Mataimakin ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar NDC a zaɓen 2027, Sanata Rabiu Kwankwaso, ya ce tsofaffin gwamnonin Kano, Malam Ibrahim Shekarau da Abdullahi Ganduje, da kuma Gwamna Abba Yusuf, sun kai ƙarshen siyasarsu a jihar. Kwankwaso ya bayyana hakan ne yayin wata tattaunawa da Kamfanin Dillancin Labarai na ƙasa (NAN) a Abuja, inda ya yi tsokaci kan makomar wasu tsofaffin abokan siyasarsa da suka raba gari.
Kwankwaso ya ce nasarar siyasa da aka gina bisa “cin amana” ba ta dawwama, yana mai cewa gogewarsa cikin sama da shekaru 25 ta nuna masa cewa ’yan siyasar da suka ci amanar abokan hulɗarsu kan rasa tasirinsu daga baya. Ya bayar da Ganduje a matsayin misali, yana cewa tsohon gwamnan ya yi aiki tare da shi na tsawon shekaru takwas a matsayin mataimaki kafin ya zama gwamna a 2015, amma daga lokacin da suka fara samun saɓani ne, a cewarsa, matsalolin siyasarsa suka fara.
Ya ce da Ganduje ya ci gaba da kasancewa cikin tsarin siyasar da suka gina tare, da ya samu ƙarin karɓuwa a Kano da sauran sassan ƙasar. Kwankwaso ya kuma soki Gwamna Abba Yusuf, yana zarginsa da nisantar mutanen da suka yi aiki domin ganin ya zama gwamna. Ya ce tsarinsu na Kwankwasiyya ya yi aiki tuƙuru wajen tabbatar da zaɓen Gwamna Yusuf a matsayin ɗan takara domin guje wa maimaita abin da ya ce ya faru tsakaninsa da Ganduje.
Kwankwaso ya ce Kwankwasiyya ta sake taimaka wa Abba Kabir wajen samun nasara a zaɓen 2023, amma daga baya gwamnan ya nisanta kansa daga ɗariƙar. Ya ce Gwamna Abba ba ya tare da Ganduje kai tsaye, amma kuma ya ƙi a kira shi da “Dan Gandujiyya”, yana mai cewa yunƙurin gwamnan na neman zama babban jigon siyasa a Kano na iya haifar masa da matsaloli. Ya kuma bayyana cewa rikicin neman gado da ikon siyasa ba sabon abu ba ne a Kano ko Nijeriya.
Da yake magana kan sauyin dangantakar ’yan siyasa, Kwankwaso ya tuna da wata tattaunawa da Shugaba Bola Tinubu, inda ya ce shugaban ya taɓa roƙonsa ya sasanta da Ganduje.
Kwankwaso ya ce ya tunatar da Tinubu kan wasu tsofaffin abokan siyasarsa da suka taɓa kasancewa kusa da shi amma daga baya suka rasa tasirinsu, ciki har da tsohon mataimakin gwamnan Legas, Kofoworola Bucknor-Akerele, da tsohon gwamnan Legas, Akinwunmi Ambode. Sai dai ya ce har yanzu yana ɗaukar tsohon gwamnan Osun, Bisi Akande, a matsayin ɗaya daga cikin abokan siyasarsa na kusa.














