ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shugaban Kwamitin Yaɗa Labarai Na Aikin Hajjin Bana Na Bauchi Ya Rasu A Saudiyya

by Khalid Idris Doya and Sulaiman
3 weeks ago
Aikin hajji

Hukumar Jin Daɗin Alhazai Musulmi ta Jihar Bauchi ta sanar da rasuwar ɗaya daga cikin jami’an kula da jin daɗin alhazan jihar, Alhaji Shehu Yahaya Jalam, a asibitin Al-Noor da ke Makkah a ƙasar Saudiyya, bayan fama da gajeruwar rashin lafiya.

Kafin rasuwarsa, marigayin ya kasance shugaban kwamitin yaɗa labarai da hulɗa da jama’a na aikin Hajjin 2026, sannan kuma babban Sakatare (permanent secretary) ne a ofishin sakataren Gwamnatin Jihar Bauchi (SSG).

Marigayin ya taka muhimmiyar rawa wajen raba masauƙin alhazan jihar Bauchi a lokacin gudanar da aikin Hajjin bana a ƙasar Saudiyya. Haka kuma marigayin Shehu ya jagoranci harkokin ciyar da alhazan jihar Bauchi, inda ya kasance sakataren kwamitin ciyarwa.

ADVERTISEMENT

Jalam ya rasu ne a daren ranar Asabar bayan gajeruwar rashin lafiya yayin da yake ci gaba da gudanar da ayyukan kula da jin daɗin alhazan jihar.

A wata hira ta wayar tarho da wakilinmu daga Saudiyya, tsohon daraktan ayyuka na hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Bauchi, kuma ɗaya daga cikin masu kula da aikin Hajjin 2026 na jihar, Alhaji Sabiu Barau Ningi, ya tabbatar da rasuwar Jalam.Ningi wanda babban sakatare (PS) ne a ofishin mataimakin gwamnan jihar Bauchi, ya ƙara da cewa, “Ya rasu ne sakamakon gajeruwar rashin lafiya. Tun bayan sauƙarsu a Madina ya ɗan koka wa abokan zama cewa baya jin dadi to kuma ya je asibiti a Madina an duba shi an ba shi magani.”

LABARAI MASU NASABA

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Gwamnatin Zamfara Ta Shirya Tallafa Wa Mata Da Masu Ƙaramin Ƙarfi Fiye Da Miliyan Ɗaya

To sun dawo sun ci gaba da aikinsu. Ka san shi cikin tawagar farko (advance team) tun ma kafin alhazan jiha su iso Makka, su sun iso Makka kuma sun zo sun ci gaba da aiki har jirgin ƙarshe wanda ya shigo daren shekaran jiya ke nan.

Cikin hukuncin Allah sun raba wa kowa ɗakuwa cikin hukuncin Allah daman na cikin waɗanda suka shugabanci kwamitin rabon ɗakuna wa alhazai to sun raba duk ɗakuna sun bai wa kowani Alhaji har da muma officials duk shi ya raba mana ɗakuna.

Ningi ya kuma bayyana cewa daga baya rashin lafiyar marigayin ta tsananta, inda aka mayar da shi sashen kulawa ta musamman (ICU) na wani asibiti a Makkah, inda daga bisani ya rasu a daren Asabar.

“Alhaji Shehu Yahaya Jalam ya rasu jiya da misalin ƙarfe 2:00 na dare agogon Saudiyya, wanda ya yi daidai da ƙarfe 12:00 na dare agogon Nijeriya, a Asibitin Al-Noor da ke Makkah,” in ji jami’in kula da aikin Hajjin.

Ya ce Babban Sakataren Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Bauchi, Imam Abdurrahman Ibrahim Idris, ya sanar da Hukumar Alhazai ta Ƙasa (NAHCON), kuma ana ci gaba da shirye-shiryen jana’izarsa a Masallacin Harami da ke Makkah.

Ya ce rashin lafiyar da suka fi tunanin ita ce ta yi ajalin mamacin ita ce bugun zuciya saboda daman marigayin na kan shan maganin hawan jini. Ya bayyana marigayin Shehu Jalam a matsayin ɗaya daga cikin jami’an da suka fi sadaukar da kai wajen hidimtawa alhazan jihar Bauchi, tare da yabawa jajircewarsa, ƙarfin hali da rashin son kai.

“Mun yi rashin mutum mai ƙwazo da sadaukarwa wanda ya sadaukar da rayuwarsa wajen tabbatar da jin daɗi da walwalar alhazan Bauchi,” in ji Ningi.

Ya miƙa ta’aziyyarsa ga Gwamnan Jihar Bauchi, Sanata Bala Mohammed, iyalan mamacin, al’ummar masarautar Jalam da ƙaramar hukumar Dambam, al’ummar jihar Bauchi, Amirul Hajjin Bauchi na 2026 da Sarkin Misau, Alhaji Ahmad Sulaiman, bisa wannan babban rashi.

Ya kara da cewa a da shekarun baya marigayi Shehu Jalam ya kasance mai zuwa aikin hajji domin hidimta wa alhazzai a matsayin ɗan sa-kai inda hakan ya sa gwamnan jihar Bala Muhammad ya lura da ƙoƙarinsa tare da jawo shi cikin kwamiti kula da jin dadin alhazzai na jihar.

Ya yi addu’ar Allah Madaukakin Sarki Ya gafarta masa kura-kuransa, Ya karɓi ayyukansa na alheri, Ya ba shi Aljannatul Firdausi, sannan Ya bai wa iyalansa, abokan aikinsa da daukacin tawagar aikin Hajjin 2026 juriyar wannan babban rashi.

“Allah Ya sanya kabarinsa ya zama ɗaya daga cikin lambunan Aljanna.”

Aikin hajji
Khalid Idris Doya
+ posts Bio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Zaɓen Fidda Gwani Na Gwamna: Ba Za Mu Lamunci Kaƙaba Mana Ɗan Takara A Bauchi Ba – Mambobin APC
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Sanata Buba Ya Janye Daga Takarar Fidda Gwani Ta Gwamnan APC A Bauchi, Ya Zargi Cewa ‘Ɗauki Ɗaura Ake Yi Ba Zaɓe Ba”
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Na Bar Harƙoƙin Siyasa Gaba Ɗaya – Ɗan Takarar Gwamnan Bauchi, Air Marshal Saddique Baba
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Gwamna Bala Ya Sayi Fom Ɗin Takarar Sanatan Bauchi ta Kudu A Jam’iyyar APM
Aikin hajji
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo
  • Sulaiman
    Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli
  • Sulaiman
    Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus
  • Sulaiman
    ’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

MASU ALAKA

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro
Manyan Labarai

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Zamfara Ta Shirya Tallafa Wa Mata Da Masu Ƙaramin Ƙarfi Fiye Da Miliyan Ɗaya
Manyan Labarai

Gwamnatin Zamfara Ta Shirya Tallafa Wa Mata Da Masu Ƙaramin Ƙarfi Fiye Da Miliyan Ɗaya

June 3, 2026
Kotu Ta Yanke Wa Waɗanda Suka Kai Hari Cocin Owo Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya
Manyan Labarai

Kotu Ta Yanke Wa Waɗanda Suka Kai Hari Cocin Owo Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya

June 3, 2026
Next Post
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

Zaɓen Fidda Gwani na APC: ‘Yan Majalisar Wakilai 12 da Suka Rasa Tikitin Komawa Takara

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026
Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

June 3, 2026
An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Magadan Gari Na 2026 A Beijing

An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Magadan Gari Na 2026 A Beijing

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.