Shugaban Kasa Bola Tinubu, ya karrama Shugaban Hukumar Kula da Tashoshin Jiragen Ruwa na Kasa NPA Dakta Abubakar Dantsoho, ta lambar yabo ta musamman bisa gudunmawar da ya ke ci gaba da bayarwa wajen samar da kyawan sauye-sauye, a fannin sufurin Jiragen Ruwa na ƙasar nan.
Tinubu ya karrama Dantsoho da lambar yabon ta musamman ne, kan samar da kayan aiki na zamani a Tashoshin Jiragen Ruwa na kasar wadanda kuma suka yi daidai, da na fadin duniya, musamman duba da cecewa, samar da kayan aikin, za su kara samar da gasa.
- Shugaban NPA Ya Bukaci A Yi Hadaka Domin Cin Gajiyar Albarkatun Fannin Sufurin Afirka
- An Jinjina Wa Shugaban NPA Kan Rage Cunkoso A Tashar Apapa
Ya karbi lambar yabon ta NEAPS a taron da aka gudanar a fadar shugaban kasa da ke Abuja, a ranar Lahadin da ta gabata.
Lambar girman ta. NEAPS wani shiri ne, fadar shugaban kasa, da ofishin Sakataren Gwamnatin Tarayya, ke tafiyar da shi wanda ake zabo zakakuran manyan ma’aikatan Gwamnatin Tarayya, da suka nuna kwarewa da bajinta,musamman wajen yin amfani da kimiyyar fasahar zamani, wajen tafiyar da ma’aikatun da suke jagoranta.
A cikin sanarwar da Hukumar ta NPA ta fitar, ta bayyana cewa, an karrma Dantsoho da lambar yabon ne, domin bunkasa fannin na sufurin Jiragen Ruwa na kasar.
“An zabo Abubakar Dantsoho ne, daga cikin sauran wadanda aka karamma da lambar yabon bisa kokarin da yake ci gaba da yi, na bunkasa fannin sufurin Jiragen Ruwa na kasar wanda hakan ya sanya, aka kara samun fitar da kaya daga kasar nan, ta hanyar Tashoshin Jiragen Ruwa na kasa dIMODantsohoa tsarin NSW ta hanyar yin amfani da dabarar PCS domin janyo ra’ayin masu zuba jari daga ketare a Tashoshin Jiragen Ruwa na kasar nan, da aka samar da kayan aiki na zamani, ” Inji sanarwar.
“Akawi kuma batun kara daga darajar Tashoshin Jiragen Ruwa na kasar a tsakanin hukumomin Jiragen Ruwa da ke a Afirka ta Yamma wato PMAWCA da kuma zabar Dantsoho, a matsayin mataimakin shugaban kungiyar masu tafiyar da hukumomin Jiragen Ruwa na kasa da kasa wato IAPH,” A cewar sanarwar.
Hukumar ta NPA ta bayyana cewa, a karkashin shugabancin Dantsoho tare da taimakawar ministan bunkasa tattalin arziki na teku Adegboyega Oyetola, an sake zabar Nijeriya, zuwa mataki na C a karkashin kungiyar kasa da kasa ta tafiyar da harkar sufurin Jiragen Ruwa wato IMO.














