ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, September 11, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

SDP Ta Gargadi INEC Kan Yin Katsalandan A Harkokin Jam’iyyar

by Leadership Hausa
9 months ago

Jam’iyyar SDP ta gargadi hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC) kan yin katsalandan a cikin harkokinta, tana mai jaddada cewa jam’iyyar ce kawai za ta iya yanke hukunci kan harkokinta na cikin gida.

Jam’iyyar ta yi maraba da hukuncin kotun koli da ta ki amincewa da shari’ar da INEC ta shigar kan rikicin shugabancinta, inda ta bayyana wannan hukunci a matsayin babban nasara ga dimokuradiyya da ‘yancin jam’iyya da kuma bin dokar kasa.

  • Sheikh Al-Sudais Ya Gargadi Masu Ibadah Kan Kiyaye Darajar Masallatan Harami
  • An Yi Bikin Murnar Cika Shekaru 15 Da Kafuwar Asibitin Abota Na Sin Da Ghana

A cikin hukuncin da ta yanke a ranar Jumma’a, kotun koli ta ki amincewa da korafin INEC na kalubalantar shugabancin SDP kuma ta umarci biyan naira miliyan 2 a matsayin kudin tara ga hukumar. Kotun koli ta bayyana korafin a matsayin wanda bai dace ba kuma ya saba wa doka.

ADVERTISEMENT

INEC ta nemi a soke hukuncin 17 ga Oktoba na kotun daukaka kara da ke Abuja, wanda ya tabbatar da hukuncin babban kotun tarayya wanda ya tilasta wa hukumar ta amince da kuma hada ‘yan takarar SDP a zabukan cike gurbi a jihohi 12.

A yayin da yake magana a taron manema labarai a shalkwatar jam’iyya da ke Abuja bayan yanke hukuncin, mukaddashin shugaban jam’iyyar SDP na kasa, Sadik Gombe, ya ce hukuncin kotun kolin ya tabbatar da matsayin shari’a da aka dade ana yi da cewa harkokin cikin gida na jam’iyyu bai kamata a samu tsoma baki daga waje ba.

LABARAI MASU NASABA

2027: APC Na Fuskantar Matsin Lamba Kan Sake Fasalin Tawagar Yakin Neman Zabe

Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin APC Da ‘Yan Adawa Kan Tallafin Gwamnatin Tarayya Ga Magidanta

“Wannan hukuncin yana da matukar muhimmanci, ba wai ga SDP kadai ba, har ma ga dukkan jam’iyyun siyasa a Nijeriya. Yana tabbatar da matsayin kotun koli na cewa al’amuran cikin gida na jam’iyyun siyasa, jam’iyyun ne kadai za su yanke hukunci a kai,” in ji shi.

Gombe ya bukaci INEC ta cika hukuncin gaba daya ta hanyar ba wa jam’iyyun siyasa damar gudanar da harkokinsu na ciki bisa tsarin kundinsu. Har ila yau, ya yi kira ga jam’iyyun da su kiyaye dabi’a na ciki gida da bin tsarin da ya dace.

“Muna godiya wa bangaren shari’a. Muna fatan wannan hukunci zai kara karfafa dimokuradiyyarmu da dokar kasa yayin da muke tukarar zaben 2027. Mun fahimci damuwarsu da sha’awarsu, duk da haka adalci dole ne ko da yaushe ya yi rinjayi. Muna sa ran INEC daga yanzu za ta daina tsoma baki a cikin harkokin cikin gida na jam’iyyun siyasa, domin wannan batun tun da farko kotun koli ta yanke hukunci tare da warware zare da abawa. Hukumar kuma dole ta daina duk wani mu’amala da mambobi da aka dakatar ko aka kore daga jam’iyya kuma ta amince nan take da sauya shugabancin mukaddashin jam’iyyar na kasa Shehu Gabam,” in ji shi.

A yayin mayar da martani ga hukuncin, babban lauya na SDP kuma dan takarar jam’iyyar na shugaban kasa a 2023, Adewole Adebayo, ya ce hukuncin ya aika da gargadi a fili ga INEC da ta guji ayyukan da za su iya raunana dimokuradiyyar jam’iyyun siyasa da dama a Nijeriya.

“Na bayyana wa INEC cewa su daina tsoma baki a harkokin ciki na SDP da sauran jam’iyyun siyasa. Dimokiradiyyar jam’iyyun da dama na bukatar alkalin da ba ya nuna bambanci ba, ba wanda ke haddasa rikice-rikice a cikin jam’iyyun adawa,” in ji Adebayo.

Adebayo ya bayyana cewa rikicin ya taso ne bayan jam’iyyar ta nada shugaban jam’iyyar na kasa na wucin gadi wanda ta rubuta wa INEC don tatace ‘yan takara, inda hukumar ta ki amincewa da shi, ta zabi ma ta yi mu’amala da shugaban da jam’iyyar ta riga ta kora.

Jam’iyyar ta tabbatar da cewa hukuncin kotun koli ya kara karfafa mata kwarin gwiwa tare da una cewa kotu ba ta yarda da tsoma baki daga hukumomin tsara dokoki cikin harkokin cikin gida na jam’iyyun siyasa ba.

Leadership Hausa
Website |  + postsBio
  • Leadership Hausa
    Wane Ne Dan Shagamu: Su Wane Ne Suka Kashe Shi A Kano?
  • Leadership Hausa
    An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu
  • Leadership Hausa
    Karuwar Farin Jinin Gwamna Umaru Bago A Siyasar Jihar Neja
  • Leadership Hausa
    Kyakkyawan Tsarin Laken Asiri Zai Dakile Shirin Magudin Zabe A Nijeriya —Mohammed

MASU ALAKA

2027: APC Na Fuskantar Matsin Lamba Kan Sake Fasalin Tawagar Yakin Neman Zabe
Tambarin Dimokuradiyya

2027: APC Na Fuskantar Matsin Lamba Kan Sake Fasalin Tawagar Yakin Neman Zabe

September 5, 2026
Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin APC Da ‘Yan Adawa Kan Tallafin Gwamnatin Tarayya Ga Magidanta
Tambarin Dimokuradiyya

Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin APC Da ‘Yan Adawa Kan Tallafin Gwamnatin Tarayya Ga Magidanta

September 4, 2026
Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?
Tambarin Dimokuradiyya

INEC Ta Zayyano Kalubalen Da Ke Iya Shafar Sahihancin Zaben 2027

August 28, 2026
Next Post
Harin Sama Na Amurka Mataki Na Farko Ne Na Dakatar Da Ta’addanci A Nijeriya — Moore

Harin Sama Na Amurka Mataki Na Farko Ne Na Dakatar Da Ta’addanci A Nijeriya — Moore

LABARAI MASU NASABA

Dalilin Da Ya Sa Ba Zan Janye Wa Atiku Ba A Zaɓen 2027 – Peter Obi

September 11, 2026
Farashin Siminti Zai Ragu Idan Farashin Kayan Aiki Ya Sauka – BUA

Gwarzon Shekarar 2026 Abdulsamad Rabiu

September 11, 2026
Cutar Kwalara Na Ci Gaba Da Yi Wa ‘Yan Nijeriya Kisan Mummuƙe

Buƙatar Ɗaukar Matakan Daƙile Yaɗuwar Cutar Mashaƙo A Nijeriya

September 11, 2026
Ding Xuexiang Ya Halarci Taron Kolin CIFTIS Tare Da Ganawa Da Manyan Jami’an Kasashen Waje

Ding Xuexiang Ya Halarci Taron Kolin CIFTIS Tare Da Ganawa Da Manyan Jami’an Kasashen Waje

September 10, 2026
Sin Ce Ta Zo Ta Farko A Rahoton Yanayin Tsaron Jama’a Na Duniya

Sin Ce Ta Zo Ta Farko A Rahoton Yanayin Tsaron Jama’a Na Duniya

September 10, 2026
Sin Ta Ciri Tuta Game Da Rawar Gani Da Take Takawa A Fannin Warware Kalubalen Tsaro A Gabas Ta Tsakiya

Sin Ta Ciri Tuta Game Da Rawar Gani Da Take Takawa A Fannin Warware Kalubalen Tsaro A Gabas Ta Tsakiya

September 10, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Gwangwaje Tawagar Kwallon Kwando Ta Mata Da Dala 100,000 Kowace

Gwamnatin Tarayya Ta Gwangwaje Tawagar Kwallon Kwando Ta Mata Da Dala 100,000 Kowace

September 10, 2026
Sin Da Amurka Na Gudanar Da Tattaunawa Dangane Da Yiwuwar Rage Harajin Ramuwar Gayya Wanda Darajarsa Ka Iya Kaiwa Dala Biliyan 30

Sin Da Amurka Na Gudanar Da Tattaunawa Dangane Da Yiwuwar Rage Harajin Ramuwar Gayya Wanda Darajarsa Ka Iya Kaiwa Dala Biliyan 30

September 10, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Dakatar da Shirin Ƙara Kuɗin Jarabawar WAEC da NECO

Gwamnatin Tarayya Za Ta Rika Bai Wa Ɗalibai 100MB Na Data Kyauta Kullum

September 10, 2026
Sin Da Amurka Na Wanzar Da Mu’amala Game Da Shirin Ganawar Da Manyan Shugabannin Kasashen Biyu Za Su Yi A Bana

Sin Da Amurka Na Wanzar Da Mu’amala Game Da Shirin Ganawar Da Manyan Shugabannin Kasashen Biyu Za Su Yi A Bana

September 10, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.