ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dalilin Da Ya Sa Taraba Ba Za Ta Samu Amfanin Gona  Mai Yalwa Ba A 2026

by Abubakar Abba
5 months ago
Gona

Wani bincike da jaridar LEADERSHIP ta gudanar, ya nuna cewa; kudin shigar da sashen bayar da hayar taraktocin noma na Jihar Taraba, wato THU ke son samu a 2026 na hayar taraktocin noma, ba za su samu kamar yadda suka tsara ba.

Hakan zai kasance ne, sakamakon ganin cewa; taraktocin noma biyu kacal ne, na Cabrio aka ware wa sashen, wanda hakan ya nuna cewa; sun yi matukar karanci a aikin noman da za a yi a kakar aikin noma ta 2026.

  • Kasar Sin Na Da Kayayyakin Tarihi Na Halittu Na Duniya Guda 15
  • Aisha Buhari Ta Ziyarci Atiku A Saudiyya 

Ana dai sa ran sashen, zai samar da kayan aikin noma da ake bukata, domin a samu tumbatsar amfanin gona, bayan an samu taraktocin noma, inda tuni manoman jihar, suka fitar da tsammanin samun wani amfanin gona mai yawa.

ADVERTISEMENT

Binciken ya kuma nuna cewa, akalla sashen na bukatar a samar masa da taraktocin noma guda 35, da suka hada da guda biyun da aka samar na Cabrio, domin yin noma a 2026.

Idan za a iya tunawa, gwamnatin jihar ta Taraba, ta kirkiro da sashen ne, domin samar da kayan aikin noma ga manoman da ke jihar a cikin farashi mai sauki, musamman domin inganta rayuwar al’ummar jihar da kuma kara samar da kudaden shiga.

LABARAI MASU NASABA

Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa

Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA

Kazalika, an kirkiro da sashen ne, domin a rika horas da injiniyoyi da rabar da taraktocin noma ga kananan hukumomin jihar 16 da kuma wasu sassa biyu, wadanda suka kasance, sun dakile ayyukan ma’aikatar bunkasa aikin noma da samar da wadataccen abinci.

Jim kadan bayan karbar taraktocin noman daga wurin ma’aikatar bunkasa aikin noma da samar da wadataccen abinci ta jihar, Janar Manaja na hukumar, Injiniya Danladi Shatalis, ya yi godiya ga gwamnan jihar Agbu Kefas, kan kokarin da gwamnatinsa ke ci gaba da yi na farfado da fannin aikin noma na jihar.

Injiniya Shatalis, ya kuma yaba da shirin da aka kirkiro da shi na samar da taraktocin noma, musamman domin samar da kayan aikin noma na zamani da kara habaka samar da wadataccen abinci a jihar.

Kazalika, ya gode wa kwamishinan ma’aikatar, bunkasa aikin noma da samar da wadataccen abinci na jihar, Farfesa Nicholas Oliber, kan ci gaba da taimaka wa sashen, musamaman kan samar da taraktocin noma guda biyu da kuma wasu kannan taraktocin noma, duk da bukatar da sashen ya gabatar na bukatar manyan taraktocin noman, domin cimma bukatar da manoman jihar suke da ita.

Bugu da kari, ya yaba wa shugaban kwamtin kula da bunkasa aikin noma da samar da wadataccen abinci na jihar, na Majalisar Dokokin Jihar, Hon. Abubakar Tanko Yusuf, kan goyon bayan da yake ci gaba da bai wa sashen, musamman goyon bayan da ya bai wa sashen a lokacin kare kashe kudin da aka ware wa sashen.

Duk da irin wannan yabo da kwamitin na Majalisar Dokokin ya yi wa sashen, sashen ya gaza cimma bukatar da ake da ita, na tara kudaden shiga a 2025, wanda hakan ya nuna cewa; akwai bukatar a kara samar da taraktocin noma ga sashen, musamman domin kara wadata jihar da abinci.

Gona
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Duk Da Sabani Tsakanin Ɗangote Da NNPC Jiragen Ruwa Ɗauke Da Man Fetur Sun Iso Nijeriya
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Manoman Citta Sun Soki Gwamnatin Delta Kan Mayar Da Su Saniyar Ware

MASU ALAKA

Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa
Noma Da Kiwo

Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa

June 20, 2026
Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA
Noma Da Kiwo

Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA

June 20, 2026
Kungiyar Manoman Citta Ta Kasa Ta Yaba Wa Gwamnatin Tarayya Kan Tallafin Da Take Ba Su
Noma Da Kiwo

Manoman Citta Sun Soki Gwamnatin Delta Kan Mayar Da Su Saniyar Ware

June 19, 2026
Next Post
Masu Ruwa Da Tsaki Sun Gudanar Da Taro Kan Yadda Za A Tunkari Kakar Noman Bana

Masu Ruwa Da Tsaki Sun Gudanar Da Taro Kan Yadda Za A Tunkari Kakar Noman Bana

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara

Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara

June 25, 2026
Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026

Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026

June 25, 2026
An Fara Gasar Tseren Dawakai Ta ‘Renewed Hope’ da Sabon Salo A Kano

An Fara Gasar Tseren Dawakai Ta ‘Renewed Hope’ da Sabon Salo A Kano

June 25, 2026
APC Ta Dage Yakin Zaben Shugaban Kasarta A Kano

An Dakatar Da Shugaban APC Na Kebbi Da Kwamishina Kan Zaɓen Cike Gurbin Zuru

June 25, 2026
Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

June 25, 2026
EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

June 25, 2026
Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

June 25, 2026
Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa — Atiku

June 25, 2026
Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.