Hukumar Jin Daɗin Alhazai Musulmi ta Jihar Bauchi ta sanar da rasuwar ɗaya daga cikin jami’an kula da jin daɗin alhazan jihar, Alhaji Shehu Yahaya Jalam, a asibitin Al-Noor da ke Makkah a ƙasar Saudiyya, bayan fama da gajeruwar rashin lafiya.
Kafin rasuwarsa, marigayin ya kasance shugaban kwamitin yaɗa labarai da hulɗa da jama’a na aikin Hajjin 2026, sannan kuma babban Sakatare (permanent secretary) ne a ofishin sakataren Gwamnatin Jihar Bauchi (SSG).
Marigayin ya taka muhimmiyar rawa wajen raba masauƙin alhazan jihar Bauchi a lokacin gudanar da aikin Hajjin bana a ƙasar Saudiyya. Haka kuma marigayin Shehu ya jagoranci harkokin ciyar da alhazan jihar Bauchi, inda ya kasance sakataren kwamitin ciyarwa.
Jalam ya rasu ne a daren ranar Asabar bayan gajeruwar rashin lafiya yayin da yake ci gaba da gudanar da ayyukan kula da jin daɗin alhazan jihar.
A wata hira ta wayar tarho da wakilinmu daga Saudiyya, tsohon daraktan ayyuka na hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Bauchi, kuma ɗaya daga cikin masu kula da aikin Hajjin 2026 na jihar, Alhaji Sabiu Barau Ningi, ya tabbatar da rasuwar Jalam.Ningi wanda babban sakatare (PS) ne a ofishin mataimakin gwamnan jihar Bauchi, ya ƙara da cewa, “Ya rasu ne sakamakon gajeruwar rashin lafiya. Tun bayan sauƙarsu a Madina ya ɗan koka wa abokan zama cewa baya jin dadi to kuma ya je asibiti a Madina an duba shi an ba shi magani.”
To sun dawo sun ci gaba da aikinsu. Ka san shi cikin tawagar farko (advance team) tun ma kafin alhazan jiha su iso Makka, su sun iso Makka kuma sun zo sun ci gaba da aiki har jirgin ƙarshe wanda ya shigo daren shekaran jiya ke nan.
Cikin hukuncin Allah sun raba wa kowa ɗakuwa cikin hukuncin Allah daman na cikin waɗanda suka shugabanci kwamitin rabon ɗakuna wa alhazai to sun raba duk ɗakuna sun bai wa kowani Alhaji har da muma officials duk shi ya raba mana ɗakuna.
Ningi ya kuma bayyana cewa daga baya rashin lafiyar marigayin ta tsananta, inda aka mayar da shi sashen kulawa ta musamman (ICU) na wani asibiti a Makkah, inda daga bisani ya rasu a daren Asabar.
“Alhaji Shehu Yahaya Jalam ya rasu jiya da misalin ƙarfe 2:00 na dare agogon Saudiyya, wanda ya yi daidai da ƙarfe 12:00 na dare agogon Nijeriya, a Asibitin Al-Noor da ke Makkah,” in ji jami’in kula da aikin Hajjin.
Ya ce Babban Sakataren Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Bauchi, Imam Abdurrahman Ibrahim Idris, ya sanar da Hukumar Alhazai ta Ƙasa (NAHCON), kuma ana ci gaba da shirye-shiryen jana’izarsa a Masallacin Harami da ke Makkah.
Ya ce rashin lafiyar da suka fi tunanin ita ce ta yi ajalin mamacin ita ce bugun zuciya saboda daman marigayin na kan shan maganin hawan jini. Ya bayyana marigayin Shehu Jalam a matsayin ɗaya daga cikin jami’an da suka fi sadaukar da kai wajen hidimtawa alhazan jihar Bauchi, tare da yabawa jajircewarsa, ƙarfin hali da rashin son kai.
“Mun yi rashin mutum mai ƙwazo da sadaukarwa wanda ya sadaukar da rayuwarsa wajen tabbatar da jin daɗi da walwalar alhazan Bauchi,” in ji Ningi.
Ya miƙa ta’aziyyarsa ga Gwamnan Jihar Bauchi, Sanata Bala Mohammed, iyalan mamacin, al’ummar masarautar Jalam da ƙaramar hukumar Dambam, al’ummar jihar Bauchi, Amirul Hajjin Bauchi na 2026 da Sarkin Misau, Alhaji Ahmad Sulaiman, bisa wannan babban rashi.
Ya kara da cewa a da shekarun baya marigayi Shehu Jalam ya kasance mai zuwa aikin hajji domin hidimta wa alhazzai a matsayin ɗan sa-kai inda hakan ya sa gwamnan jihar Bala Muhammad ya lura da ƙoƙarinsa tare da jawo shi cikin kwamiti kula da jin dadin alhazzai na jihar.
Ya yi addu’ar Allah Madaukakin Sarki Ya gafarta masa kura-kuransa, Ya karɓi ayyukansa na alheri, Ya ba shi Aljannatul Firdausi, sannan Ya bai wa iyalansa, abokan aikinsa da daukacin tawagar aikin Hajjin 2026 juriyar wannan babban rashi.
“Allah Ya sanya kabarinsa ya zama ɗaya daga cikin lambunan Aljanna.”















Discussion about this post