Babban Darakta Gudanarwa na Shirin gwamnatin tarayya kan Iskar Gas ta CNG da Motocin Wutar Lantarki (Pi-CNG & EV), Ismaeel Ahmed, ya jaddada cewa ɗorewar haɗin kai da zuba jari su ne ƙashin bayan cimma muradin Nijeriya na komawa amfani da hanyoyin sufuri masu tsafta. Ya bayyana hakan ne ta bakin Babban Jami’in Bin Dokoki na tsarin, Zayyanu Tamberi, a yayin Taron Masana’antar Ƙera Motoci na Nijeriya karo na 3 (3rd Nigeria Auto Industry Summit) da aka gudanar ranar Alhamis, 30 ga Yuli, 2026 a jihar Lagos.
Taron, wanda Ƙungiyar Manema Labaran Masana’antar Motoci (NAJA) tare da Haɗin Gwuiwar Hukumar Haɓaka Ƙera Motoci ta Ƙasa (NADDC) suka shirya, ya mai da hankali ne kan hanyar Nijeriya ta komawa amfani da wutar lantarki da CNG a ƙarƙashin gwamnatin Shugaba Bola Tinubu.
Malam Ahmed ya bayyana cewa wannan shiri na shugaban ƙasa yana ɗaukar matakai masu mahimmanci wajen haɓaka adadin cibiyoyin sauya tsarin motoci zuwa CNG, da faɗaɗa tashoshin mai na iskar gas, da haɓaka motocin wutar lantarki, da gina koyar da ma’aikata. Ya ƙara da cewa a cikin shekaru biyu da suka gabata, shirin ya samu nasarori wajen horar da dubban ma’aikatan sauya wa zuwa tsarin, da kuma ƙaddamar da tsarin sa ido na ‘Nigeria Gas Vehicle Monitoring System’ domin tabbatar da tsaro da kiyaye ƙa’idoji.
Sai dai ya bayyana ƙarancin kayan aiki, da ƙarancin tsarin tallafin kuɗi ga masu saya, da raunin masana’antun gida a matsayin ƙalubalen da ke buƙatar haɗin gwiwar dukkan masu ruwa da tsaki.
Haka zalika, ya yabawa kafafen labarai a matsayin abokan tarayya masu muhimmanci a wannan tafiya, inda ya buƙaci mambobin ƙungiyar NAJA da su riƙa wallafa ingantattun labarai domin wayar da kan jama’a, ƙalubalantar labaran ƙarya, da jawo hankalin masu zuba jari. Ahmed ya jaddada aniyar shirin na rage kuɗaɗen sufuri ga ‘yan Nijeriya, da ƙirƙirar damar samar da ayyuka, da tabbatar da tsaron makamashi, da kuma samar da kyakkyawar rayuwa ta hanyar haɗin gwiwa mai ƙarfi da sanya jari a ɓangaren sufuri mai tsafta.
A nasa ɓangaren, Darakta Janar na Hukumar NADDC, Joseph Osanipin, wanda Darakta mai kula da Yaɗa Labarai na hukumar, Susan Bisong-Taiwo ta wakilta, ya yi kira ga masu zuba jari da su faɗaɗa zuba jarinsu a gidajen mai na CNG da sansanonin caji motocin lantarki.
Osanipin ya bayyana cewa ko da yake Nijeriya tana da cibiyoyin sauya tsarin motoci zuwa CNG guda 345 da aka amince da su a faɗin ƙasar, ana buƙatar ƙarin zuba jari daga ɓangaren masu zaman kansu domin rage dogayen layuka a gidajen mai da kuma sauƙaƙa amfani da motocin wutar lantarki a tafiye-tafiye masu nisa.














