ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Tuesday, July 14, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shugaban Kwamitin Yaɗa Labarai Na Aikin Hajjin Bana Na Bauchi Ya Rasu A Saudiyya

by Khalid Idris Doya and Sulaiman
2 months ago
Aikin hajji

Hukumar Jin Daɗin Alhazai Musulmi ta Jihar Bauchi ta sanar da rasuwar ɗaya daga cikin jami’an kula da jin daɗin alhazan jihar, Alhaji Shehu Yahaya Jalam, a asibitin Al-Noor da ke Makkah a ƙasar Saudiyya, bayan fama da gajeruwar rashin lafiya.

Kafin rasuwarsa, marigayin ya kasance shugaban kwamitin yaɗa labarai da hulɗa da jama’a na aikin Hajjin 2026, sannan kuma babban Sakatare (permanent secretary) ne a ofishin sakataren Gwamnatin Jihar Bauchi (SSG).

Marigayin ya taka muhimmiyar rawa wajen raba masauƙin alhazan jihar Bauchi a lokacin gudanar da aikin Hajjin bana a ƙasar Saudiyya. Haka kuma marigayin Shehu ya jagoranci harkokin ciyar da alhazan jihar Bauchi, inda ya kasance sakataren kwamitin ciyarwa.

ADVERTISEMENT

Jalam ya rasu ne a daren ranar Asabar bayan gajeruwar rashin lafiya yayin da yake ci gaba da gudanar da ayyukan kula da jin daɗin alhazan jihar.

A wata hira ta wayar tarho da wakilinmu daga Saudiyya, tsohon daraktan ayyuka na hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Bauchi, kuma ɗaya daga cikin masu kula da aikin Hajjin 2026 na jihar, Alhaji Sabiu Barau Ningi, ya tabbatar da rasuwar Jalam.Ningi wanda babban sakatare (PS) ne a ofishin mataimakin gwamnan jihar Bauchi, ya ƙara da cewa, “Ya rasu ne sakamakon gajeruwar rashin lafiya. Tun bayan sauƙarsu a Madina ya ɗan koka wa abokan zama cewa baya jin dadi to kuma ya je asibiti a Madina an duba shi an ba shi magani.”

LABARAI MASU NASABA

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

Tsohon Sanatan Gombe, Bayero Nafada, Ya Fice Daga PDP Bayan Ganawa da Shugabannin APC

To sun dawo sun ci gaba da aikinsu. Ka san shi cikin tawagar farko (advance team) tun ma kafin alhazan jiha su iso Makka, su sun iso Makka kuma sun zo sun ci gaba da aiki har jirgin ƙarshe wanda ya shigo daren shekaran jiya ke nan.

Cikin hukuncin Allah sun raba wa kowa ɗakuwa cikin hukuncin Allah daman na cikin waɗanda suka shugabanci kwamitin rabon ɗakuna wa alhazai to sun raba duk ɗakuna sun bai wa kowani Alhaji har da muma officials duk shi ya raba mana ɗakuna.

Ningi ya kuma bayyana cewa daga baya rashin lafiyar marigayin ta tsananta, inda aka mayar da shi sashen kulawa ta musamman (ICU) na wani asibiti a Makkah, inda daga bisani ya rasu a daren Asabar.

“Alhaji Shehu Yahaya Jalam ya rasu jiya da misalin ƙarfe 2:00 na dare agogon Saudiyya, wanda ya yi daidai da ƙarfe 12:00 na dare agogon Nijeriya, a Asibitin Al-Noor da ke Makkah,” in ji jami’in kula da aikin Hajjin.

Ya ce Babban Sakataren Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Bauchi, Imam Abdurrahman Ibrahim Idris, ya sanar da Hukumar Alhazai ta Ƙasa (NAHCON), kuma ana ci gaba da shirye-shiryen jana’izarsa a Masallacin Harami da ke Makkah.

Ya ce rashin lafiyar da suka fi tunanin ita ce ta yi ajalin mamacin ita ce bugun zuciya saboda daman marigayin na kan shan maganin hawan jini. Ya bayyana marigayin Shehu Jalam a matsayin ɗaya daga cikin jami’an da suka fi sadaukar da kai wajen hidimtawa alhazan jihar Bauchi, tare da yabawa jajircewarsa, ƙarfin hali da rashin son kai.

“Mun yi rashin mutum mai ƙwazo da sadaukarwa wanda ya sadaukar da rayuwarsa wajen tabbatar da jin daɗi da walwalar alhazan Bauchi,” in ji Ningi.

Ya miƙa ta’aziyyarsa ga Gwamnan Jihar Bauchi, Sanata Bala Mohammed, iyalan mamacin, al’ummar masarautar Jalam da ƙaramar hukumar Dambam, al’ummar jihar Bauchi, Amirul Hajjin Bauchi na 2026 da Sarkin Misau, Alhaji Ahmad Sulaiman, bisa wannan babban rashi.

Ya kara da cewa a da shekarun baya marigayi Shehu Jalam ya kasance mai zuwa aikin hajji domin hidimta wa alhazzai a matsayin ɗan sa-kai inda hakan ya sa gwamnan jihar Bala Muhammad ya lura da ƙoƙarinsa tare da jawo shi cikin kwamiti kula da jin dadin alhazzai na jihar.

Ya yi addu’ar Allah Madaukakin Sarki Ya gafarta masa kura-kuransa, Ya karɓi ayyukansa na alheri, Ya ba shi Aljannatul Firdausi, sannan Ya bai wa iyalansa, abokan aikinsa da daukacin tawagar aikin Hajjin 2026 juriyar wannan babban rashi.

“Allah Ya sanya kabarinsa ya zama ɗaya daga cikin lambunan Aljanna.”

Aikin hajji
Khalid Idris Doya
+ posts Bio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    ATBU Ta Janye Filin Ginin Masallaci Da Ta Bai wa TIMSAN, Ta Amince Kowa Ya Yi Addininsa Yadda Ya Fahimta
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ɗan Majalisar Dokokin Bauchi, Hon. Wanzam, Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Tsohon Mataimakin Gwamnan Bauchi, Audu Sule Katagum Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Kotu Ta Umarci DSS Ta Mutunta Umarninta Kan Shari’ar Filin Firo Na Bauchi
Aikin hajji
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026
  • Sulaiman
    An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”
  • Sulaiman
    Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu
  • Sulaiman
    Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

MASU ALAKA

Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga
Manyan Labarai

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
Tsohon Sanatan Gombe, Bayero Nafada, Ya Fice Daga PDP Bayan Ganawa da Shugabannin APC
Manyan Labarai

Tsohon Sanatan Gombe, Bayero Nafada, Ya Fice Daga PDP Bayan Ganawa da Shugabannin APC

July 14, 2026
Sojoji Sun Kashe ’Yan Ta’adda 3, Sun Ƙwato Makamai A Sakkwato
Manyan Labarai

Sojoji Sun Daƙile Harin ISWAP A Borno

July 14, 2026
Next Post
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

Zaɓen Fidda Gwani na APC: ‘Yan Majalisar Wakilai 12 da Suka Rasa Tikitin Komawa Takara

LABARAI MASU NASABA

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

July 14, 2026
Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

July 14, 2026
Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

July 14, 2026
CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

July 14, 2026
Tsohon Sanatan Gombe, Bayero Nafada, Ya Fice Daga PDP Bayan Ganawa da Shugabannin APC

Tsohon Sanatan Gombe, Bayero Nafada, Ya Fice Daga PDP Bayan Ganawa da Shugabannin APC

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.