Wasu daga cikin mambobin Majalisar Wakilai masu ci a yanzu sun gaza samun tikitin komawa takara a zaɓen fidda gwani na jam’iyyar APC da aka gudanar a faɗin ƙasar nan gabanin babban zaɓen shekarar 2027.
Daga cikin fitattun ‘yan majalisar da suka rasa tikitin akwai Jagoran Masu Rinjaye na Majalisar Wakilai, Julius Ihonvbere, wanda ƙoƙarinsa na neman wa’adi na uku a mazaɓar Owan ta Tarayya a Jihar Edo ya ci tura. Ya sha kaye ne a hannun tsohon Kwamishinan Ma’adinai, Andrew Ijegbai.
A Jihar Edo kuma, wani ɗan majalisa mai ci, Eseosa Iyawe, ya rasa tikitin APC na mazaɓar Oredo ta Tarayya ga tsohon Kwamishinan Ilimi, Dakta Paddy Iyamu.
Iyawe na daga cikin ‘yan majalisar da aka zaɓa a ƙarƙashin jam’iyyar Labour Party amma daga baya suka koma APC.
A Jihar Imo, mambobin majalisar wakilai guda huɗu masu ci sun rasa tikitin komawa takara.
Sun haɗa da Matthew Nwogu mai wakiltar Aboh Mbaise/Ngor Okpala, Miriam Onuoha ta Okigwe South, Harrison Nwadike mai wakiltar Isu/Njaba/Nkwerre/Nwangele, da Emeka Martins Chinedu na mazaɓar Ahiazu/Ezinihitte.Haka kuma, Ismail Kayode, mai wakiltar mazaɓar Ifelodun/Oyun/Offa ta Tarayya a Jihar Kwara, ya rasa tikitin APC ga tsohon Babban Sakataren Yaɗa Labarai na Gwamna AbdulRahman AbdulRazaq, Rafiu Ajakaye.
A Jihar Kebbi, ɗan majalisa mai ci Mansur Musa Jega ya rasa tikitin APC na mazaɓar Jega/Gwandu/Aleiro bayan wata yarjejeniyar maslaha da ta bai wa tsohon Kwanturola Janar na Hukumar Gyaran Hali ta Nijeriya, Jafar Ahmed Jega, tikitin.
Haka zalika, ‘yan majalisar wakilai guda huɗu masu ci a Jihar Jigawa sun rasa tikitin komawa takara yayin zaɓen fidda gwani.
Sun haɗa da Muktar Muhammad mai wakiltar Kazaure/Roni/Gwiwa/Yankwashi; Ibrahim Usman Auyo na Hadejia/Auyo/Kafin Hausa; Sa’adu Wada Taura mai wakiltar Ringim/Taura, da Yusif Sa’idu Miga na Jahun/Miga.















Discussion about this post