ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dalilin Da Ya Sa Taraba Ba Za Ta Samu Amfanin Gona  Mai Yalwa Ba A 2026

by Abubakar Abba
4 months ago
Gona

Wani bincike da jaridar LEADERSHIP ta gudanar, ya nuna cewa; kudin shigar da sashen bayar da hayar taraktocin noma na Jihar Taraba, wato THU ke son samu a 2026 na hayar taraktocin noma, ba za su samu kamar yadda suka tsara ba.

Hakan zai kasance ne, sakamakon ganin cewa; taraktocin noma biyu kacal ne, na Cabrio aka ware wa sashen, wanda hakan ya nuna cewa; sun yi matukar karanci a aikin noman da za a yi a kakar aikin noma ta 2026.

  • Kasar Sin Na Da Kayayyakin Tarihi Na Halittu Na Duniya Guda 15
  • Aisha Buhari Ta Ziyarci Atiku A Saudiyya 

Ana dai sa ran sashen, zai samar da kayan aikin noma da ake bukata, domin a samu tumbatsar amfanin gona, bayan an samu taraktocin noma, inda tuni manoman jihar, suka fitar da tsammanin samun wani amfanin gona mai yawa.

ADVERTISEMENT

Binciken ya kuma nuna cewa, akalla sashen na bukatar a samar masa da taraktocin noma guda 35, da suka hada da guda biyun da aka samar na Cabrio, domin yin noma a 2026.

Idan za a iya tunawa, gwamnatin jihar ta Taraba, ta kirkiro da sashen ne, domin samar da kayan aikin noma ga manoman da ke jihar a cikin farashi mai sauki, musamman domin inganta rayuwar al’ummar jihar da kuma kara samar da kudaden shiga.

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Sabbin Cibiyoyin Kula Da Lafiyar Dabbobi

Abin Da Ya Sa Gwamnatin Taraba Ta Sayo Sabbin Kayan Noma Na Zamani

Kazalika, an kirkiro da sashen ne, domin a rika horas da injiniyoyi da rabar da taraktocin noma ga kananan hukumomin jihar 16 da kuma wasu sassa biyu, wadanda suka kasance, sun dakile ayyukan ma’aikatar bunkasa aikin noma da samar da wadataccen abinci.

Jim kadan bayan karbar taraktocin noman daga wurin ma’aikatar bunkasa aikin noma da samar da wadataccen abinci ta jihar, Janar Manaja na hukumar, Injiniya Danladi Shatalis, ya yi godiya ga gwamnan jihar Agbu Kefas, kan kokarin da gwamnatinsa ke ci gaba da yi na farfado da fannin aikin noma na jihar.

Injiniya Shatalis, ya kuma yaba da shirin da aka kirkiro da shi na samar da taraktocin noma, musamman domin samar da kayan aikin noma na zamani da kara habaka samar da wadataccen abinci a jihar.

Kazalika, ya gode wa kwamishinan ma’aikatar, bunkasa aikin noma da samar da wadataccen abinci na jihar, Farfesa Nicholas Oliber, kan ci gaba da taimaka wa sashen, musamaman kan samar da taraktocin noma guda biyu da kuma wasu kannan taraktocin noma, duk da bukatar da sashen ya gabatar na bukatar manyan taraktocin noman, domin cimma bukatar da manoman jihar suke da ita.

Bugu da kari, ya yaba wa shugaban kwamtin kula da bunkasa aikin noma da samar da wadataccen abinci na jihar, na Majalisar Dokokin Jihar, Hon. Abubakar Tanko Yusuf, kan goyon bayan da yake ci gaba da bai wa sashen, musamman goyon bayan da ya bai wa sashen a lokacin kare kashe kudin da aka ware wa sashen.

Duk da irin wannan yabo da kwamitin na Majalisar Dokokin ya yi wa sashen, sashen ya gaza cimma bukatar da ake da ita, na tara kudaden shiga a 2025, wanda hakan ya nuna cewa; akwai bukatar a kara samar da taraktocin noma ga sashen, musamman domin kara wadata jihar da abinci.

Gona
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Abin Da Ya Sa Gwamnatin Taraba Ta Sayo Sabbin Kayan Noma Na Zamani
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Kamfanin Simintin Ɗangote Ya Ƙaddamar Da Shirye-shiryen Tallafa Wa Mazauna Jihar Biniwe
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Dalilin Gwamnatin Kwara Na Zuba Dala Biliyan 70 A Fannin Kiwon Dabbobi
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Cibiyar IAR Ta Gudanar Da Ayyukan Bincike 140 Kan Sabbin Amfanin Gona 

MASU ALAKA

Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Sabbin Cibiyoyin Kula Da Lafiyar Dabbobi
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Sabbin Cibiyoyin Kula Da Lafiyar Dabbobi

May 31, 2026
Abin Da Ya Sa Gwamnatin Taraba Ta Sayo Sabbin Kayan Noma Na Zamani
Noma Da Kiwo

Abin Da Ya Sa Gwamnatin Taraba Ta Sayo Sabbin Kayan Noma Na Zamani

May 31, 2026
Laifukan Intanet: Kotun Abuja Ta Karɓi Rahoton DSS, Ta Ba Da Belin Wani Ɗan Gwagwarmaya
Noma Da Kiwo

IAR Ta Fara Horas Da Malaman Gona Don Fuskantar Daminar Bana

May 24, 2026
Next Post
Masu Ruwa Da Tsaki Sun Gudanar Da Taro Kan Yadda Za A Tunkari Kakar Noman Bana

Masu Ruwa Da Tsaki Sun Gudanar Da Taro Kan Yadda Za A Tunkari Kakar Noman Bana

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026
Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.