ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shugabannin ECOWAS Sun Jaddada Aniyarsu Ta Yaki Da Ta’addanci

by Sani Anwar
5 months ago
ECOWAS

Shugabannin Kasashen Ghana, Laberiya da Saliyo tare da wakilai daga Burkina Faso, Mali, Mauritaniya, Nijeriya, Senegal da Togo, sun jaddada aniyarsu ta zurfafa hadin gwiwar kasashen yankin, wajen yaki da ta’addanci da rashin tsaro.

Shugabannin, sun gana a birnin Akara daga ranar 29 zuwa 30 ga watan Janairu, a wani babban taron bayar da shawara kan hadin kai da tsaro a yankin, wanda shugaban Kasar Ghana, John Dramani Mahama ya jagoranta, tare da Shugaban Kasar Saliyo, Julius Maada Bio da Shugaban Kasar Laberiya, Joseph Boakai da suka jagoranci tawagarsu.

  • HOTUNA: Ɗan Ganduje Ya Ziyarci Kwankwaso A Kano
  • Sinawa Masu Amfani Da Yanar Gizo Sun Kai Biliyan 1.125

A cikin sanarwar hadin gwiwar da aka fitar a karshen taron na kwanaki biyu, shugabannin sun yi gargadin cewa, yammacin Afirka ya zama wata cibiyar ta’addanci da tsattsauran ra’ayi a duniya, tare da yin nuni da cewa, “a kowace rana, ana samun hare-haren ta’addanci akalla takwas, wanda ya yi sanadin mutuwar mutane 44.

ADVERTISEMENT

“Fiye da rabin duk mace-macen da ake samu, wadada ke da alaka da ta’addanci a duniya, ana samun su ne a yankunanmu. Muna ganin yadda ake samun tashin hankali a hare-haren masu tsattsauran ra’ayi, wanda rashin daukar mataki ba zai taba haifar mana da da mai ido ba.”

Taron, wanda ya biyo bayan shawarwarin da ministocin harkokin waje da na jami’an tsaro da leken asiri suka yi, ya kuma samu nakaltowa daga Hukumar Tarayyar Afirka, shirin raya ci gaban Majalisar Dinkin Duniya da kuma kungiyoyin fararen hula.

LABARAI MASU NASABA

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

Sanarwar ta jaddada bukatar samar da wani tsari na dindindin na hadin gwiwa, wanda zai wuce “diflomasiya ta al’ada ko iyakanceccen aiki.”

Ya kara da cewa, tsarin zai mayar da hankali a kan shirye-shiryen da aka tanada da ka’idoji da kuma sauran abubuwan more rayuwa.

A game da yaki da ta’addanci, shugabannin sun amince da “karfafa tarukan yau da kullum na jihohi a yankin, domin sake duba alkawuran zaman lafiya da tsaro,” inganta musayar bayanan sirri, daidaita tsarin shari’a, don gurfanar da laifuffukan da ke da alaka da ta’addanci da kuma karfafa shirye-shiryen kawar da tsattsauran ra’ayi.

Domin magance tsaron kan iyaka, taron ya himmatu wajen yin la’akari da daukar yarjejeniyoyin “zafafa bi”, da tsara ka’idar fahimtar juna a cikin watanni uku da karfafa hanyoyin yaki da fataucin miyagun kwayoyi da makamai. Yarda da cewa, martanin soji kadai ba zai iya tabbatar da zaman lafiya mai dorewa ba, sanarwar ta yi alkawarin bayar da fifiko ga tsaron lafiyar mutane ta hanyar samar da abinci, kiwon lafiya, samar da ayyukan yi da kuma ilimi.

Har ila yau, ta yi kira da a karfafa gudanar da mulki a cikin gida da kuma amfani da fasahar zamani, domin zamanantar da sarrafa kan iyakoki da sauran ayyuka.

ECOWAS
Sani Anwar
+ postsBio
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Tattalin Arziƙin Ƙasa: Masana Sun Buƙaci Tinubu Ya Yi Hattara Da Shawarar IMF
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (2)
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (1)
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

MASU ALAKA

Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso
Manyan Labarai

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku
Manyan Labarai

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Next Post
Wa’adin Da Tinubu Ya Bai Wa Manoman Da Suka Ci Bashin ‘Anchor Borrowers’ Ya Cika

Dalilin Da Ya Sa Taraba Ba Za Ta Samu Amfanin Gona  Mai Yalwa Ba A 2026

LABARAI MASU NASABA

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026
Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

June 24, 2026
Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

June 24, 2026
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

June 24, 2026
An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.