su Falalu Dorayi, Abba El Mustapha da sauransu domin zakulo hanyoyin da za su kaimu ga samun nasara, kuma Alhamdulillahi hakan ya matukar tasiri domin kuwa abin da muke yi a yanzu ya samu karbuwa a ciki da wajen Nijeriya in ji Jammaje.

 

Jammaje wanda yanzu haka yake da makarantun koyar da harshen Turanci a mafi yawancin jihohin Arewacin Nijeriya ya ci gaba da cewa, a lokacin da na shigo masana’antar Kannywood ban yi tunanin bayan Ali Nuhu akwai wadanda suke jin turanci ba, amma kuma bayan na shiga sai na gano akwai wadanda su ka kware sosai a turanci a masana’antar wanda hakan sai ya sau kaka mana aikin.

 

Da yake amsa tambaya a kan wace irin nasara ya samu tun bayan fara wannan yunkurin Kabiru Musa Jammaje ya ce akwai tarin nasarori da aka samu, domin kuwa a shekarar 2017 a wata ziyara da ya kai kasar Ingila akwai wasu iyali da ya nuna masu fim din There Is A Way, sai suke mamaki har suna tambaya dama akwai wani yanki da ake kira Arewa a Nijeriya, sai suke cewa basu taba jin wani yare wai Hausa ba, sai na ce masu ai wannan fim fin kacokan dinsa an yi shi ne a arewacin Nijeriya kuma duka abin da suka gani shi ne asalin abin da bahaushe ya kunsa, kama daga zamantakewa, al’ada da kuma yanayin sutura sai suka dinga mamaki.

 

Sannan kuma fina finan da muka yi sun samu daukaka sosai don kuwa har da kyautuka muka dinga samu a ta sanadiyarsu kamar fim din ‘In Search Of The King’ da ya taba lashe kyautar Fim Mafi Kyawu a wani bikin karramawa da aka yi, sai kuma sabon fim dinmu mai suna Nanjala wanda yanzu haka akwai wani wurin yawon bude ido da ke kasar Turkey da suka saye fim din domin su nunawa bakinsu (Tourist) irin yadda al’adar mutanen kasashen Afirika musamman Arewacin Nijeriya ta ke.

Jammaje
Rabilu Sanusi Bena
+ posts Bio
  • Rabilu Sanusi Bena
    https://hausa.leadership.ng/author/rabilu-sanusi-bena/
    Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City
  • Rabilu Sanusi Bena
    https://hausa.leadership.ng/author/rabilu-sanusi-bena/
    Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya
  • Rabilu Sanusi Bena
    https://hausa.leadership.ng/author/rabilu-sanusi-bena/
    Galatasaray Ta Sanya Farashin Yuro Miliyan 150 Kan Osimhen, Chelsea Ta Nuna Sha’awar Ɗaukarsa
  • Rabilu Sanusi Bena
    https://hausa.leadership.ng/author/rabilu-sanusi-bena/
    Super Eagles Ta Tafi Poland Domin Wasan Sada Zumunta
Jammaje
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa
  • Sulaiman
    Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku
  • Sulaiman
    Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito
  • Sulaiman
    An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

MASU ALAKA

Ban Taɓa Fitowa A Fim Na Yi Da-na-sani Ba —Habibu Yaro
Nishadi

Ban Taɓa Fitowa A Fim Na Yi Da-na-sani Ba —Habibu Yaro

May 31, 2026
Laifukan Intanet: Kotun Abuja Ta Karɓi Rahoton DSS, Ta Ba Da Belin Wani Ɗan Gwagwarmaya
Nishadi

Ya Kamata Mawaƙa Su Guji Munafunci Da Hassada Su Rungumi Juna —Fati UK

May 23, 2026
Har Yanzu Burina Bai Cika Ba A Waka —Hadiza Maikano
Nishadi

Har Yanzu Burina Bai Cika Ba A Waka —Hadiza Maikano

May 16, 2026
Next Post
Ribar Wasu Manyan Kamfanonin Masana’antun Sin Ta Karu Da 0.8% a Farkon Watanni Uku Na Bana

Ribar Wasu Manyan Kamfanonin Masana’antun Sin Ta Karu Da 0.8% a Farkon Watanni Uku Na Bana

LABARAI MASU NASABA

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026
Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

June 4, 2026
Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

June 4, 2026
Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.