Shugabannin gungiyoyi mabiya addinin Kirista da ƴan’uwansu Musulmai a Jihar Kaduna, sun rattaba hannun yarjejeniyar yaƙi da yi wa ƴaƴa mata fyaɗe da kuma take ƴancin Ɗan’adam.
Sun rabbata hannun ne a taron kwana biyu da cibiyar sasanci tsakanin addinai (IMC) ta shirya tare da tallafin ofishin jakadanci na ƙasar Jamus da ke Abuja.
Matan an zaɓo su ne daga shiyya ta biyu da ke a Kaduna, wanda idan matan sun koma cikin al’umominsu za su zama jakadu na tabbatar da wannann manufar da taron ya cimma.
A jawabinsa a wajen taron a madadin cibiyar, Mista Samson Auta ya ce manufar aikin shi ne, domin a daƙile yawan fyaɗen da ake yi wa ƴaƴa mata a jihar.
Ya ce ƙarin manufar rabbata hannun yarjejeniyar shi ne, domin matan su ƙara wa waɗanda aka yi wa fyaɗen ƙwarin giwa, su rinƙa fitowa fili suna faɗa wa hukumomin da suka dace, maimakon yin shiru, domin a ɗaukar matakin shari’a.
Ya ƙara da cewa ƙarin manufar shi ne, domin a daƙile nuna ƙyama da tsangwama da kuma kyara ga wanɗanda aka yi wa fyaɗen a cikin al’umomin da suka fito.
A nata jawabin, shugabar ƙungiyar lauyoyi ta ƙasa (FIDA) reshen Kaduna, Barrista Olufunke Bamikole ta ce, fahimtar muhimmancin ƴancin Ɗan’dam a tsakanin mahalarta taron, zai ƙara ba su damar sanin yadda za su kare ƴancin waɗanda aka ci zarafinsu ta hanyar fyaɗen.
Ta koka da cewa, rashin gazawar ɗaukar matakin gaggawa na wasu hukumomin a yankin Arewacin ƙasar, musamman a yankunan da ke karkara na hukunta waɗanda ake zargi, sun ci mutuncin ƴaƴa mata da yara ta hanyar fyaɗe.
Olufunke ta buƙaci gwamnatocin ƙasar, musamman na yankin Arewa da su ƙara ƙarfafa dokokin kare cin zarafin ƴaƴa mata da yaran da aka yi wa fyaɗe, musamman domin hukunta duk wanda aka kama, saboda ya zama darasi ga sauran masu aikata hakan.
Ita kuwa manajar Cibiyar Salama da ke duba lafiyar ƴaƴa mata da yaran da aka yi wa fyaɗe kyauta da ke asibitin ƙwararru na Yusuf Ɗanstoho da ke a Tudun Wada Kaduna, Barista Sidikat Bello Adegboye, ta yi kira ga ƙungiyoyi masu zaman kansu da su ƙara ƙaimi wajen wayar da kan al’umma kan yadda za a daƙile aikata ta’asar.
Ita kuwa ɗaya daga cikin jami’an Cibiyar Salama da ke duba lafiyar ƴaƴa mata da yaran da aka yiwa fyaɗe kyauta da ke asibitin ƙwararru na Gwamna Awon a Kakuri, Nanak Ndam, ta yi nuni da cewa waɗanda aka yi wa fyaɗe na shafar rayuwarsu ta yau da kullum, inda ta ce akwai matuƙar buƙatar a ba su kulawar da dace.
Shi kuwa jami’in da ke lura da sashen bai wa yara kariya a hukumar Sibil Difence reshen jihar, Suleiman Maiyaki, ya nuna ɓacin ransa kan yadda wasu iyayen ke lalata shaidar da za a iya amfani da ita na waɗanda aka yi wa fyaɗen, wanda hakan ke zama ƙalubale na bi masu haƙƙinsu a shari’ance.














