ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, July 17, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zaɓen Fidda Gwani na APC: ‘Yan Majalisar Wakilai 12 da Suka Rasa Tikitin Komawa Takara

by Sulaiman
2 months ago
Majalisa

Wasu daga cikin mambobin Majalisar Wakilai masu ci a yanzu sun gaza samun tikitin komawa takara a zaɓen fidda gwani na jam’iyyar APC da aka gudanar a faɗin ƙasar nan gabanin babban zaɓen shekarar 2027.

Daga cikin fitattun ‘yan majalisar da suka rasa tikitin akwai Jagoran Masu Rinjaye na Majalisar Wakilai, Julius Ihonvbere, wanda ƙoƙarinsa na neman wa’adi na uku a mazaɓar Owan ta Tarayya a Jihar Edo ya ci tura. Ya sha kaye ne a hannun tsohon Kwamishinan Ma’adinai, Andrew Ijegbai.

A Jihar Edo kuma, wani ɗan majalisa mai ci, Eseosa Iyawe, ya rasa tikitin APC na mazaɓar Oredo ta Tarayya ga tsohon Kwamishinan Ilimi, Dakta Paddy Iyamu.

ADVERTISEMENT

Iyawe na daga cikin ‘yan majalisar da aka zaɓa a ƙarƙashin jam’iyyar Labour Party amma daga baya suka koma APC.

A Jihar Imo, mambobin majalisar wakilai guda huɗu masu ci sun rasa tikitin komawa takara.

LABARAI MASU NASABA

Bayan Ceto Daliban Oyo: Kallo Ya Koma Borno Da Yobe

Batun Yawan Bashin Da Nijeriya Ke Ciyowa Daga Ketare

Sun haɗa da Matthew Nwogu mai wakiltar Aboh Mbaise/Ngor Okpala, Miriam Onuoha ta Okigwe South, Harrison Nwadike mai wakiltar Isu/Njaba/Nkwerre/Nwangele, da Emeka Martins Chinedu na mazaɓar Ahiazu/Ezinihitte.Haka kuma, Ismail Kayode, mai wakiltar mazaɓar Ifelodun/Oyun/Offa ta Tarayya a Jihar Kwara, ya rasa tikitin APC ga tsohon Babban Sakataren Yaɗa Labarai na Gwamna AbdulRahman AbdulRazaq, Rafiu Ajakaye.

A Jihar Kebbi, ɗan majalisa mai ci Mansur Musa Jega ya rasa tikitin APC na mazaɓar Jega/Gwandu/Aleiro bayan wata yarjejeniyar maslaha da ta bai wa tsohon Kwanturola Janar na Hukumar Gyaran Hali ta Nijeriya, Jafar Ahmed Jega, tikitin.

Haka zalika, ‘yan majalisar wakilai guda huɗu masu ci a Jihar Jigawa sun rasa tikitin komawa takara yayin zaɓen fidda gwani.

Sun haɗa da Muktar Muhammad mai wakiltar Kazaure/Roni/Gwiwa/Yankwashi; Ibrahim Usman Auyo na Hadejia/Auyo/Kafin Hausa; Sa’adu Wada Taura mai wakiltar Ringim/Taura, da Yusif Sa’idu Miga na Jahun/Miga.

Majalisa
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Pew: Sin Ta fi Amurka Samun Amincewar Al’ummun Duniya
  • Sulaiman
    Sin Ta Fitar Da Tsarin Sanya Ido Don Inganta Muhalli Da Muhallin Halittu Na Shekarar 2026 Zuwa 2030
  • Sulaiman
    Nazari Game Da Damammakin Da Sin Ta Samar Cikin Rahoton Ci Gaban Tattalin Arzikinta Na Rabin Farkon Shekara
  • Sulaiman
    Gwamna Bala Ya Rushe Kwamitin Gudanarwar Wikki Tourists Bayan Rashin Nasararta A Gasar NPFL

MASU ALAKA

Bayan Ceto Daliban Oyo: Kallo Ya Koma Borno Da Yobe
Manyan Labarai

Bayan Ceto Daliban Oyo: Kallo Ya Koma Borno Da Yobe

July 17, 2026
Batun Yawan Bashin Da Nijeriya Ke Ciyowa Daga Ketare
Manyan Labarai

Batun Yawan Bashin Da Nijeriya Ke Ciyowa Daga Ketare

July 17, 2026
Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu
Manyan Labarai

Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu

July 16, 2026
Next Post
Za A Gudanar Da Jadawalin Cancantar Shiga AFCON 2027 A Alkahira Ranar Talata

Za A Gudanar Da Jadawalin Cancantar Shiga AFCON 2027 A Alkahira Ranar Talata

LABARAI MASU NASABA

Mata Manoma Sun Gina Gada, Rijiyar Burtsatse A Danbare, Kano

Mata Manoma Sun Gina Gada, Rijiyar Burtsatse A Danbare, Kano

July 17, 2026
Yadda NDLEA Ke Fatattakar Dillalan Miyagun Kwayoyi Na Kudancin Amurka

Yadda NDLEA Ke Fatattakar Dillalan Miyagun Kwayoyi Na Kudancin Amurka

July 17, 2026
Gwamnan Da Bai Taba Samun Mulkin Jihar Kano Ba

Gwamnan Da Bai Taba Samun Mulkin Jihar Kano Ba

July 17, 2026
An Ceto Wasu Mutane Huɗu Da Aka Sace A Kogi

An Ceto Wasu Mutane Huɗu Da Aka Sace A Kogi

July 17, 2026
NPA Ta Tara Kudin Shiga Naira Biliyan 758.2 A 2024

Dalilin Da Ya Sa Kungiyar NCTR Ta Jinjina Wa Shugaban NPA

July 17, 2026
Yunkurin Dauda Lawal Na Bunkasa Bangaren Ma’adanan Jihar Zamfara

Yunkurin Dauda Lawal Na Bunkasa Bangaren Ma’adanan Jihar Zamfara

July 17, 2026
Gbajabiamila Ya Maka Daraktan Bogi Na PFIPC Kotu, Ya Nemi Diyyar Biliyan 15

Gbajabiamila Ya Maka Daraktan Bogi Na PFIPC Kotu, Ya Nemi Diyyar Biliyan 15

July 17, 2026
Bayan Ceto Daliban Oyo: Kallo Ya Koma Borno Da Yobe

Bayan Ceto Daliban Oyo: Kallo Ya Koma Borno Da Yobe

July 17, 2026
Batun Yawan Bashin Da Nijeriya Ke Ciyowa Daga Ketare

Batun Yawan Bashin Da Nijeriya Ke Ciyowa Daga Ketare

July 17, 2026
Pew: Sin Ta fi Amurka Samun Amincewar Al’ummun Duniya

Pew: Sin Ta fi Amurka Samun Amincewar Al’ummun Duniya

July 16, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.