ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shugabannin ECOWAS Sun Jaddada Aniyarsu Ta Yaki Da Ta’addanci

by Sani Anwar
5 months ago
ECOWAS

Shugabannin Kasashen Ghana, Laberiya da Saliyo tare da wakilai daga Burkina Faso, Mali, Mauritaniya, Nijeriya, Senegal da Togo, sun jaddada aniyarsu ta zurfafa hadin gwiwar kasashen yankin, wajen yaki da ta’addanci da rashin tsaro.

Shugabannin, sun gana a birnin Akara daga ranar 29 zuwa 30 ga watan Janairu, a wani babban taron bayar da shawara kan hadin kai da tsaro a yankin, wanda shugaban Kasar Ghana, John Dramani Mahama ya jagoranta, tare da Shugaban Kasar Saliyo, Julius Maada Bio da Shugaban Kasar Laberiya, Joseph Boakai da suka jagoranci tawagarsu.

  • HOTUNA: Ɗan Ganduje Ya Ziyarci Kwankwaso A Kano
  • Sinawa Masu Amfani Da Yanar Gizo Sun Kai Biliyan 1.125

A cikin sanarwar hadin gwiwar da aka fitar a karshen taron na kwanaki biyu, shugabannin sun yi gargadin cewa, yammacin Afirka ya zama wata cibiyar ta’addanci da tsattsauran ra’ayi a duniya, tare da yin nuni da cewa, “a kowace rana, ana samun hare-haren ta’addanci akalla takwas, wanda ya yi sanadin mutuwar mutane 44.

ADVERTISEMENT

“Fiye da rabin duk mace-macen da ake samu, wadada ke da alaka da ta’addanci a duniya, ana samun su ne a yankunanmu. Muna ganin yadda ake samun tashin hankali a hare-haren masu tsattsauran ra’ayi, wanda rashin daukar mataki ba zai taba haifar mana da da mai ido ba.”

Taron, wanda ya biyo bayan shawarwarin da ministocin harkokin waje da na jami’an tsaro da leken asiri suka yi, ya kuma samu nakaltowa daga Hukumar Tarayyar Afirka, shirin raya ci gaban Majalisar Dinkin Duniya da kuma kungiyoyin fararen hula.

LABARAI MASU NASABA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Sanarwar ta jaddada bukatar samar da wani tsari na dindindin na hadin gwiwa, wanda zai wuce “diflomasiya ta al’ada ko iyakanceccen aiki.”

Ya kara da cewa, tsarin zai mayar da hankali a kan shirye-shiryen da aka tanada da ka’idoji da kuma sauran abubuwan more rayuwa.

A game da yaki da ta’addanci, shugabannin sun amince da “karfafa tarukan yau da kullum na jihohi a yankin, domin sake duba alkawuran zaman lafiya da tsaro,” inganta musayar bayanan sirri, daidaita tsarin shari’a, don gurfanar da laifuffukan da ke da alaka da ta’addanci da kuma karfafa shirye-shiryen kawar da tsattsauran ra’ayi.

Domin magance tsaron kan iyaka, taron ya himmatu wajen yin la’akari da daukar yarjejeniyoyin “zafafa bi”, da tsara ka’idar fahimtar juna a cikin watanni uku da karfafa hanyoyin yaki da fataucin miyagun kwayoyi da makamai. Yarda da cewa, martanin soji kadai ba zai iya tabbatar da zaman lafiya mai dorewa ba, sanarwar ta yi alkawarin bayar da fifiko ga tsaron lafiyar mutane ta hanyar samar da abinci, kiwon lafiya, samar da ayyukan yi da kuma ilimi.

Har ila yau, ta yi kira da a karfafa gudanar da mulki a cikin gida da kuma amfani da fasahar zamani, domin zamanantar da sarrafa kan iyakoki da sauran ayyuka.

ECOWAS
Sani Anwar
+ postsBio
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Tattalin Arziƙin Ƙasa: Masana Sun Buƙaci Tinubu Ya Yi Hattara Da Shawarar IMF
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (2)
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (1)
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

MASU ALAKA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
Labarai

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
Ra'ayi Riga

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma
Labarai

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Next Post
Wa’adin Da Tinubu Ya Bai Wa Manoman Da Suka Ci Bashin ‘Anchor Borrowers’ Ya Cika

Dalilin Da Ya Sa Taraba Ba Za Ta Samu Amfanin Gona  Mai Yalwa Ba A 2026

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.