ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shugabannin ECOWAS Sun Jaddada Aniyarsu Ta Yaki Da Ta’addanci

by Sani Anwar
4 months ago
ECOWAS

Shugabannin Kasashen Ghana, Laberiya da Saliyo tare da wakilai daga Burkina Faso, Mali, Mauritaniya, Nijeriya, Senegal da Togo, sun jaddada aniyarsu ta zurfafa hadin gwiwar kasashen yankin, wajen yaki da ta’addanci da rashin tsaro.

Shugabannin, sun gana a birnin Akara daga ranar 29 zuwa 30 ga watan Janairu, a wani babban taron bayar da shawara kan hadin kai da tsaro a yankin, wanda shugaban Kasar Ghana, John Dramani Mahama ya jagoranta, tare da Shugaban Kasar Saliyo, Julius Maada Bio da Shugaban Kasar Laberiya, Joseph Boakai da suka jagoranci tawagarsu.

  • HOTUNA: Ɗan Ganduje Ya Ziyarci Kwankwaso A Kano
  • Sinawa Masu Amfani Da Yanar Gizo Sun Kai Biliyan 1.125

A cikin sanarwar hadin gwiwar da aka fitar a karshen taron na kwanaki biyu, shugabannin sun yi gargadin cewa, yammacin Afirka ya zama wata cibiyar ta’addanci da tsattsauran ra’ayi a duniya, tare da yin nuni da cewa, “a kowace rana, ana samun hare-haren ta’addanci akalla takwas, wanda ya yi sanadin mutuwar mutane 44.

ADVERTISEMENT

“Fiye da rabin duk mace-macen da ake samu, wadada ke da alaka da ta’addanci a duniya, ana samun su ne a yankunanmu. Muna ganin yadda ake samun tashin hankali a hare-haren masu tsattsauran ra’ayi, wanda rashin daukar mataki ba zai taba haifar mana da da mai ido ba.”

Taron, wanda ya biyo bayan shawarwarin da ministocin harkokin waje da na jami’an tsaro da leken asiri suka yi, ya kuma samu nakaltowa daga Hukumar Tarayyar Afirka, shirin raya ci gaban Majalisar Dinkin Duniya da kuma kungiyoyin fararen hula.

LABARAI MASU NASABA

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Sanarwar ta jaddada bukatar samar da wani tsari na dindindin na hadin gwiwa, wanda zai wuce “diflomasiya ta al’ada ko iyakanceccen aiki.”

Ya kara da cewa, tsarin zai mayar da hankali a kan shirye-shiryen da aka tanada da ka’idoji da kuma sauran abubuwan more rayuwa.

A game da yaki da ta’addanci, shugabannin sun amince da “karfafa tarukan yau da kullum na jihohi a yankin, domin sake duba alkawuran zaman lafiya da tsaro,” inganta musayar bayanan sirri, daidaita tsarin shari’a, don gurfanar da laifuffukan da ke da alaka da ta’addanci da kuma karfafa shirye-shiryen kawar da tsattsauran ra’ayi.

Domin magance tsaron kan iyaka, taron ya himmatu wajen yin la’akari da daukar yarjejeniyoyin “zafafa bi”, da tsara ka’idar fahimtar juna a cikin watanni uku da karfafa hanyoyin yaki da fataucin miyagun kwayoyi da makamai. Yarda da cewa, martanin soji kadai ba zai iya tabbatar da zaman lafiya mai dorewa ba, sanarwar ta yi alkawarin bayar da fifiko ga tsaron lafiyar mutane ta hanyar samar da abinci, kiwon lafiya, samar da ayyukan yi da kuma ilimi.

Har ila yau, ta yi kira da a karfafa gudanar da mulki a cikin gida da kuma amfani da fasahar zamani, domin zamanantar da sarrafa kan iyakoki da sauran ayyuka.

ECOWAS
Sani Anwar
+ postsBio
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Sojoji Sun Ceto Mutum 92 Tare Da Daƙile Harin Ƴan Ta’adda A Borno
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Uzodimma: Babu Dimokraɗiyya Idan Babu Hamayya
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Alamomin Fara Ruɓewar Hannu Bayan Ɗorin Gida
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Ministocin Da Suka Ajiye Muƙamansu Ba Su Samu Tikitin Takara Ba

MASU ALAKA

Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed
Labarai

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa
Labarai

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Next Post
Wa’adin Da Tinubu Ya Bai Wa Manoman Da Suka Ci Bashin ‘Anchor Borrowers’ Ya Cika

Dalilin Da Ya Sa Taraba Ba Za Ta Samu Amfanin Gona  Mai Yalwa Ba A 2026

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.