ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zaɓen Fidda Gwani na APC: ‘Yan Majalisar Wakilai 12 da Suka Rasa Tikitin Komawa Takara

by Sulaiman
3 weeks ago
Majalisa

Wasu daga cikin mambobin Majalisar Wakilai masu ci a yanzu sun gaza samun tikitin komawa takara a zaɓen fidda gwani na jam’iyyar APC da aka gudanar a faɗin ƙasar nan gabanin babban zaɓen shekarar 2027.

Daga cikin fitattun ‘yan majalisar da suka rasa tikitin akwai Jagoran Masu Rinjaye na Majalisar Wakilai, Julius Ihonvbere, wanda ƙoƙarinsa na neman wa’adi na uku a mazaɓar Owan ta Tarayya a Jihar Edo ya ci tura. Ya sha kaye ne a hannun tsohon Kwamishinan Ma’adinai, Andrew Ijegbai.

A Jihar Edo kuma, wani ɗan majalisa mai ci, Eseosa Iyawe, ya rasa tikitin APC na mazaɓar Oredo ta Tarayya ga tsohon Kwamishinan Ilimi, Dakta Paddy Iyamu.

ADVERTISEMENT

Iyawe na daga cikin ‘yan majalisar da aka zaɓa a ƙarƙashin jam’iyyar Labour Party amma daga baya suka koma APC.

A Jihar Imo, mambobin majalisar wakilai guda huɗu masu ci sun rasa tikitin komawa takara.

LABARAI MASU NASABA

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Sun haɗa da Matthew Nwogu mai wakiltar Aboh Mbaise/Ngor Okpala, Miriam Onuoha ta Okigwe South, Harrison Nwadike mai wakiltar Isu/Njaba/Nkwerre/Nwangele, da Emeka Martins Chinedu na mazaɓar Ahiazu/Ezinihitte.Haka kuma, Ismail Kayode, mai wakiltar mazaɓar Ifelodun/Oyun/Offa ta Tarayya a Jihar Kwara, ya rasa tikitin APC ga tsohon Babban Sakataren Yaɗa Labarai na Gwamna AbdulRahman AbdulRazaq, Rafiu Ajakaye.

A Jihar Kebbi, ɗan majalisa mai ci Mansur Musa Jega ya rasa tikitin APC na mazaɓar Jega/Gwandu/Aleiro bayan wata yarjejeniyar maslaha da ta bai wa tsohon Kwanturola Janar na Hukumar Gyaran Hali ta Nijeriya, Jafar Ahmed Jega, tikitin.

Haka zalika, ‘yan majalisar wakilai guda huɗu masu ci a Jihar Jigawa sun rasa tikitin komawa takara yayin zaɓen fidda gwani.

Sun haɗa da Muktar Muhammad mai wakiltar Kazaure/Roni/Gwiwa/Yankwashi; Ibrahim Usman Auyo na Hadejia/Auyo/Kafin Hausa; Sa’adu Wada Taura mai wakiltar Ringim/Taura, da Yusif Sa’idu Miga na Jahun/Miga.

Majalisa
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo
  • Sulaiman
    Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli
  • Sulaiman
    Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus
  • Sulaiman
    ’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

MASU ALAKA

Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe
Siyasa

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro
Manyan Labarai

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Zamfara Ta Shirya Tallafa Wa Mata Da Masu Ƙaramin Ƙarfi Fiye Da Miliyan Ɗaya
Manyan Labarai

Gwamnatin Zamfara Ta Shirya Tallafa Wa Mata Da Masu Ƙaramin Ƙarfi Fiye Da Miliyan Ɗaya

June 3, 2026
Next Post
Za A Gudanar Da Jadawalin Cancantar Shiga AFCON 2027 A Alkahira Ranar Talata

Za A Gudanar Da Jadawalin Cancantar Shiga AFCON 2027 A Alkahira Ranar Talata

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026
Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

June 3, 2026
An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Magadan Gari Na 2026 A Beijing

An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Magadan Gari Na 2026 A Beijing

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.