ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dalilin Da Ya Sa Taraba Ba Za Ta Samu Amfanin Gona  Mai Yalwa Ba A 2026

by Abubakar Abba
5 months ago
Gona

Wani bincike da jaridar LEADERSHIP ta gudanar, ya nuna cewa; kudin shigar da sashen bayar da hayar taraktocin noma na Jihar Taraba, wato THU ke son samu a 2026 na hayar taraktocin noma, ba za su samu kamar yadda suka tsara ba.

Hakan zai kasance ne, sakamakon ganin cewa; taraktocin noma biyu kacal ne, na Cabrio aka ware wa sashen, wanda hakan ya nuna cewa; sun yi matukar karanci a aikin noman da za a yi a kakar aikin noma ta 2026.

  • Kasar Sin Na Da Kayayyakin Tarihi Na Halittu Na Duniya Guda 15
  • Aisha Buhari Ta Ziyarci Atiku A Saudiyya 

Ana dai sa ran sashen, zai samar da kayan aikin noma da ake bukata, domin a samu tumbatsar amfanin gona, bayan an samu taraktocin noma, inda tuni manoman jihar, suka fitar da tsammanin samun wani amfanin gona mai yawa.

ADVERTISEMENT

Binciken ya kuma nuna cewa, akalla sashen na bukatar a samar masa da taraktocin noma guda 35, da suka hada da guda biyun da aka samar na Cabrio, domin yin noma a 2026.

Idan za a iya tunawa, gwamnatin jihar ta Taraba, ta kirkiro da sashen ne, domin samar da kayan aikin noma ga manoman da ke jihar a cikin farashi mai sauki, musamman domin inganta rayuwar al’ummar jihar da kuma kara samar da kudaden shiga.

LABARAI MASU NASABA

Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa

Me Ya Sa Har Yanzu Manoma A Arewa Suka Gwammace Yin Noma Da Galmar Shanu

Kazalika, an kirkiro da sashen ne, domin a rika horas da injiniyoyi da rabar da taraktocin noma ga kananan hukumomin jihar 16 da kuma wasu sassa biyu, wadanda suka kasance, sun dakile ayyukan ma’aikatar bunkasa aikin noma da samar da wadataccen abinci.

Jim kadan bayan karbar taraktocin noman daga wurin ma’aikatar bunkasa aikin noma da samar da wadataccen abinci ta jihar, Janar Manaja na hukumar, Injiniya Danladi Shatalis, ya yi godiya ga gwamnan jihar Agbu Kefas, kan kokarin da gwamnatinsa ke ci gaba da yi na farfado da fannin aikin noma na jihar.

Injiniya Shatalis, ya kuma yaba da shirin da aka kirkiro da shi na samar da taraktocin noma, musamman domin samar da kayan aikin noma na zamani da kara habaka samar da wadataccen abinci a jihar.

Kazalika, ya gode wa kwamishinan ma’aikatar, bunkasa aikin noma da samar da wadataccen abinci na jihar, Farfesa Nicholas Oliber, kan ci gaba da taimaka wa sashen, musamaman kan samar da taraktocin noma guda biyu da kuma wasu kannan taraktocin noma, duk da bukatar da sashen ya gabatar na bukatar manyan taraktocin noman, domin cimma bukatar da manoman jihar suke da ita.

Bugu da kari, ya yaba wa shugaban kwamtin kula da bunkasa aikin noma da samar da wadataccen abinci na jihar, na Majalisar Dokokin Jihar, Hon. Abubakar Tanko Yusuf, kan goyon bayan da yake ci gaba da bai wa sashen, musamman goyon bayan da ya bai wa sashen a lokacin kare kashe kudin da aka ware wa sashen.

Duk da irin wannan yabo da kwamitin na Majalisar Dokokin ya yi wa sashen, sashen ya gaza cimma bukatar da ake da ita, na tara kudaden shiga a 2025, wanda hakan ya nuna cewa; akwai bukatar a kara samar da taraktocin noma ga sashen, musamman domin kara wadata jihar da abinci.

Gona
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Nazari A Kan Wasu Cututtuka Da Ke Shafar Dabbobi Lokacin Damina
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Ɗantsoho Ya Jinjina Wa Hukumar FCC Kan Sabbin Sauye-Sauyen Da Ta Samar
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    “Mutunta Ƴancin Addinai Ita Ce Hanyar Wanzar Da Zaman Lafiya A Kaduna”

MASU ALAKA

Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Noma Da Kiwo

Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa

July 11, 2026
Me Ya Sa Har Yanzu Manoma A Arewa Suka Gwammace Yin Noma Da Galmar Shanu
Noma Da Kiwo

Me Ya Sa Har Yanzu Manoma A Arewa Suka Gwammace Yin Noma Da Galmar Shanu

July 4, 2026
Dalilin Masu Kiwon Kajin Gidan Gona Na Sukar Haɗakar Gwamnatin Tarayya Da Chana
Noma Da Kiwo

Dalilin Masu Kiwon Kajin Gidan Gona Na Sukar Haɗakar Gwamnatin Tarayya Da Chana

July 3, 2026
Next Post
Masu Ruwa Da Tsaki Sun Gudanar Da Taro Kan Yadda Za A Tunkari Kakar Noman Bana

Masu Ruwa Da Tsaki Sun Gudanar Da Taro Kan Yadda Za A Tunkari Kakar Noman Bana

LABARAI MASU NASABA

Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Lalata Da Ƙaramar Yarinya: Kotu Ta Yanke Wa Tsoho Mai Shekara 75 Hukuncin Ɗaurin Shekara 10 A Ribas

July 15, 2026
Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

July 15, 2026
‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi

‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi

July 15, 2026
Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

July 15, 2026
Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

July 15, 2026
Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.