ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shugabannin ECOWAS Sun Jaddada Aniyarsu Ta Yaki Da Ta’addanci

by Sani Anwar
7 months ago
ECOWAS

Shugabannin Kasashen Ghana, Laberiya da Saliyo tare da wakilai daga Burkina Faso, Mali, Mauritaniya, Nijeriya, Senegal da Togo, sun jaddada aniyarsu ta zurfafa hadin gwiwar kasashen yankin, wajen yaki da ta’addanci da rashin tsaro.

Shugabannin, sun gana a birnin Akara daga ranar 29 zuwa 30 ga watan Janairu, a wani babban taron bayar da shawara kan hadin kai da tsaro a yankin, wanda shugaban Kasar Ghana, John Dramani Mahama ya jagoranta, tare da Shugaban Kasar Saliyo, Julius Maada Bio da Shugaban Kasar Laberiya, Joseph Boakai da suka jagoranci tawagarsu.

  • HOTUNA: Ɗan Ganduje Ya Ziyarci Kwankwaso A Kano
  • Sinawa Masu Amfani Da Yanar Gizo Sun Kai Biliyan 1.125

A cikin sanarwar hadin gwiwar da aka fitar a karshen taron na kwanaki biyu, shugabannin sun yi gargadin cewa, yammacin Afirka ya zama wata cibiyar ta’addanci da tsattsauran ra’ayi a duniya, tare da yin nuni da cewa, “a kowace rana, ana samun hare-haren ta’addanci akalla takwas, wanda ya yi sanadin mutuwar mutane 44.

ADVERTISEMENT

“Fiye da rabin duk mace-macen da ake samu, wadada ke da alaka da ta’addanci a duniya, ana samun su ne a yankunanmu. Muna ganin yadda ake samun tashin hankali a hare-haren masu tsattsauran ra’ayi, wanda rashin daukar mataki ba zai taba haifar mana da da mai ido ba.”

Taron, wanda ya biyo bayan shawarwarin da ministocin harkokin waje da na jami’an tsaro da leken asiri suka yi, ya kuma samu nakaltowa daga Hukumar Tarayyar Afirka, shirin raya ci gaban Majalisar Dinkin Duniya da kuma kungiyoyin fararen hula.

LABARAI MASU NASABA

Hormuz: Iran Ta Kai Muggan Hare-hare Kan Sansanin Amurka A Jordan

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

Sanarwar ta jaddada bukatar samar da wani tsari na dindindin na hadin gwiwa, wanda zai wuce “diflomasiya ta al’ada ko iyakanceccen aiki.”

Ya kara da cewa, tsarin zai mayar da hankali a kan shirye-shiryen da aka tanada da ka’idoji da kuma sauran abubuwan more rayuwa.

A game da yaki da ta’addanci, shugabannin sun amince da “karfafa tarukan yau da kullum na jihohi a yankin, domin sake duba alkawuran zaman lafiya da tsaro,” inganta musayar bayanan sirri, daidaita tsarin shari’a, don gurfanar da laifuffukan da ke da alaka da ta’addanci da kuma karfafa shirye-shiryen kawar da tsattsauran ra’ayi.

Domin magance tsaron kan iyaka, taron ya himmatu wajen yin la’akari da daukar yarjejeniyoyin “zafafa bi”, da tsara ka’idar fahimtar juna a cikin watanni uku da karfafa hanyoyin yaki da fataucin miyagun kwayoyi da makamai. Yarda da cewa, martanin soji kadai ba zai iya tabbatar da zaman lafiya mai dorewa ba, sanarwar ta yi alkawarin bayar da fifiko ga tsaron lafiyar mutane ta hanyar samar da abinci, kiwon lafiya, samar da ayyukan yi da kuma ilimi.

Har ila yau, ta yi kira da a karfafa gudanar da mulki a cikin gida da kuma amfani da fasahar zamani, domin zamanantar da sarrafa kan iyakoki da sauran ayyuka.

ECOWAS
Sani Anwar
+ postsBio
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Ko Kun San Amfanin Kwanciya Da Bangaren Hagu?
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    2027:Mata Shida Da Ke Takarar Neman Shugabancin Nijeriya
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Dambarwa A Kasuwancin Iyalan Indimi
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Illar Shan Taba Sigari Da Dangoginta

MASU ALAKA

Iran Ta Musanta Ikirarin Trump Tare Da Zafafa Hare-hare Kan Isra’ila
Manyan Labarai

Hormuz: Iran Ta Kai Muggan Hare-hare Kan Sansanin Amurka A Jordan

September 9, 2026
ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto
Labarai

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

September 9, 2026
Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja
Labarai

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Next Post
Wa’adin Da Tinubu Ya Bai Wa Manoman Da Suka Ci Bashin ‘Anchor Borrowers’ Ya Cika

Dalilin Da Ya Sa Taraba Ba Za Ta Samu Amfanin Gona  Mai Yalwa Ba A 2026

LABARAI MASU NASABA

Iran Ta Musanta Ikirarin Trump Tare Da Zafafa Hare-hare Kan Isra’ila

Hormuz: Iran Ta Kai Muggan Hare-hare Kan Sansanin Amurka A Jordan

September 9, 2026
ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

September 9, 2026
Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.