ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, July 5, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

SDP Ta Gargadi INEC Kan Yin Katsalandan A Harkokin Jam’iyyar

by Leadership Hausa
6 months ago

Jam’iyyar SDP ta gargadi hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC) kan yin katsalandan a cikin harkokinta, tana mai jaddada cewa jam’iyyar ce kawai za ta iya yanke hukunci kan harkokinta na cikin gida.

Jam’iyyar ta yi maraba da hukuncin kotun koli da ta ki amincewa da shari’ar da INEC ta shigar kan rikicin shugabancinta, inda ta bayyana wannan hukunci a matsayin babban nasara ga dimokuradiyya da ‘yancin jam’iyya da kuma bin dokar kasa.

  • Sheikh Al-Sudais Ya Gargadi Masu Ibadah Kan Kiyaye Darajar Masallatan Harami
  • An Yi Bikin Murnar Cika Shekaru 15 Da Kafuwar Asibitin Abota Na Sin Da Ghana

A cikin hukuncin da ta yanke a ranar Jumma’a, kotun koli ta ki amincewa da korafin INEC na kalubalantar shugabancin SDP kuma ta umarci biyan naira miliyan 2 a matsayin kudin tara ga hukumar. Kotun koli ta bayyana korafin a matsayin wanda bai dace ba kuma ya saba wa doka.

ADVERTISEMENT

INEC ta nemi a soke hukuncin 17 ga Oktoba na kotun daukaka kara da ke Abuja, wanda ya tabbatar da hukuncin babban kotun tarayya wanda ya tilasta wa hukumar ta amince da kuma hada ‘yan takarar SDP a zabukan cike gurbi a jihohi 12.

A yayin da yake magana a taron manema labarai a shalkwatar jam’iyya da ke Abuja bayan yanke hukuncin, mukaddashin shugaban jam’iyyar SDP na kasa, Sadik Gombe, ya ce hukuncin kotun kolin ya tabbatar da matsayin shari’a da aka dade ana yi da cewa harkokin cikin gida na jam’iyyu bai kamata a samu tsoma baki daga waje ba.

LABARAI MASU NASABA

Ci-ma-zaunen Ƴan Siyasa Ne Ke Tunanin Yin Maguɗi A Zaɓen 2027 – Makarfi

An Samu Ruɗani Kan Rashin Bayyana Jerin Ƴan Takarar Jam’iyyun Siyasa Na Zaɓen 2027

“Wannan hukuncin yana da matukar muhimmanci, ba wai ga SDP kadai ba, har ma ga dukkan jam’iyyun siyasa a Nijeriya. Yana tabbatar da matsayin kotun koli na cewa al’amuran cikin gida na jam’iyyun siyasa, jam’iyyun ne kadai za su yanke hukunci a kai,” in ji shi.

Gombe ya bukaci INEC ta cika hukuncin gaba daya ta hanyar ba wa jam’iyyun siyasa damar gudanar da harkokinsu na ciki bisa tsarin kundinsu. Har ila yau, ya yi kira ga jam’iyyun da su kiyaye dabi’a na ciki gida da bin tsarin da ya dace.

“Muna godiya wa bangaren shari’a. Muna fatan wannan hukunci zai kara karfafa dimokuradiyyarmu da dokar kasa yayin da muke tukarar zaben 2027. Mun fahimci damuwarsu da sha’awarsu, duk da haka adalci dole ne ko da yaushe ya yi rinjayi. Muna sa ran INEC daga yanzu za ta daina tsoma baki a cikin harkokin cikin gida na jam’iyyun siyasa, domin wannan batun tun da farko kotun koli ta yanke hukunci tare da warware zare da abawa. Hukumar kuma dole ta daina duk wani mu’amala da mambobi da aka dakatar ko aka kore daga jam’iyya kuma ta amince nan take da sauya shugabancin mukaddashin jam’iyyar na kasa Shehu Gabam,” in ji shi.

A yayin mayar da martani ga hukuncin, babban lauya na SDP kuma dan takarar jam’iyyar na shugaban kasa a 2023, Adewole Adebayo, ya ce hukuncin ya aika da gargadi a fili ga INEC da ta guji ayyukan da za su iya raunana dimokuradiyyar jam’iyyun siyasa da dama a Nijeriya.

“Na bayyana wa INEC cewa su daina tsoma baki a harkokin ciki na SDP da sauran jam’iyyun siyasa. Dimokiradiyyar jam’iyyun da dama na bukatar alkalin da ba ya nuna bambanci ba, ba wanda ke haddasa rikice-rikice a cikin jam’iyyun adawa,” in ji Adebayo.

Adebayo ya bayyana cewa rikicin ya taso ne bayan jam’iyyar ta nada shugaban jam’iyyar na kasa na wucin gadi wanda ta rubuta wa INEC don tatace ‘yan takara, inda hukumar ta ki amincewa da shi, ta zabi ma ta yi mu’amala da shugaban da jam’iyyar ta riga ta kora.

Jam’iyyar ta tabbatar da cewa hukuncin kotun koli ya kara karfafa mata kwarin gwiwa tare da una cewa kotu ba ta yarda da tsoma baki daga hukumomin tsara dokoki cikin harkokin cikin gida na jam’iyyun siyasa ba.

Leadership Hausa
Website |  + postsBio
  • Leadership Hausa
    Batun Dakile Shan Taba Sigari A Tsakanin Yara A Nijeriya
  • Leadership Hausa
    Har Yanzu Akwai Sauran Rina A Kaba Game Da Makomar Yara A Nijeriya
  • Leadership Hausa
    Yadda Arsenal Ta Lashe Gasar Firimiya Bayan Shekara 22
  • Leadership Hausa
    Bukatar Kawo Karshen Akidar Kyamar Baki A Kasar Afirka Ta Kudu

MASU ALAKA

makarfi
Tambarin Dimokuradiyya

Ci-ma-zaunen Ƴan Siyasa Ne Ke Tunanin Yin Maguɗi A Zaɓen 2027 – Makarfi

June 26, 2026
Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni
Tambarin Dimokuradiyya

An Samu Ruɗani Kan Rashin Bayyana Jerin Ƴan Takarar Jam’iyyun Siyasa Na Zaɓen 2027

June 26, 2026
Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku
Tambarin Dimokuradiyya

Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku

June 19, 2026
Next Post
Harin Sama Na Amurka Mataki Na Farko Ne Na Dakatar Da Ta’addanci A Nijeriya — Moore

Harin Sama Na Amurka Mataki Na Farko Ne Na Dakatar Da Ta’addanci A Nijeriya — Moore

LABARAI MASU NASABA

FIFA Ta Dakatar Da Aiwatar Da Hukuncin Hana Folarin Balogun Buga Wasa

FIFA Ta Dakatar Da Aiwatar Da Hukuncin Hana Folarin Balogun Buga Wasa

July 5, 2026
Sabbin Shaidu Sun Bulla Dake Kara Tabbatar Da Ta’asar Amfani Da Sinadarai Masu Guba Yayin Da Dakarun Japan Ke Mamaya A Sassan Kasar Sin

Sabbin Shaidu Sun Bulla Dake Kara Tabbatar Da Ta’asar Amfani Da Sinadarai Masu Guba Yayin Da Dakarun Japan Ke Mamaya A Sassan Kasar Sin

July 5, 2026
Matsalar Tsaro: Gwamnatin Tarayya Ta Nemi Taimakon Ƙasashen Waje

Yajin Aiki: Ƙungiyar Likitocin Nijeriya Ta Ba Gwamnati Wa’adin Mako Huɗu

July 5, 2026
An Gabatar Da Littafin “Bayanan Xi Jinping Kan Basirar Gudanar Da Ayyuka A Kananan Hukumomi”

An Gabatar Da Littafin “Bayanan Xi Jinping Kan Basirar Gudanar Da Ayyuka A Kananan Hukumomi”

July 5, 2026
Ko Kafa Ƴansandan Jihohi Zai Taimaka Wajen Kawo Ƙarshen Matsalolin Tsaro?

Ko Kafa Ƴansandan Jihohi Zai Taimaka Wajen Kawo Ƙarshen Matsalolin Tsaro?

July 5, 2026
Rashin Tarbiyya Da Ilimin Addini Ne Ke Sa Matasa Ɗaukar Doka a Hannu – Hon. Aminu Adam

Rashin Tarbiyya Da Ilimin Addini Ne Ke Sa Matasa Ɗaukar Doka a Hannu – Hon. Aminu Adam

July 5, 2026
Kayayyakin Sin Sun Jawo Hankalin Sassan Kasa Da Kasa

Kayayyakin Sin Sun Jawo Hankalin Sassan Kasa Da Kasa

July 5, 2026
Sin Da Rasha Za Su Gudanar Da Atisayen Sojojin Ruwa Da Sintiri Na Hadin Gwiwa

Sin Da Rasha Za Su Gudanar Da Atisayen Sojojin Ruwa Da Sintiri Na Hadin Gwiwa

July 5, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan ‘Ƴan Nijeriya 2 A Afrika Ta Kudu

Gwamnatin Tarayya Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan ‘Ƴan Nijeriya 2 A Afrika Ta Kudu

July 5, 2026
Tawagar Jami’an Lafiya Ta Sin Ta Kafa Cibiyar Horar Da Ma’aikatan Jinya A Saliyo

Tawagar Jami’an Lafiya Ta Sin Ta Kafa Cibiyar Horar Da Ma’aikatan Jinya A Saliyo

July 5, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.